Sashe 43
A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Fahad wai bazaka buɗe baki ka gaya mani abun da ya haɗa ku bane? A ina ka san Salma kuma mi ta yi maka ne? Wuri na fa aka aiko ta." Ba tare da ya ce komai ba ya juya ya tafi, hajiya da Balaraba suka bi shi da ido cike da al'ajabi har ya shige ciki inda ɗakuna suke, maido kallon ta ta yi kan Salma ta matsa tare da dafa ta ta ce ta faɗi mata mi ya haɗa su, sam ta kasa magana sai kuka take yi tare da ƴar ajiyar zuciya, hajiya ta fahimci jin nauyin faɗi mata take yi, kallon inda Deen yake zaune yana kallon duk abun da ke faruwa ta yi ta ce, "Ko ka san abun da ya haɗa su ne?" Ɗan yamutsa fuska ya yi ya ce ba komai ya sani ba amman ita yarinyan ai ta san mi ya haɗa ta da shi ta faɗi mata mana, zaunar da Salma ta yi saman kujera mai mazaunin mutum biyu itama hajiya ta zauna, hannunta akan kafaɗarta cikin sigar rarrashi ta ce mata kar ta ji komai ta faɗi mata abun da ya haɗa su zata fahimta, dakatawa ta yi da murzar idon da take yi da gyalenta tana ci gaba da yin kukan cikin zuciya tana kikkafta ido, a hankali take bin mutanen cikin falon da kallo har da Balaraba dake a can bakin kicin, tsaida idonta ta yi akan Deen daidai lokacin ya yi mata kallon ƙasan ido, da sauri ta kauda idonta don sai ta ga kamar ya harare ta, "Ina jin ki Salma.." Hajiya ta faɗa,
Cikin rawar murya ta fara magana, "D...dama ɗazun ne lokacin da na dawo daga makaranta...shi..ne zan tsallaka titi na hango motar su can nesa, to..na yi tunanin har zan tsallaka basu ƙaraso ba..shine suka kusa buge ni da mota, to...shine ya leƙo yana mani magana...shi..ne..." Kasa ƙarasawa ta yi ta ci gaba da yin ajiyar zuciya tana murzar ido, hajiya ta so ta fahimci sa6ani ne ya shiga tsakanin su da abun ya faru shiyasa Salma ta kasa faɗi mata, miƙewa ta yi ta ce mata kada ta tafi ta jira tana zuwa daga haka ta nufi cikin hanyar da Fahad ɗin ya bi, gaban Salma ne ya ci gaba da bugu don ta gane wurin shi hajiyar zata je kuma ta san zai iya faɗi mata komai, ƙasa ƙasa ta ci gaba da yin kukan gyalenta a fuska,
"Kina ma wa kuka? Ko wani ya sa ki ne ki yi mashi rashin kunyan?" Kamar daga sama ta tsinkayi muryar Deen ya faɗi hakan, cire gyalen ta yi daga fuskarta ta kalle shi da jiƙaƙƙun idanuwa, ɗage mata gira ya yi ya sake cewa, "You caused it, so what's the point of crying now?"
Cikin muryar kuka ta ce, "Ai ni ba rashin kunya na yi mashi ba wllh, tun farko saida na bashi haƙuri amman shine ya ce mani dabba mara hankali, kuma farko ni bance mashi komai ba shine ya sake ce mani mara kunya..." Shiru ta yi tana kikkafta ido tana ɗan nishin kuka,
"Sai kika nuna mashi ke mara kunyan ne?" Ya ɗage mata gira, girgiza masa kai ta yi tana motsa baki, ta sa gyale tana goge ƙwallan da suka zubo mata ba tare da ta ce komai ba, ɗan ta6e baki ya yi ya ci gaba da ta6a wayan shi.......
