← Book details Tumfafiya Uwar Kwankwamai Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 286

Sashe 9

Tumfafiya Uwar Kwankwamai Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

To Allah yaba amare da uwargida ikon ganawa da maman yusuf likitan mata yasa a dace da abinda ake nema a wurinta amin gadai hajiya mama ta fara baiya a gidan mayana. Maimunatu ina dai lafiya kira haka da wanan uban safiyan haka har kin ban tsoro gaba yana faduwa ina badai wani abin bane yafaru kuma ? Tsuki mama din taja tana fadin wallahi wanan banzan hjy kariman tazo jiya ta hanani barci da dadi da wani zance nata mara dadi akan maamah. Maamah dai yar nata ta fada cikin tsigan tambaya wallahi wani tuni tayi min kan yarinyar nan wai mun kusa samun sarakai gwanoni ko wasu hamshakai akan maamah din. Ai keda bakisan da hakan yana tafe gareku bane kome kike nufi kinsan fa maamah din nan ta faye shegen kyau da daukan idon duk inda ta shiga. Aina dauka kin gama da wanan babinko tuntuni don banji kina wanan zancen ba ga mazan yanzu kinsa su da sa ido ga mace mai irin dirin yarinyar nan taku idan bamuyi hankaliba sai kiga tazo tafi su Nana samun daki. Don Allah bari maganan nan ina raye har haka zai faru da diyana aikoda sayen miji ake zanje na sayowa su nana mijin da kudina nagani a fada na shiga tsara. Nasan zaki iya ai basai kin fada ba to yanzu dai sai na shigo ke nan ko kema ai kin sani tunda har na kiraki don wanan zancen ya tsaya mun a raina sosai wallahi. Barin shigo sai mu san yaya za ayi ki dubi hanyata zuwa gobe insha Allahu da sauri hjy maimuna tace anya gobe baiyi nisa ba kuwa dadina dake ke nan yar uwanta fada. Sun dai aje nagana zata ganta ko yau ko gobe da haka suka aje wayan suka rabu cewa zata shigo koda zuwa yammane insha Allahu. Gari ya haska ummah tashigo dubani ta sameni zaune ina addua take fadin kin kin samu tashi ke nan eh na bata amsa ina gaida ita da kwana ta amsa min tare da tambayana kaina nace da sauki. Allah ya kara sauki tayi min tana juyawa sai kuma ta tsaya tana fadin zakiko shiga school yau nace insha Allahu ummah ina mikewa to kifito ki karya da wuri kada ki makara ta fada ta fita. Mikewa nayi na nade abin sallah kafin nafara kokarin zame dogon rigan dake jikina ya rage sai dan wandon tie dake daga kasana ban dakin na fada nayi wanka kafin na fito na fara shiri. Sannu a hankali naji ciwon kan daya dameni jiya yana dawo min amma haka na daure na nufi wurin ummah dake zaune falo tana sallaman kannena zuwa makaranta. Zama nayi kujeran dake gefen wanda mamake zaune na dafe kai banyi magana ba har saida ummah ta fahinci hakan ta dago kai tana tambayana lafiya kike kuwa maa,ma ? Kaina dago da idanuwana da sukarine na girgiza kai ina nuna mata kaina da kamar ya tsage don ciwo kanne kuma ya kara tashi ta fada cikin dan rudewa. Wanan wani irin ciwom kaine haka ki karya muje asibiti zaifi a dubaki a can tea din da ummah tasa aka kawo min na kasa sha karshe da kuka haka na kwanta kife har ummah ta fita ta kira mai aikinta tabar mata kula da part ta kamani muka fita zuwa asibitin da ita. Magani aka bani muka dawo gida mun samu yan gidan sun tashi daga kwana don mama bata da karamin yaron yanzu don haka bata bude part din da safe sai sun shaki barcin su na safe kafin su bude wurin su. Ban san ya akayi ba mama taji cewa mun tafi asibiti da ummah sai gata a part din mu tana fada daga dakin nake jiyo muryanta sama sama tana fadin. Salma na gane yanzun kina son nuna min bani na haifi maamah ba da har za a kai yarinyar nan asibiti ina gidan nan ban sani ba. Nina isa in rabaki da yarki kawao dai ganin yadda ta kwanane kuma lokacin baki tashi ba da safe yasa na dauke ta zuwa asibitin do kada na katse maki barcin ki. Amma ai ciwo ya kauwar da komai ko kedai kin nuna min kece kika haifi abinki kawai yasa kikai min hakana ko yanzu din dan murmushi ummah tayi amma bata bata hakkuri irin yadda suka saba ba . Ta dai shigo inda nake kwance ta dubeni tayi min sannu na amsa da kyar ta fito tun ina jin muryan su sama sama suna wani zancen har na daina jinsu don barcin daya daukeni a lokacin. Yinin ranan yai aikin shi dukda yasan yanayi duk da madam tayi alkawarin ba zata bashi kudin aiki shi ba haka kuma bata bashi abinci amma hakan bai hana ya tsaya yai mata aiki tsakani da Allah ba dan kayan cikin kifin daya gyara ya saka a ledan da abincin nan plate biyu da dayan mai aikin tayi dabaran sayar dana farkon da zai wuce ta diban mashi wani maizafi ya gyara masu ko ina na shagon