Sashe 99
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gudidi ta katseta da fad’in “Kinfi Murja sonta ne..? Dashike ba d’anki aka so lik’awa ba dole Ki wani marairaice kice ke tausayi kike... Itama yarinyar inace iyayenta b’arayin daji ne yo koma su waye ta aura ai ‘yan ta’adda ne ‘yan uwanta... Kinga idan har kina k’aunar Murja a matsayin k’awa zaki taimaka min mu fitar da wannan annobar yarinyar daga cikin rayuwarta....!!” Ta k’arashe cikin huci..
Jiki a sanyaye Salame ta k’arasa ta tallafi b’angare guda na Muhibbah Gudidi na rik’eda b’angare guda suka fito da ita suna janyota kanta rufe da mayafi....A haka suka fakaice idanun mutane da hankalinsu ya tafi ga masu busa dan tuni an soma dawowa daga wajen d’aurin aure ga labaru daban daban na tashi na irin d’aurin auren da akai.... Sai sannan ne Mommy take jin Wai ma wasu fataken Buzaye Yawale ya bada auren Muhibbah... Hankali tashe Mommy Ke kuma tambayar mutanen dake wajen yanda al’amarin auren ya kasance...
Tuni su Gudidi Sun fita Ta can bayan layin suna jan Muhibbah da k’yar da k’yar har dai suka hango Yawale tsaye jikin wata mota.... Yawale ya d’ago masu hannu yace su k’araso...
Tuni suka k’arasa yanda motar take... Take Barde ya fito ya bud’e masu d’aya b’angaren da babu kowa suka ajeta ciki gefeda Mahmood... Itadai Salame tsoron mutanen ne ma ya rufeta, jikinta har rawa yake tana alla alla su bar wajen... Suna ajeta Barde ya maida k’ofar mota ya rufe yai sallama da Yawale....
Suka koma gefe suna kallo aka tafi da Muhibbah Yawale na Washe baki yana fad’in “An yarda k’wallan mangoro an huta da k’uda...!” Harda d’aga hannu yana waving motar...
Guididi ma Ta tintsire da dariya tana tayasa da fad’in “A k’are can a duniyar matsafa dan wannan daga gani ‘yan shan jini ne suka sayi yarinyar nan...!”
Yawale yai shiru kaman mai nazari sai ya jinjina kai yana mai tabbatarda maganan Gudidi da tace ‘yan shan jini ne suka sayi Muhibbah dan ya tuna mak’udan zinarin da suka bada matsayin sadakinta, sai yanzu yake ciza yatsa dama ya saida masu ita da tsada da yanzu yayi dukiya, amma dukda haka ya samu ai, sannan ga Hameedarsa zata auri Ansar d’an Hajiya Murjah...
Mommy a fujajan ta nufi d’aki yanda aka kulle Muhibbah saidai babu Muhibbah babu dalilinta... Take taji wasu irin hawaye na zuwa mata, Ta shiga bud’e k’ofofi tana ambato sunan Muhibbah mutane na kallon ikon Allah...
Shigowarsu Salame da Gudidi yasa Mommy ta nufesu tana tambayarsu ko sunga Muhibbah... Salame na k’ok’arin danne kukanta take girgiza kai, lokaci guda take furta “Murjah Muhibbah ta tafi... Ta tafi kuma bazaki sake ganinta ba..!” Ta k’arashe hawaye na gangaro mata...
Tamkar mutum mutumi haka Mommy ke dubansu hawaye basu daina ambaliya a fuskarta ba... Cikin wane irin zabura tasa kai Ta nufi waje tana fad’in “Ina suke... Na fasa na fasa aura masu Muhibbah... Ku dawo min da d’iyata wllhi na fasa..!!”
Gudidi tai ta maza ta kamo Mommy ta dawo da ita cikin gida... Gidan biki dai ya kacame da maganganu da hargitsi... Wannan kenan..!