*Littafin A Cikin Rayuwa kashi na farko zai zo maku a kyauta, ga mai buƙatar kashi na biyu zai biya 500 kacal. Domin neman ƙarin bayani a tuntubi waɗannan lambobin ta hanyar aika saƙon whatsApp kawai banda kira, 09013804524, 08169856268*
*_✨A CIKIN RAYUWA✨_*
ZAINAB BATURE
_Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai._
Page 15
Dawowa hajiya ta yi ta nufo cikin falon tana gyara zama glasses dinta tare da faɗin, "Kai, abun dai bai yi dadi ba sam, ni bana son abun tashin hankali wllh..." Tsayawa ta yi ba tare da ta ƙaraso cikin falon ba ta ce, "Salma ta so kin ji." Miƙewa ta yi tana gyara gyalenta ta nufi hajiyar, kama hannunta ta yi suka koma hanyar da ta fito, cikin corridor ɗin da ɗakuna suke suka nufa, wata ƙofa hajiya ta tura suka ta shiga tana riƙe da hannun Salma, wani irin sanyin ac da ƙamshi ne suka karade cikin ɗakin, gaban Salma ne ya faɗi ganin Fahad ɗin kwance a saman lafiyayyan gadon ɗakin ya kwanta rigingine tare da rufe idanun shi,
"Zo ki bashi haƙuri, ai durƙusa ma wada ba gajiyawa bane, balle ma wannan ba wadan bane, shi bin na gaba bin Allah ne." A ɗarare Salma ta matsa daga bakin gadon ta durƙusa ƙasa, idanunta cike da ƙwalla cikin rawar murya ta furta, "D...don Allah Ka yi haƙuri." Shiru kaman bai san da su a wurin ba don ko motsawa bai yi ba,
"Fahad, baka ji ana magana ba."Hajiya dake tsaye bakin gadon ta faɗa idanunta akan shi, sai da aka ɗan ɗauki lokaci sannan ya bude idanunsa da har sun ɗan sauya kala, nuni hajiya ta yi mashi da Salma ta ce mashi gata nan tana bashi haƙuri, ɗaura idanunsa ya yi akanta still tana durƙushe suka haɗa ido ya wani ƙara tamke fuska, "Ka yi haƙuri don Allah..." Ta faɗa tana sussune kai tare da kai hannu tana ta6a gefen fuskarta, ɗauke idanun shi ya yi ba tare da ya ce komai ba, hajiya ce ta ƙara ce mashi ya yi shiru sannan a taƙaice ya ce, "Ta je." Sanin yana da zuciya ya sa hajiya yin ɗan murmushi ta ce, "Ka haƙura ko?" Shiru ya ɗan yi kafin ya ɗan ɗaga hannu, hajiya ta ce, "Ba shike nan ba, taso to Salma." Miƙewa ta yi suka nufi ƙofa, a hankali ya juya yana kallon bayan su har lokacin fuskar shi a ɗaure take, can ƙasan maƙoshi ya ɗan ja guntun tsoki bayan sun fita.
Cikin falon suka dawo Deen ya ɗaga ido yana kallon su, wuri hajiya ta nuna ma Salma ta ce ta zauna itama ta zauna, "Ta bashi haƙuri ba shike nan ba, dama duk sharrin zuciya ne ba wani abu ba, da kuma shaiɗan da bai son ya ga an zauna lafiya." Hajiya ta faɗa tana daga hannu idanunta akan Deen, ɗan murmushin gefe Deen ya yi ya ɗauke idonsa daga kan su, bayan ɗan lokaci Salma ta miƙe tana kallon hajiya ta ce mata zata tafi gida,
"To shike nan Salma na gode. Komi ya wuce kada ma ki yi maganar a gida kin ji ko. Kuma daga yau kada ki sake yi ma babba haka, idan babba ya yi maka abu ka rama people will see you as disrespectful, don haka koda abu bai yi maka daɗi ba, in dai babba ne ya yi maka ka yi haƙuri ya fi kuma hakan ba faɗuwa bane, kin ji?" Kai ta ɗaga a sanyaye ta ce, "In sha Allahu ba zan ƙara ba." Hajiya ta ce, "Yauwa Salma, dama na san ba halin ki bane, kawai sharrin zuciya ne." Shiru Salma ta yi kafin a hankali ta ce mata sai anjima ta juya ta nufi kofa, "Salma ɗan dakata, bari a kawo maki robar...koda yake je ki ma kawai zan aiko a kawo harda saƙo." Kai ta jinjina ta ci gaba da tafiya, tana zuwa ƙofa zata fita, a hankali ta juya da niyyar ta saci kallon Deen, kamar an ce shima ya ɗago karaf suka haɗa ido da sauri ta juya ta fuce, ya yi kaman zai yi murmushi ganin yadda ta yi.
Miƙewa ya yi zai bar falon hajiya ta ce halan ya gaji da zaman, shafa sumar shi ya yi ya ce mata zai je ya shirya ne za su je gidan su Fahad,
"Ko ku bari zuwa bayan magrib don ga awara can ana haɗa maku kuma tafi daɗi mutum ya ci ana gama soyawa, na san dai ba wani ƙoshin kirki kuka yi ba, bama kamar kai nasan ka baka wasa da abinci, dama ana cewa ƴan ƙwallo cin tsiya ne da ku. To dama yadda kuke jijjige jiki ma ai dole ku ci abinci." Murmushi kawai ya yi ba tare da ya ce komai ba ya juya ya nufi hanyar corridor.
