Sashe 180
Tumfafiya Uwar Kwankwamai Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rayuwa ke nan mutuwar yarinyar nan ya taba su mama zakace wani babban mutum ne ya mutu a lokacin ba yar jariri haka ba mundai isa nida hannatu munyi gaisuwa inda muka samu ana fama da uwar tayi hakkuri sai faman kuka take. Harda wasu yan abi yarima asha kida suma suna kukan ita dai mama nasan damuwanta damuwar yartace Aisha. Don Aisha yar gaban goshin mamace sosai a cikin yayanta koma zata iya yiwa Aisha din a rayuwa idan tana bukatan abu. Ganin yamma yayi sosai mukai masu sallama muka dawo wurin ummah don mu sallameta bata part din tana part din daddy lokacin dole muka zauna zaman jiranta kada mu tafi bamu samu sallama da ita ba asalima bata ina cikin gidan ba a lokacin . Uhmmm wai kiji min sister din nan naki daga Allah ya rabata da wahala ya karbi ran yarinyar a huta gardama wai shine take kuka haka ? Hannatu rayuwace fa ta rasa dole tayi kuka ai balle da ance shiga ran uwa yakeyi sosai tun yana ciki kinga ke nan dole ta damu kona dan lokacine. Balle ga wahalan daukan ciki gana haihuwa yaya mutum ba zaiyi kuka ba shiyasa nake ganin karfin halin irin matan nan masu daukan cikin shege a waje. Suyi wahalan daukan nauyin ciki idan sun haihu kuma kiga mace wai taje ta yarda yaron a bola don rashin imani da tausayi ko shekaran jiya naji ance an sunci yaro a cikin wani kwalbati a gidan da mukaje kitso muke jin labarin haka. Gidan gulma ke nan ai in kina neman labarin gari kije gidan kitso kona kumshi a nan zakiji labarin shege da shegiyan gari ke har kishiyan data gagara zakiji ko namijin da baya kula da matanshi ke ko wani labari na gidan kitson daya shahara a gari. Kai hannatu ashe da gaskiyane da ake fadin tashin kaka daban suke ko wurin iya tsara maganansu irin na tsufine ke din nan akwai iya lafazi a bakin nan naki yanzu dai mudake zuwa gidan kitson mune yan gulman ? Kafin tayi magana ummah ta shigo tana ganin mu mamaki ya kamata take fadin ku kuma yaushe kuka shigo daga school muka wuto zuwa nan don gobe muna da test ba zan samu shigowa da wuri ba. Aikun kyauta gara da kukazo yau din nan dan uwa zai gane kana da muhinmanci a wurin shi don baka sanin ranan dan uwa ko dadinshi sai idan wani abin bakin ciki ya sameka dan uwa ke tsayawa ya tayaka kukan hakan. Ta sake jiki kuwa Aishan don sunce tun safe da yar ta cika taki cin komai a cikinta har lokacin da na shiga dazun kara dubata abin ne akwai tausayi ummah ta fada. Gaskiya kwance muka sameta tana kuka da muka shiga saidai tana jin muryan mu ta dago tana fadin zahra kinga babyn mu tayi tafiyanta ta barmu ko ? Murmushi ummah tayi tace ai haka ta fada dana shiga dazun tace ummah zahra tana son yarinyar nan sosai jiya bakiga yadda take kafa kafa da itaba kada a dauketa ta wahala ashema duk hakan bazaiyi ba sai ta mutu. Niko naga aita huta da rikincin su dake kwance kasa tunda ace mijin ma baizo ba har yanzu andaci karfinshine yayi suna yadda mutane ke fadi agari don akwai wata yar uwanshi a unguwan mu. Kai hannatu aikece gidan kitso ko wani labari yana bakinki ku tashi dare yayi kuje gida barin kira Shehu yazo ya saukeku dama yanzu ya dawo kai motan wurin wanki da cewa wani dan yar uwar Abba daya leke shikuma wurin ummah tun yana karaminshi. Mama tayi zagi tayi koranshi har hjy saida ta saka baki amma yaki barin ummah har gashi mun girma tun muna Abuja yana karami yake zuwa hutu wurin mu. Ta daga waya ta kirashi dacewa idan ka dawo wanke motan gasu mahmah ka kaisu gida don Allah yace to gashi nan zuwa lokacin ummah ta kalleni tace ba zakije ku gaisa da Abban ku ba. Wani har nayi da idanu alaman ban son zuwa tace kuje suna nan falo da hjy karima yanzun na barsu zaune tare ummah da dai ki bari sai nayi wani zuwan kuma idan yazo. Au har yanzu baki daina wanan sakatcin naki ba ashe ubankine fa kome kikeji a ranki game dashi gara ki aje donshi ko a jikinshi duk da dai jiya ya tambayeni wai ko kema kina da cikine yaga kinyi kiba ? Ciki kuma nikan banda komai wallahi idan nayi ciki yanzu ai asirina saiya tono ina gab da zana jerabawana kuma ciki yazo min dan zugurana hannatu tayi wai na daina maganan a gaban ummah haka rashin kunyanefa. Dole dau muka nufi wurin Abba yadda ummah din ta fada hakane da hjy karima suna zaune suna hira mukayi sallama muka shiga falon nasa da ummah din ta gyara tas sai kamshin turaren shikka yake tashi a cikinsa. Suka amsa muna muka shiga hjy karimace tace a, a kune ashe kuji mutuwar yar ke nan