yaje yayiwa madam sallama ya tafi. Karfe shidda da rabi ya iso gidan nasu har lokacin ya samu unguwar a hargitse musanman kofan su da bai samu gyara ba ga ruwa ya jawo shara ya tara a kofan gidan nasu. Ya shiga da sallama da ledan abinvin shi a hannu ya karasa kofan Dije dake uwar dakinta tana dan gyare gyare jin sallaman shi yasa ta dakatar da abinda takeyi lokacin. Ta dan taso da dingeshi tana fadin Amadi har ka dawo ke nan ya amsa da eh Dije yaya kafan taki yau da sauki ko ya tambayeta. Fuska ta da yamutsa kafin tace Amadi sauki saina Allah tunda ba wani magani nake shaba yanzu ledan hannunshi ya miko mata ya juya kawai zuwa dakin shi tabishi da kallo. Kafin ta nisa ta mayar da kallonta ga ledan hannun ta tana mamakin meya riko haka da dan nauyi a cikin ledan tana budewa taga hadaden abincin da suke sayarwane a ciki kulli biyu sai miya da aka zuba mai dabban a cikin bakar leda. Shiko yana fita dakin shibya nufa ya kwabe kayan jikinshi ya saka wa yan nan tsofin nasa ya dauki abinda suke gyaran kwata ya fita kofan su da kewayen su ya gyara ko ina a cikkn azama din magariba daya kawo kai a lokacin. Kiran farko ya shiga gida ya kwabe wanan kayan dayai aiki dasu ya saka wani tsohon jallabiyashi ya dauki buta yayi alwala ya nufi masallaci duk wana abinda yake Dije na kallon shi tasan kotayi mai magana miskilacinsa ba zai bari ya amsa mata ba. Takan tausayawa rayuwan jikin nata mai rayuwa da gadara kamar dan wani da wata masu fada a gari zakace koshi din dan masarautane shi idan yana rayuwa irin tasa sai ka rantse yana da jinin sarauta a jikinshi. Itama alwala tayi ra shige daki don lokacin har sauron sun fara bin kafanta daga inda take zaune din tun fitowan da tayi lokacin daya dawo ya mika mata ledan daya shigo dashi a hannun shi. Bayan ta idar ta saka idon shigowan shi duk da tasan ba lalai bane ya shigo a lokacin sai an hada isha,i yafi shigowa gidan don hakane bata damu da dawowan shiba a lokacin. Chemist din dan bayaro dake unguwarsu ya nufa inda ya da hado mashi magani na dubu daya hardana shafawan da Dije tafiso a ciki rashin kudine ke hana ya saya mata har sai ya kare ta koma nema a karshe. Yana shigowa dakin nata ya nufa ya aje ledan a gefenta kafin ya samu wuri a gefenta yana kaiwa zaune tare da jingina bayan shi a bangon dakin yana sauke ajiyan zuciya lokaci guda. Me kuma na samu dan albarka da alaman yau dai mun wayi gari a cjkin sa,a ga leda shake da abinci har da, , , , Sai kuma ta dakata ganin maganin da tayi ya kwaso mata na ciwon kafanta harda abinda tafi so a ciki man abonoke da take shafe kafan dashi ya bar mata zugi. Kai zancena gaskiya maigida kace yau muna cikin falalan ubangijine haka masha Allah a ina wanan alherin Allah ya samu haka ta tambaya tana kallon fuskan shi. Ya dan ja tsuki tare da fadin kinsan ai na Allah basa taba karewa a duniya wallahi aikin nan dana tsaya dazun na taimakawa malam tanimu har yasa na makara. Ina zuwa jami,a madam ta hauni da sababin nan nata a cikin mutane tana min tozarci a bainar jama,a a nan na samu mai zuciyar tsusayi da imani kawai ta ban abinci da kudi ban santa ba ban ma taba ganin ta a school di nan ba sai kawai ta bayar wai a kawo min. Inji Allah ke nan Dije ta fada idan tayima don ta wullakantaka a idon jama,ane ai hakan ya zama ma alheri don ba duka aka zamo daya ba dama. Akwai masu tausayi har duniya ta nade yace kwarai kuwa shine Annah yarinyar da muke aiki a tare tayi min dubura ta sayar da wacan abincin sai ta ban wanan tare da sauran canjina kinga kudin nan ya tura hannu a aljihu ya ciro sauran dari biyun da suka rage ya mikowa Dijen . Ido ta zare da sauri tana fadin kudin haka sabbi dasu yace wallahi Dije shine na dauki dubu daya na kaso maki yanzu wurin maganin nan. Kaji abin Allah ba Allah mun godema yasakawa yarinyar nan da mafificin alheri yadda ta faranta muna rai Allah ya faranta mata ranta har abada kudi haka masu yawa ? Shiru yayi yana tunane a ciki zuciyar shi kafin Dije takai hannu tana miko mashi ledan abincin a gabanshi ya kalla yana sauke ajiyan zuciya take fadin nasn bakaci komai ba a hakan ko ? Banci ba kuma ban dauki azumi ba yau dan ganin zanyi aiki da yawa sai ruwa kawai nasha a can ya fada yana mika hannu ga abincin da ya riga da yayi sanyi ko alokacin. Ha yaci abincin duk da yana jin bakin shi babu dadi lokacin ya gama ya balle maganin daya sayowa Dije din ya kora da ruwa yana hamdala kafin ya mike ya fita ruwa ya dinga dibowa a makwabtansu
Chapter 9 · 0% Book details