Sashe 18
Tumfafiya Uwar Kwankwamai Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali nake jin muryanshi dake dawo dani cikin hankalina da har nasan inda nake a lokacin yana fadin this unfair ace komai sai kin dauka a waya haka kuna yadawa duniya. Riban me zaka samu a cikin yin hakan yanzu da kake daukanta din a haka ciwone fa ya kuma san kofan kowa anan da ace kanwance ko wata taka zaka iya yada vedio ta a haka ? Maishi yaso yaja dashi naji yace dashi kajinan wallahi duk wanan vedio din yayi link nasanka na kuma sheda fuskan ka sai mun makaka kotu. Jin hakan yasa maishi fadin kan wanan din gashi kaga a gaban ka na gogeshi ban iya wahala yace ka iya tunda baka da tauhidi kun dauki dabi,un yahudawa kun dorawa kanku don gulma. Ciwon kai din shine abinda zaka tsaya kana dauka makin kai mata addua akan hakan kowa nan yasan yadda ciwon kai mai tsanani yake ai. Ganin yadda yake fada da yadda ya tsaya ya kula dani sai yawanci suka dauka ai yasanin ne muna da wani alaka dashi dama sai gasu suna watsewa daga wurin daya bayan daya aka barmu dagani sai shi a wurin. Watace tazo wuce naji tace a, a Ahmad kana ganuwa kuwa kwana biyu kabar lekomu shago banji mai yace mata ba sai tayi dariya kawai zata wuce takallo inda nake zaune a cikin mota naji tace dashi OK ka hadu da ita ashe ? Sai a lokacin ya juyo inda nake din ya dan kalleni farine sol dashi saidai wahala ya boye hakan na gane hakane kawai don farin bai dishe duka ba gareshi yace wake nan yana kallona. Tace yarinyar ranan data saya ma abinci ta baka canji ai wanan dince itace gata tana nunoni daga inda nake zaune a cikin motan nawa ina maida numfashin wahala. Bani ruwa daya ya fada don ta dauko katon din ruwane saidai an fara taba ledan an diba yana kokarin ciro kudi a cikin aljihunshi ta miko mai tare da fadin barshi kawai lokacin daya mika mata tsohuwar dari biyun datasha takura cikin aljihunshi. Kai ya girgiza mata yana fadin ki karba kema ba naki bane ai tace bani nace ka barshi ba zan jefa mata kudin ciki ai kadai barmu ke nan yanzu gashi madam ta fara nadaman rashinka wurin mu ko jiya saida tayi maganan ka. Nabar wurin ku kenan har abada bana son harka da wullakanci gara naje na nemi wani sana,a zaifi min da cin fuskan madam kullun a kanmu. Kakafa ta tambayeshi tana nan lafiya ya bata amsa yana balle marfin ruwan daya karba a hannun ta tare da cuna mata matattan dari biyu lokaci guda da karban goran ruwan ya nufoni yana fadin. Dan sauke kafanki ki wanke fuskanki zai kara lafa maki In sha Allahu wai dama ashe kasantane haba nayi mamaki ranan nan data mika min kudi da abinci in baka ai ? Veronica please excuse us bata da lafiyane ta kalloni tana fadin ayyah sannu ko Allah ya sauka Ahmed sai gani na biyu ke nan ko duk lokacin ina jin abinda suke fada saidai surutun yarinyar yana shiga min har kasan raina a lokacin don natsuwa kawai nake son samu. Miko hannu nayi da niyar ya ban sai yace miko hannu na zuba maki ki wanke fuskanki dashi kara miko mai hannu nayi tare da kwatancen zansha. No ba zaki sha ruwa yanzu ba wanke fuskanki kawai zaki samu relief kadan ko a zuba maki a kafanki zaifi kice zakisha. Na sake kada mashi kai alaman naji da kyat na sauko da kafana kasa ina gyara gyalen dana dora a kaina lokacin don Allah ya taimakeni na yafa gyalen da kyau yana rufe min jikina. Haka bujen dake jikina ya sauka min har kasa dadin saka suturan kwarai a jiki ke nan don baka san me zai faru da kai ba tunda rayuwan mu ba a hannun mu yake ba. Taro hannun ki ya fada a cikin sound din command a gareni na tara ya zuba min ruwan tare da fadin wanke fuskanki dashi nayi yadda yace din sai ya zuba min a kafa lokaci guda na sauke ajiyan zuciya a wurin. Shi kuma yana fadin sannu yanzu ya kikejin kanki ya lafa ko har yanzu yana sarawa ya lafa na fada a kasalance har lokacin kuma akwai wasu da suka zubawa abinda mukeyi ido daga nisa suna magana saidai sunki suzo su taimaka minne su don kowa na gudun shiga wahala yanzu. A wahalce na dago kai tare da fadin na gode dan uwa bai amsa min ba sai cewan da yayi zaki iya zuwa gida da kanki kai na kada alaman eh ok shiga motan mu gani ya fada yana tsureni da idanu. Ganin yadda na koma ciki ina kokarin tayar da motan yasa shi fadin fito ki koma baya ki kwanta har kan ya dan sakeki don tuki a gareki yanzu gangancine. Yadda yake ban umurni zaki rantse shidin dan uwanane na jini ba lkkacin muka hadu dashi ba don yadda yake nuna