Sashe 156
Tumfafiya Uwar Kwankwamai Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Barkan da wanan lokacin yan uwa musulmai ubangiji Allah ya karba muna ibadun mu Amin Allah ya bamu ikon jajircewa a wanan watan mu samu falalan dake cikin sa Allahuma Amin. Duhune ya mamaye dakin baka ganin komai a lokacin sai duhu a hankali ya dago santala talan hanayen shi ya kaisu ga makunin wutan gefen gadon dake dakin ya kuna. Hjy Yabice a gefensa kwance tana kwasab barcin ta a lokacin dan hasken daya kunna bai hanata barcinta ba a lokacin don asalima ita bata san ya kunna wanan wutan ba a lokacin. Bin dakin nasa yakeyi da kallo zakace bakoneshi a dakin ranan ya fara ganin dakin nasa don yadda yake bin ko ina na dakin da kallo lokaci guda. Hankalinshi ne ya karkata zuwa mafalkin daya tasheshi a lokacin tabbas yasan a yan kwanakin nan mafalkin wanan matashin na yawan damun shi a cikin barcin shi. Saidai ya kasa tuno inda yasan fuskan yaron mai zubi daya da nasu don yasan ba danshi yasir yake gani a mafalkin nasa ba son wanan yafi yasir din shi tsayi da haske da mugun kama dashi wurin kamanni . Mikewa yayi zuwa bandaki ya dauro alwala yana kokarin tayarda sallah lokacin ne matar nasa ta dan falka ta sauke kallonta gareshi . Idan ba gizau idon take mataba sallah yake kokarin yi a lokacin duk da mamakin sabbin halaiyan shi a yanzu nauyin barcin dake idon ta bai barta taci gaba da cigaba da mamakin nashi ba. Kamar yadda shima a yanzun yake mamakin kansancewarta matarshi don gani yake komai ya faru dashine a cikin rashin sani ko a malfaki. Iya abinda zai iya tunowa a baya shine irin tsana da tsangwaman da bangarenta suka nuna mashi a baya kasancewan shi da daya tillo daya fito a wurin mahaifiyar shi kafinta bar duniya. Da yadda ya taso a cikin shi suna nuna mai hasada da bakin ciki irin na yan uba a lokacin wanda badon shi din ya iya kanshi ba da ba yadda zai taso a gaban ita uwar rikon yabi din wace kishiyar uwane a gareshi lokacin kuma mahaifin shi ya hana bangaren uwan shi dasu daukeshi. Yabi yar kanwar Attuce data rasu tabarta tana karama a cikin yan uwanta su hudu duk Attu din ta kwasosu ta rikesu lokacin a hannun ta tana tayar dasu a cikin gidan mahaifin nasu. Kasancewanta ita din matar basarkene a lokacin kuma mai abin hannun shi don yana da dukiyanshi da abin hannunshi sosai don haka abinci bai masu wuya koya katse masu a gidan yasa ta dauko yaran ta hada da nata ta rike Akan yaran tana iya sabawa da kowa a gidan a wanan lokacin don yadda ta daukesu a ranta amma diyan mijinta kiri kiri take nuna masu kiyayyanta a fili. Kowa yayi mamakin batan habu dan gaske da suke mai lakani da hakan don kasancewan shi da daya dasha wuyan kishiyoyin uwarshi kuma yana raye a cikin su ya tashi hakana. Lokacin daya fara bude ido da kasuwanci mahaifin nasa ya dauki wani kason daya gada a wurin mahaifiyarshi sai wanan matar abin yai mata bakin ciki sosai a zuciyar ta . Duk da mijin nasu ya fahintar da ita cewa kason shine na mahaifiyar shi ya fara juyawa amma sai bata yarda da hakan ba tayi ta kokarin ganin ta hada kai da sauran iyalan gidan aiwa mijin nasu banga kan hakan sai sauran basu mai da kai ga hakan ba. Wanan yasa taje wani dutse wurin wani boka yai mata aiki suka turashi uwar duniya daga tafiya ba a kara jin duriyan shi ba kuma har tsawon wani lokaci. Fahintar hakan da amin nasa sukayi sune suka shiga suka fita sukai masa aikin dayafi nata har Allah ya dawo masu dashi gida kwatsam aka ganshi ya dawo a jirgice babu wani abinda ya dawo dashi lokacin. A binciken mahaifinsa ne ya gano cewa yayi aure acan inda yake harda karuwa amma ba hausa ya aura wanda su kuma basu son hada jinin su da hausa don sunyi yakinin cewa hausawa ba abin yarda bane. Wanan yana cikin shawaran tsohuwa mallam a lokacin ita ta shiga ta fita data gano cewa dole fa sai tabi ta wani hanya sanan bukatanta akan habu din zai biya. Don hakane ta dauki yarta datake gabanta a lokacin ta mika masa da sunan irin hadin su na fulani wanda mutane da yawa a lokacin basu so hakan ba. Saidai zaman ta mai fada aji a gidan yasa kowa yaja bakin shi yai shiru ya zura ido suga manufanta duk da sun san me hakan da tayi ke nufi amma babu halin magana akai. Shima din uban gayyan bai cikin hankalinshi don gaba daya juyashi akeyi akan komai har zuwa lokacin nan da abu ke shirin faruwa dashi din. Sallah ya tayar don neman sauki a wurin ubangiji bai daga ba har dan gyangyadi ya fara daukan shi wurin kuma anan ya sakeafalkin daya daga mashi hankali sosai. Ina zaune muna