nace eh ina school dazun ummah ta kirani tana fada min daga can shine nazo nan. Mijin naki ya dawone Abba ya tambaya a,a yana can waya mukayi dashi dai OK wanan itace kawar nan taki lokacin buki ko hjy karima ta tambaya nace eh tare da fadin Abba ya mukaji da hakkuri kuma ? To hakkuri sai Allah shiya bayar kuma ya karba sai ai fatan lafiya yanzu ga uwar nace hakane tare da fadin to zamu koma idan kun tafi Allah ya kaiku lafiya. Ai muna nan sati daya zamuyi hjy karima ta fada daga inda take zaune nace Allah sarki tau mun mike naji yace tunda mijin ki baya gari barin baki wani abu kona shiga school kya samu. Lah Abba da ke Abban naku zai maki alheri kiki karba eh to ba mamaki kinsan mijinta last donen ne ai matar mai kudin sakaine Abba ya bada amsa yana miko muna sabbin kudi yan dari biyar. Na duka na karba ina gidiya ya miko wani tare da fadin ke kuma gashi ki rike hannatu tazo da sauri ta karba tana godiya a lokacin ne hjy karima tace da motarki kikazo ko ? Naga dare ya somayi ga unguwar naku da dan nisa kai na girgiza kafin inyi magana hannatu tace ai tunda aka karbi motan da bukinta ba a mayar mata dashi ba. What kina nufin motar haya kike hawa kome da ita mukazo hannatun ta kara fadi Alh yaya akai haka za a barta tana shiga motan haya a gari ita kadai da sauri nace. Mommy hakan yafi min yanzu ma kinga na farko a yanzu ban iya laluran motar kuma gidan kingani babu inda zan aje motana ai a gidan. Dazunma kafin muzo nan muga wani yana yawo da motan ya kwaso yan mata acikinsa ai kunnena ya tsinkayi hannatu na fada a bayana. Kaji ko motar ma ba a aje matashi ba wani ke shigarta yanzu wanan son kai gaskiya da yawa yake in anyi magana kace wai wani abu da sauri na bar falon hannatu ma ta biyoni baya. Gaskiya hannatu bata taba bata min raina irin na wanan ranan ba don har nayi nadaman zuwa da ita gidan mu din a lokacin . Don haka har na kasa boyeewa saida fuskana ya nuna hakan muna komawa gun ummah na samu shehu ya iso yana jirab mu a falonta mukai sallama muka nuna mata kudin da Abban ya bamu tace angode ta mikowa ko wanin mu leda na karba ina godiya muka fito har muka shiga mota na kama hira da shehu. Ita muka fara saukewa don ina gaba da ita sai ya tafi dani har kofan gida ya kaini na sauka nayi mai godiya ya tafi ni kuma na shiga cikin gidan. Kwananshi biyu a south Africa na uku ya dawo da safe saidai ya samu ba kowa a gidan hakan yaba yar aikin daman labarta mai abinda taji daga bakin hjy yabi ranan. Ba koma nagode Asabe ki kara kula yacewa tsohuwar yau din nan matana na biyu zata iso garin nan da fatan zaki bata hadin kai a zauna lafiya banda tsegumi don Allah a tsakanin su yarda da aminci yasa na baki amana. Tsohuwar ta gyara tana fadin insha Allahu Alh nakuma gode nima ka fitar dani daga zargin ubangijina Allah don wanan abin yana damuna shekara da shekaru wallahi bandai da bakin maganane kawai. Sai daya da wani abu mutanen gidan suka fara dawowa salimace ta farko sai uwarta data dawo a gajiye lokacin sai bayan ta hutane Asabe ke fada mata ai maigidan ma ya dawo lokacin. Haka kawai taji lokaci guda gabanta ya fadi akaro na farko da ta taba jin hakan nan a zuciyarta game dashi ke nan ranan haka ta daure ta mike zuwa wajenshi saidai baya nan yana masallaci a lokacin. Bai fito ba sai bayan isowan matar nasa amaryan nasa data iso mota biyu ita da yarinyar datake tayarwa sai kanwata guda datake riko sai yayunta biyu da sukayo mata rakiya da tsohuwa daya da aka hadosu da ita daga gida. Nan aka fara shiga masu da kayansu cikin gida harsai da aka kusan gamawa sanan taji labari daga bakin yarta dataga shigowansu lokacin. Tashin hankali a sukwane ta fada dakin uwar nasu tana fadin mommy su wayene sukazo naga wasu mata na shiga da kaya wanan part din da aka gyara. Mata da kaya kuma ta tambayi yar a cikin mamaki tace eh mummy gasu can suna shiga yanzu haka da kayansu wallahi. Ai a su kwane take saukowa daga kan gado har tana hadawa da rarafe lokacin haka ta samu ta sauko daga matakala zuwa falo. Ja tayi ta tsaya wuri daya jin mijin nata yana yaren fulatanci da tsohuwar yana tambayanta mutanen gida a lokacin nan take fada mai duk suna gaidashi saida daga inda hjy yabi din take tsaye ba zata iya sheda ko wacece tsohuwar ba alokacin don ko muryanta ma bata sheda ba.. Cikin mamaki take karasowa inda suke yarta Salima tana biye a bayanta who is she daddy Salima din ta tambaya daga inda take tsaye a bayab uwarta din. Jin hakan yasa ya juyo a lokacin ya dan kallosu