Sashe 62
A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"To a ina kike ganin za a saka kayan?" Innarsu ta tambaya tana kallonta, "A cikin leda ko?" Salma ta faɗa, "Amman kina ganin lafiya lau a saka a leda? Na ga su ƴan gayu zaki ga a ɗan kwando suke saka kayan abinci." Dariya maganar ta ba Salma ta ce, "To ai mu ba ƴan gayun bane bamu da kwandon, in dai ba a cikin riyon Usman za a saka ba matsayin kwandon..." Dariya ta saka kafin ta gama maganar ganin irin kallon da innar tasu take jefa mata, ta ce, "Ta ya za a saka kayan abinci a cikin riyo in banda abun ki, ai sai ma ya kasa cin abincin." Still dariya Salma take yi ta ce, "To kema innarmu tun da kin san babu kwandon kawai a saka a ledan mana ai ba wani abu bane." Amsa mata ta yi da to ta ce tana zuwa ta nufi hanyar ɗakinta da sauri, fitowa ta yi hannunta riƙe da wata farar leda mai ƙauri irin ta siyayya ta nufo Salma tana faɗin, "Ina ganin zai fi a saka a wannan ledan, dama ganin mai kyau ce yasa na 6oye ta." Kai Salma ta ɗaga, bayan an gama saka kayan ta ɗauka tana faɗin sai ta dawo, innarsu ta ce mata to, lokacin da ta kai bakin soro tana niyyar fita innar ta ɗan ɗaga murya ta ce, "Ki faɗa ma hajiya a yi mana godiya ya bamu kuɗi." Ta amsa mata da to daga haka ta fice. Hajiya zaune a falo ta kara waya a kunnanta tana waya fuskarta ɗauke da fara'a, da sallama Salma ta shigo cikin falon, bayan ta ƙarasa ciki ta tsaya ɗan gefe da hajiyan tana jiran ta gama wayan, bata daɗe da shigowa ba hajiya ta kammala yin wayar bayan ta ajiye a gefenta ta ɗago ta kalli Salma, da murmushi ta ce, "Salma ce..." Ta amsa mata, "Eh, ina wuni hajiya." Bayan ta amsa ta nuna mata kujera ta ce ga wuri ta zauna, zama ta yi ta ɗan yi shiru haka nan sai ta ji nauyin yadda zata faɗi abun da ya kawo ta, "Ya maman taku da ƴan'uwanki?" Da ɗan murmushi ta kalli hajiyan ta ce mata duk suna nan lafiya lau, hajiya ta ce, "Ma sha Allah." Shiru suka ɗan ƙara yi idon hajiya na akan tv, can ta juyo ta kalli Salma ta ce aiken ta aka yi? da sauri ta ce, "A'a, dama innarmu ta ce in kawo wannan a bawa yaya Deen, sannan ta ce in faɗa maki a yi mana godiya ya bamu kuɗi." Murmushi ne akan fuskar hajiya ta ce, "To, mi Deen ya samu?" Miƙewa Salma ta yi ta kai ledan gabanta tana faɗi mata abun da ke ciki, godiya hajiya ta yi ta ce bari a kirawo shi yana nan, wayarta ta ɗauka ta fara dannawa kafin ta kara ta a kunne, tana murmushi ta ce, "Ka zo falo ga saƙo an kawo maka." Daga haka ta cire wayan tana faɗin, "Tun ɗazun da ya dawo gidan yake a ɗaki, dana ji shirun ta yi yawa har leƙawa na yi na iske shi wai suna meeting ne da mutanensu yan ƙwallo ta kwamfuta." Ɗan murmushi ne akan fuskar Salma ba tare da ta ce komai ba, after few minutes sai gashi ya fito, wani irin faɗuwa gaban Salma ya yi ganin a yadda ya fito daga shi sai wando 3-quarter, da sauri ta sunnar da kanta ƙasa, daga gefen kujeran da hajiya take ya tsaya yana kallonta kamar yadda itama take kallonsa ta ce, "Sarkin jin zafi, har ta kai an cire riga ke nan." Ɗan murmushi kawai ya yi, nuna masa ledan dake gabanta ta yi ta ce gashi nan dama Salma ce ta kawo mashi awara in ji innarsu, ɗaura idonsa ya yi akan Salma da bata