fuskantar juna da ita mamakine a fuskanta karara wanda take mamakin abinda nake fada mata din a lokacin kafin ta nisa tana fadin. Ni abinda nagani shine kifita zancen kowa zahra ki kama mijin ki tunda bashi ke maki hakan ba kuma shi har yana nuna rashin son hakan a fili kanki. Don me zan fita zancen hakan yanzu ina yake ina tare dasu ya tafi ya barni a nan zaune kinga ke nan ya zama dole in gyara zama tsakanina dasu tako wani hanya. Kaita girgiza tana fadin Zahra ke nan ki rabu da irin matan nan masu kishi da matan diyan su duk abinda zakiyi ba zataga hakan ba don idonta ya rufe ga son danta a yanzu. Tana ganin komai ya samu akanki yake karewa duk abinda yake masu bata ganin hakan ita gani take keyske kashewa ke kadai a yanzu. Kada ki rage ki kara ita irin matan nan ne masu adawa da hassada tana ganin kin fito gida akwai kin fisu kina daga masu kai ko tana ganjn kedin baki cancanci hakan ba garesu ai. Ta manta Allah ke bayarwa a inda yaga dama shike zaba yaba wanda yaso a rayuwa har ma ke wani hali itin na diyan masu kudi kike dashi zahra tunda abinki bai rufe maki ido ba ga kowa. Ita bata tunanen arzikin kine master ya shafa har ya dago yakai haka a yanzu idan ita bata san wanan ba kowa ya sani a gari don da yaya dan nata yake cikin garin nan yana yawo a kafa a talauce zabar tausayi. Murmushi nayi ina fadin hannatu ke nan wanan kuma wani hukuncine na Allah ya nuna hakan amma ai ban isa in masa arziki bani. Nasan da hakan amma mutane sun camfa hakan kuma hakan maganan yake don ko last week saida su munir sukai zancen ku irin wanan . Don haka ni in nice wallahi zan bita a yadda take son mu zauna don nasan ba zata iya sa master ya sakeki ba saidai abinda ya fito daga Allah. Hannatu bawai akan hakane na nemi shawaran kiba a yanzu na nemi sharankine naji hanyar da zan fito mata mu zauna lafiya shine dalilin dana nemeki shawara yanzu . Akan hali irin nakiba zahra na sanyin hali amma inda nice wallahi daidai zamuyi da wanan matar amma tunda kince haka yanzu ai shikenan . Shawaran da zan baki shine ki kara harkuri ki bita da halinta sai kuma yaran nan kiyi kokarin jansu a jiki kina masu dan alheri kinga insunga hakan ba zasu biye mata wurin shirmenta ba. A karshe kuma kila ita din ayi sa,a ta sauko don ance idan kana son kama uwa kaso danta fiye da ita zaka kama zuciyarta a dan kankanin lokaci. Shiru nayi ina nazarin zancen ta wanda ba komai nake tunane ba a hakan ta ina zan farane yanzu don iya bi da kyautatawa ai naga ina masu amma duk bata ganin hakan ita. Kamar tasan me nake tunane sai naji tace irin kayan ki dake aje baki amfani dasu din nan ki dan rika basu shi idan sunyi kwaliya da bai maki ba kikirasu ki gyara masu da hakan har dai ki jawosu zuwa jikin ki kubarta can tana haukan ta ita. Wallahi wanan shawaran yayi kamar kin shiga zuciyana dama kingani hannatu don ina son masu hakan ina tsoron matan nan don sam bata boye kiyayyarta gareni kada tace nabawa diyan ta kwance sha tusa don naji ranan tana zagin kanwarta da hakan data aiko mata da wasu kayan jikinta. Haba dai zahra wasu kayan ba amma ba dai irin nakiba da wasu sakawa daya ko biyu kikai masu a jikin ki ina za,a hada da wanan da nasu kilama yasha wanki ashirin albarkahakan Kai kajiki da wani zance yanzu dai zan gwada wanan shawara naki in gani idan anyi nasara zanfi kowa farin ciki da hakan. Don wallahi hannatu wanan matar ta daga min hankali sosai niba auren da tace zataiwa master bane yadameni kamar yadda take fita tana aibantani wurin mutanen ta. Kada hakan ya dameki da baki da alhakinta ai gashi har dakin ki akazo aka fada maki komai kunya kuma ya rage a gareta ranan da zata gane gaskiyan hakan. To amin na bata amsa ina mikewa na fita na debo mata abincin dana girka don zuwanta don nasan halinta bata wasa da cikinta. Na samu takai kwance lokacin tana duban wayanta dake hannunta na dire abincin a gabanta kamshin yasata dagowa tana fadin kai don haka nake sonki mutumiyar. Kamar kinsan wallahi a matse nake nan ina shirin tambayan ki ko akwai abin tabawa na taba sai gashi kin kawo min tana mikewa zaune take fadin haka . Fita nayi na dauko muna drinks da cups na kawo muna na zauna muna ci a lokacin ne Aisha ta leko part din tana fadin . Matar yaya kina cikine kin kwanta tana lekowa ta ganmu zaune a falo muna cin abinci hannun ta rugume da kayanta sai kuma ta dan dare daga kofa tana fadin ashe kina da bakuwane. Ina wuni hannuta ta amsa mata ba wani sakewa nayi saurin kawar da hakan da fadin ashe baku tafi ba aina dauka kun fita tun dazunne wallahi