min kulawa sosai da damuwa. Fita nayi idanuwa a kaina ya bude bayan motan na shiga ya rufe ya dawo yayi tsaye a gefe window din motan yana mazurai da idanu ga masu kallon mu lokacin. Yan mintina kadan ya duko yana fadin zaki gane gida kuwa a haka dana lalaba nakaiki gida yanzu kai na dan gyada masa dama key na jikin motan bawai sosai ya iya mota ba koshi lokacin da yayi wankin mota da yana secondary a lokacin ya koya bawai ya wani gwane bane da tukin. Haka ya lalaba ina nuna mashi hanya saida muka kusa shiga layin mu na dan jawo jakkana da kyat wayana na lalabo a ciki na dannawa ummah kira ringing uku ta dauka. Nace ummah banda lafiya gani nan wani zai kawoni gida yanzu salati ta saka tana mikewa tsaye wurin mama ta nufa ta fada mata abinda ke faruwa. Saidai tana kai kofan shiga part din taji muryan mama da yar uwanta suna zagin ta haka yasa ta juyo bata shiga ba ta nufo waje lokacin har Tani mai aikin ummah ta fita wajen. Zuwan ummah yayi daidai da isowan mu gidan an bude get din gida muna shigowa lokacin suka nufo inda motan ya tsaya sannu da kokari suke mashi ya fito yana gaidasu. Nan Tani ta bude bayan motan ta fito dani a hankali lokacin shi yanawa ummah bayanin halinda ya sameni ciki hankalin umma ya tashi sosai lokaci guda ga zancen data sama nata anayi dakin mama ga kuma wanan matsalana a yanzu. Nan tayi mai godiya suka kamani bayan ummah tace don Allah ya jira ai masa sako yace shi don Allah ya taimakeni ai badon wani abu ba. Bawan Allah mun gode don Allah ka taimaka muna da wanan maganin da kace shi ka shaka mata ta dawo daidai din kaga sai a dinga mata amfani dashi Tani ku shiga ki dauko leda ko kuma barin shigo dai ummah ta fada. Ta biyo bayan mu duk da yace bai karban kudi haka bai hana ummah bayar da dubu biyar akai mashi ba da leda amma yaki karban kudin ya dai raba maganin biyu yayi alkwarin zai karo aimun amfani dashi. Ikon Allah ashe har yanzu akwai irin yaran nan karamin yaro haka da halin manya ummah ta fada ta maida kallonta gareni kuma kafin ta nisa don abubuwan sun daure mata kai a lokaci guda haka gashi kuma bata ko karbi lamban matashin ba har ya tafi. Tsuki taja sai tani ke fadin hjy wani abin ne wallahi ya kamata ace mun amshi layin yaron nan amma rudewa yasa mun barshi ya tafi bamu karba ba. Hjy ni ai har gidan su yayi min kwantace na kuma gane layin nasu kai amma kin kyauta min Tani don in maganin yana da kyau ai dole mu nema mu aje a wurin mu don bacin rana irin haka. Barci nayi sosai ranan saidai ina tashi naji wasai ba wanan ciwon kan ko gani dishi dishi gashi na koma ina jina normal dani kamar ba abinda ya faru dani. Saidai da idan na tuna da abinda ya faru dani sai naji nauyi da kunyar hakan amma idan kuma natuno da abinda wanan matashin ya fada sai naji somehow amma aiba kowane yasan haka ba na fada ni daya a daki ina jan tsoki Itako ummah kantane ya kara daurewa sosai da lamarin mama don data fito har kofa ummah suke yarta tana sallama ummah din saiki rantse babu wani abinda ya taba hadasu ko suke shiryawa a kasa daya shafi kisantaka irin na matan da basu da hakkuri da tawakkali ga ubangiji. Shin ko sun dade suna mata wanan bata gano bane sai yanzu da ubangiji ya haska mata har taji da kunnuwanta ba wani ya fada mata ba amma sai gashi taji komai a saukake. Har da shigowa dakin suna gaida maamah da jiki sukai Allah ya sauwaka kamar da gaske sun damu bayan fitan su ta lekasu sai gashi suna dariya kamar wasu yara dasu irin nuna sam basu damu ba su. Ranan haka ummah ta kwana cikin damuwa da tashin hankali har gari ya waye tun kan tayi sallah saida ta leka dakina ta tasheni da barci na tashi nayi sallah. Sam ummah bata zata zan samu zuwa makaranta ba a ranan sai gashi na fito da shirina ina sallaman ummah din bata yarda na fita gida ba saida ta tabbatar da cewa na karya kafin na fita. Dkn Tani bata riga da ta iso ba a lokacin don haka ummah ta hada min shayi da ruwan flask din dake dakinta ruwan tea din kawai nasha ban hada da komai ba nasha na fita. Tani don damuwan data kwana dashi bata zo gidan mu ba direct data fito sai ta wuce gidan wanan matashin don ta karbo maganin tayi sa,a ta sameshi ya fito zai tafi school. Saida ta tuna mai ko ita wacece tare da fada mai sakon hjy yasa ya dubi lokaci yace su shiga daga ciki tabi bayan shi zuwa cikin gidan tana bin ko ina na gidan da kallon mamakin iri rayuwan talaucin da bayin Allah nan keyi a cikin gidan nasu. Ke nan