Cikin sauri take tafiya bayan da ta fito daga cikin gidan, lokacin da ta shigo kwanar gidan su ta hango su Sagir acan saman dandamalin gidan dake kallon gidansu, su da yawa suna ta hargowa, ashe baya a gida, tun yana gama cin abinci bai daɗe da kwanciya ba wani abokinsa ya kira sa yake sanar masa game da zuwan Deen, aikuwa wuff ya tashi, rigarsa ma a ƙofar gida ya ƙarasa saka ta, lokacin da Salma ta shiga gidan hajiya yana a cikin mutanen da ta gani a wurin parking space don da bala'e sai da ya yi yadda ya samu suka shiga, zaman da suka yi a nan tattaunawa suke akan ganawar da suka yi da Deen ɗin inda ya yi masu albishir da zai kafa sabon club ɗin shi anan Funtua shine ya basu za6in sunan da suke son a saka ma club din shine fa ake ta musayar ra'ayi kamar za su tashi sama don daɗi, ko kallon su Salma bata yi ba lokacin da ta ƙaraso saitin su ta wuce zata shiga gida,
"Ke, Salma zo nan..." Banza ta mashi ko juyowa bata yi ba,
Cikin rawar murya ta fara magana, "D...dama ɗazun ne lokacin da na dawo daga makaranta...shi..ne zan tsallaka titi na hango motar su can nesa, to..na yi tunanin har zan tsallaka basu ƙaraso ba..shine suka kusa buge ni da mota, to...shine ya leƙo yana mani magana...shi..ne..." Kasa ƙarasawa ta yi ta ci gaba da yin ajiyar zuciya tana murzar ido, hajiya ta so ta fahimci sa6ani ne ya shiga tsakanin su da abun ya faru shiyasa Salma ta kasa faɗi mata, miƙewa ta yi ta ce mata kada ta tafi ta jira tana zuwa daga haka ta nufi cikin hanyar da Fahad ɗin ya bi, gaban Salma ne ya ci gaba da bugu don ta gane wurin shi hajiyar zata je kuma ta san zai iya faɗi mata komai, ƙasa ƙasa ta ci gaba da yin kukan gyalenta a fuska,
"Kina ma wa kuka? Ko wani ya sa ki ne ki yi mashi rashin kunyan?" Kamar daga sama ta tsinkayi muryar Deen ya faɗi hakan, cire gyalen ta yi daga fuskarta ta kalle shi da jiƙaƙƙun idanuwa, ɗage mata gira ya yi ya sake cewa, "You caused it, so what's the point of crying now?"
Cikin muryar kuka ta ce, "Ai ni ba rashin kunya na yi mashi ba wllh, tun farko saida na bashi haƙuri amman shine ya ce mani dabba mara hankali, kuma farko ni bance mashi komai ba shine ya sake ce mani mara kunya..." Shiru ta yi tana kikkafta ido tana ɗan nishin kuka,
"Sai kika nuna mashi ke mara kunyan ne?" Ya ɗage mata gira, girgiza masa kai ta yi tana motsa baki, ta sa gyale tana goge ƙwallan da suka zubo mata ba tare da ta ce komai ba, ɗan ta6e baki ya yi ya ci gaba da ta6a wayan shi.......
*Littafin A Cikin Rayuwa kashi na farko zai zo maku a kyauta, ga mai buƙatar kashi na biyu zai biya 500 kacal. Domin neman ƙarin bayani a tuntubi waɗannan lambobin ta hanyar aika saƙon whatsApp kawai banda kira, 09013804524, 08169856268*
*_✨A CIKIN RAYUWA✨_*
ZAINAB BATURE
_Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai._
Page 15
Dawowa hajiya ta yi ta nufo cikin falon tana gyara zama glasses dinta tare da faɗin, "Kai, abun dai bai yi dadi ba sam, ni bana son abun tashin hankali wllh..." Tsayawa ta yi ba tare da ta ƙaraso cikin falon ba ta ce, "Salma ta so kin ji." Miƙewa ta yi tana gyara gyalenta ta nufi hajiyar, kama hannunta ta yi suka koma hanyar da ta fito, cikin corridor ɗin da ɗakuna suke suka nufa, wata ƙofa hajiya ta tura suka ta shiga tana riƙe da hannun Salma, wani irin sanyin ac da ƙamshi ne suka karade cikin ɗakin, gaban Salma ne ya faɗi ganin Fahad ɗin kwance a saman lafiyayyan gadon ɗakin ya kwanta rigingine tare da rufe idanun shi,
"Zo ki bashi haƙuri, ai durƙusa ma wada ba gajiyawa bane, balle ma wannan ba wadan bane, shi bin na gaba bin Allah ne." A ɗarare Salma ta matsa daga bakin gadon ta durƙusa ƙasa, idanunta cike da ƙwalla cikin rawar murya ta furta, "D...don Allah Ka yi haƙuri." Shiru kaman bai san da su a wurin ba don ko motsawa bai yi ba,
"Fahad, baka ji ana magana ba."Hajiya dake tsaye bakin gadon ta faɗa idanunta akan shi, sai da aka ɗan ɗauki lokaci sannan ya bude idanunsa da har sun ɗan sauya kala, nuni hajiya ta yi mashi da Salma ta ce mashi gata nan tana bashi haƙuri, ɗaura idanunsa ya yi akanta still tana durƙushe suka haɗa ido ya wani ƙara tamke fuska, "Ka yi haƙuri don Allah..." Ta faɗa tana sussune kai tare da kai hannu tana ta6a gefen fuskarta, ɗauke idanun shi ya yi ba tare da ya ce komai ba, hajiya ce ta ƙara ce mashi ya yi shiru sannan a taƙaice ya ce, "Ta je." Sanin yana da zuciya ya sa hajiya yin ɗan murmushi ta ce, "Ka haƙura ko?" Shiru ya ɗan yi kafin ya ɗan ɗaga hannu, hajiya ta ce, "Ba shike nan ba, taso to Salma." Miƙewa ta yi suka nufi ƙofa, a hankali ya juya yana kallon bayan su har lokacin fuskar shi a ɗaure take, can ƙasan maƙoshi ya ɗan ja guntun tsoki bayan sun fita.