yarda ta ƙara ɗagowa ba, don a yadda ta gansa har tsorata ta yi ba wai don bata ta6a ganin namiji ba riga ba, wannan ma ta saba gani wurin su Auwalu da Sagir, sai dai akwai bambancin ƙirar jiki a tsakaninsu da Deen nesa ba kusa ba, gaba ɗaya a murɗe yake ga six-pack din cikinsa sun fito baro baro, fatar jikinsa fara tass da ita ba ko ɗan ta6o, yadda cikinsa yake a ɗame tamkar baya cin abinci, maido idonsa ya yi ya sake kallon ledan da ɗan alamun mamaki akan fuskar tasa, "Tukuici ne aka aiko maka, ta ce in taya su yi maka godiya ka basu kuɗi. Allah Ya saka da alkhairi." Sai da ya ji maganar da hajiya ta yi ya fahimci komai, ganin yana niyyar juyawa ta yi saurin cewa, "Ba zaka tsaya ka ci yanzu ba, awara ce na san kuma kana son ta." Hajiya ta faɗa idonta a kan sa, da hannu ya yi mata alamar zai saka riga ne daga haka ya koma ciki, sai da Salma ta tabbatar ya bar wurin sannan ta ɗago ta bi hanyar da ya koma da kallo, bayan ɗan lokaci sai gashi ya sake dawowa, singlet ce ya sako fara ƙal da ita kai ka ce a lokacin aka buɗe ta a ledarta ta kama jikinsa, a ɗayan 6angaren ya zauna yana ɗago fuskarsa suka haɗa ido da Salma, da sauri ta ɗan sunkuyar da kai tana gaishe sa ya ɗaga mata kai kawai, "Salma kai masa, sai ki je kitchen ki ɗauko masa plate." Ta amsa da to tana miƙewa, tana niyyar nufar dinning area ya dakatar da ita da hannu, ce mata ya yi ta matso masa da c-table ta ɗaura a sama, bayan ta yi kamar yadda ya ce ta wuce kitchen ta ɗauko masa plate sai da ta yi tunanin wanne yakamata ta ɗauko masa tsakanin spoon da fork, ƙarshe dukansu ta ɗauko bayan ta sake wanke su, fitowa ta yi ta nufo inda yake, bayan ta ɗaura abubuwan da ta ɗauko a saman table ɗin ta fiddo kulan awaran da roban coleslaw daga cikin ledan, har zata buɗe ta yi serving nasa wata zuciyar ta kwa6e ta da ya saka ta yin hakan? Dakatawa ta yi ta ɗago ta kalle sa ta ga shima ya kalle ta, slowly ta ce, "In zuba maka?" Kai ya ɗaga mata alamar eh, sannan ta buɗe kulan ta fiddo da roban sauce ɗin, da fork ɗin da ta ɗauko ta yi amfanin wurin zuba masa awaran, sai da ya dakatar da ita sannan ta daina zubawa, ta buɗe sauce ta sa cokali ta zuba masa da coleslaw ɗin, ɗagowa ta yi da ɗan murmushi ta ce masa gashi nan, ya ɗan lumshe ido tare da ɗaga kai a hankali ya furta, "Thank you.." Juyawa ta yi ta koma kujeran da ta taso ta zauna, "Wannan awara ta musamman ce aka haɗa maka, don daga jin ƙamshinta ba sai an faɗa ba zata yi daɗi." Hajiya ta faɗa tana murmushi, sadda kai Salma ta yi itama tana ɗan murmushi, tabbas yana da kula kan abincin da zai ci, amman ya ji lafiya lau zai iya cin abun da aka kawo masa saboda ya riga ya san awaran da ake haɗa masa yana ci sune suke yin ta, a hankali Salma take ɗan ɗagowa tana satar kallon shi yayin da ya fara cin awaran a nutse,