Cikin falon suka dawo Deen ya ɗaga ido yana kallon su, wuri hajiya ta nuna ma Salma ta ce ta zauna itama ta zauna, "Ta bashi haƙuri ba shike nan ba, dama duk sharrin zuciya ne ba wani abu ba, da kuma shaiɗan da bai son ya ga an zauna lafiya." Hajiya ta faɗa tana daga hannu idanunta akan Deen, ɗan murmushin gefe Deen ya yi ya ɗauke idonsa daga kan su, bayan ɗan lokaci Salma ta miƙe tana kallon hajiya ta ce mata zata tafi gida,
"To shike nan Salma na gode. Komi ya wuce kada ma ki yi maganar a gida kin ji ko. Kuma daga yau kada ki sake yi ma babba haka, idan babba ya yi maka abu ka rama people will see you as disrespectful, don haka koda abu bai yi maka daɗi ba, in dai babba ne ya yi maka ka yi haƙuri ya fi kuma hakan ba faɗuwa bane, kin ji?" Kai ta ɗaga a sanyaye ta ce, "In sha Allahu ba zan ƙara ba." Hajiya ta ce, "Yauwa Salma, dama na san ba halin ki bane, kawai sharrin zuciya ne." Shiru Salma ta yi kafin a hankali ta ce mata sai anjima ta juya ta nufi kofa, "Salma ɗan dakata, bari a kawo maki robar...koda yake je ki ma kawai zan aiko a kawo harda saƙo." Kai ta jinjina ta ci gaba da tafiya, tana zuwa ƙofa zata fita, a hankali ta juya da niyyar ta saci kallon Deen, kamar an ce shima ya ɗago karaf suka haɗa ido da sauri ta juya ta fuce, ya yi kaman zai yi murmushi ganin yadda ta yi.
Miƙewa ya yi zai bar falon hajiya ta ce halan ya gaji da zaman, shafa sumar shi ya yi ya ce mata zai je ya shirya ne za su je gidan su Fahad,
"Ko ku bari zuwa bayan magrib don ga awara can ana haɗa maku kuma tafi daɗi mutum ya ci ana gama soyawa, na san dai ba wani ƙoshin kirki kuka yi ba, bama kamar kai nasan ka baka wasa da abinci, dama ana cewa ƴan ƙwallo cin tsiya ne da ku. To dama yadda kuke jijjige jiki ma ai dole ku ci abinci." Murmushi kawai ya yi ba tare da ya ce komai ba ya juya ya nufi hanyar corridor.
Cikin sauri take tafiya bayan da ta fito daga cikin gidan, lokacin da ta shigo kwanar gidan su ta hango su Sagir acan saman dandamalin gidan dake kallon gidansu, su da yawa suna ta hargowa, ashe baya a gida, tun yana gama cin abinci bai daɗe da kwanciya ba wani abokinsa ya kira sa yake sanar masa game da zuwan Deen, aikuwa wuff ya tashi, rigarsa ma a ƙofar gida ya ƙarasa saka ta, lokacin da Salma ta shiga gidan hajiya yana a cikin mutanen da ta gani a wurin parking space don da bala'e sai da ya yi yadda ya samu suka shiga, zaman da suka yi a nan tattaunawa suke akan ganawar da suka yi da Deen ɗin inda ya yi masu albishir da zai kafa sabon club ɗin shi anan Funtua shine ya basu za6in sunan da suke son a saka ma club din shine fa ake ta musayar ra'ayi kamar za su tashi sama don daɗi, ko kallon su Salma bata yi ba lokacin da ta ƙaraso saitin su ta wuce zata shiga gida,
"Ke, Salma zo nan..." Banza ta mashi ko juyowa bata yi ba,