yarda ta ƙara ɗagowa ba, don a yadda ta gansa har tsorata ta yi ba wai don bata ta6a ganin namiji ba riga ba, wannan ma ta saba gani wurin su Auwalu da Sagir, sai dai akwai bambancin ƙirar jiki a tsakaninsu da Deen nesa ba kusa ba, gaba ɗaya a murɗe yake ga six-pack din cikinsa sun fito baro baro, fatar jikinsa fara tass da ita ba ko ɗan ta6o, yadda cikinsa yake a ɗame tamkar baya cin abinci, maido idonsa ya yi ya sake kallon ledan da ɗan alamun mamaki akan fuskar tasa, "Tukuici ne aka aiko maka, ta ce in taya su yi maka godiya ka basu kuɗi. Allah Ya saka da alkhairi." Sai da ya ji maganar da hajiya ta yi ya fahimci komai, ganin yana niyyar juyawa ta yi saurin cewa, "Ba zaka tsaya ka ci yanzu ba, awara ce na san kuma kana son ta." Hajiya ta faɗa idonta a kan sa, da hannu ya yi mata alamar zai saka riga ne daga haka ya koma ciki, sai da Salma ta tabbatar ya bar wurin sannan ta ɗago ta bi hanyar da ya koma da kallo, bayan ɗan lokaci sai gashi ya sake dawowa, singlet ce ya sako fara ƙal da ita kai ka ce a lokacin aka buɗe ta a ledarta ta kama jikinsa, a ɗayan 6angaren ya zauna yana ɗago fuskarsa suka haɗa ido da Salma, da sauri ta ɗan sunkuyar da kai tana gaishe sa ya ɗaga mata kai kawai, "Salma kai masa, sai ki je kitchen ki ɗauko masa plate." Ta amsa da to tana miƙewa, tana niyyar nufar dinning area ya dakatar da ita da hannu, ce mata ya yi ta matso masa da c-table ta ɗaura a sama, bayan ta yi kamar yadda ya ce ta wuce kitchen ta ɗauko masa plate sai da ta yi tunanin wanne yakamata ta ɗauko masa tsakanin spoon da fork, ƙarshe dukansu ta ɗauko bayan ta sake wanke su, fitowa ta yi ta nufo inda yake, bayan ta ɗaura abubuwan da ta ɗauko a saman table ɗin ta fiddo kulan awaran da roban coleslaw daga cikin ledan, har zata buɗe ta yi serving nasa wata zuciyar ta kwa6e ta da ya saka ta yin hakan? Dakatawa ta yi ta ɗago ta kalle sa ta ga shima ya kalle ta, slowly ta ce, "In zuba maka?" Kai ya ɗaga mata alamar eh, sannan ta buɗe kulan ta fiddo da roban sauce ɗin, da fork ɗin da ta ɗauko ta yi amfanin wurin zuba masa awaran, sai da ya dakatar da ita sannan ta daina zubawa, ta buɗe sauce ta sa cokali ta zuba masa da coleslaw ɗin, ɗagowa ta yi da ɗan murmushi ta ce masa gashi nan, ya ɗan lumshe ido tare da ɗaga kai a hankali ya furta, "Thank you.." Juyawa ta yi ta koma kujeran da ta taso ta zauna, "Wannan awara ta musamman ce aka haɗa maka, don daga jin ƙamshinta ba sai an faɗa ba zata yi daɗi." Hajiya ta faɗa tana murmushi, sadda kai Salma ta yi itama tana ɗan murmushi, tabbas yana da kula kan abincin da zai ci, amman ya ji lafiya lau zai iya cin abun da aka kawo masa saboda ya riga ya san awaran da ake haɗa masa yana ci sune suke yin ta, a hankali Salma take ɗan ɗagowa tana satar kallon shi yayin da ya fara cin awaran a nutse,