**
Tunda suka d’au hanya ya kasa janye idanunsa daga kanta, tsananin tausayinta yakeji na taso masa daga can k’asar zuciyarsa.... Idan da ace bai aureta ba tabbas wad’annan mugayen mutane da Sun bayar da ita ma ko wane irin mutum, tabbas zasu iya salwantar da rayuwarta sabida son zuciya... A hankali harshensa ya furta “You’re safe now..!” Dai dai lokacin da aka d’ale speed bump abinka da mai bacci sai ta fad’o cikin jikinsa tai matashi da k’irjinsa... Dukda bacci take yana Iya jin bugun zuciyarta cikin nasa k’irjin, tamkar zukatan nasu lokaci guda suke bugawa... Yanayin da ya jima bai tsinci kansa ciki ba ya ziyarcesa.... A hankali yake k’ok’arin kai hannu jikinta yana son gyara mata kwanciyar zuciyarsa naci gaba da harbawa... Wai fah ita d’in matarsa ce yanzu, ji yake kaman idan ya tab’ata zata farka.... Ya maida hannunsa ya ajesu ba tareda ya gyara mata kwanciyar ba, tana nan kwance cikin k’irjinsa.... Burki da Turaki ya d’an ja ne ya sanyata zamowa daga kan k’irjinsa zuwa cinyarsa.... Yai mata K’uri yana dubanta, wane irin duba yake mata wanda ko iya janye idanunsa baiyi, a hankali ya kai hannunsa yana k’ok’arin yaye rufin dake fuskarta.... Sannu a hankali yake janye mayafin hardai fuskarta ya bayyana... Zuciyarsa ta kuma bugawa lokaci guda, fuskar nata fayu babu ko kwalliya tamkar ba Amarya ba, hasalima a kod’e fuskar tata take irin na wanda yaci kuka harda sauran busassun hawaye a fuskar nata... Dogayen bak’ak’en gashin idanunta da sukayi marfi wa manyan idanun nata duk sun shige cikin juna alamu kuka taci sosai, idanunsa suka sauk’o kan labb’anta masu d’an duhu kad’an wanda kaman an zane k’arshensu da liner... A hankali ya lumshe idanunsa yana mai k’ok’arin janye fuskarsa daga barin dubanta, nan idanunsa suka sauk’a kan hannunta da yasha zanen flowers na lalle dunk’ule da wata ‘yar takarda... Yai K’uri yana duban hannun nata... Duk wannan bacci da take takardan na nan mak’ale cikin hannunta bai fad’i ba... Daga gani ba rik’on wasa taiwa takardan ba...
Mahmood yakai hannunsa yana k’ok’arin bud’e hannun nata dake dunk’ule da takardar...
A hankali ya warware hannun nata har ya ciro takardan... Gabansa ya buga kikaci guda sanda ya warware takardan... Zanen ginin gidan sarautar nan ya gani... Take mafarkin da yayi da ita tana guduwa da zanen ya shiga dawo masa... Ikon Allah..! Wato dai mafarkinsa ta tabbata gaskiya... Yarinyar nan tanada wani agenda d’inta cikin gidan...! Toh ya akai irin zanen da Wambai ya basa ya fad’o hannunta... Mai takeyi da zanen..? Kuma a ina Ta samu..?! Tambayoyin da suka tsaya masa a rai har suka isa masarauta...
Lokacinda suka hankulan d’aukacin jama’an Masarautar naga hidindimun bikukuna da ake sannan wata labari da d’umi d’umi ta iso Masarautar cewa auren Raheemah dai ba da Mahmood aka d’aura ba da K’aninsa Yazeed aka d’aura...
Wannan hargitsi yasa har Mahmood ya ciccib’i amaryarsa ya shige da ita sashen da ya tanada na musamman Don ajeta ciki...
Yana fitowa ya tadda Barde da Turaki har sun sauya shiga suma, take ya kuma jaddada masu cewa babu wanda zaisan batun aurensa da Muhibbah..!
Barde ya jinjina kai cikeda risinawa yana mai tabbatar masa amincinsa garesa...!
Mahmood ya jinjina kai yace “Ina Kuyangin dana ce ka ware mun su...?!”
Barde ya kuma risinawa yace “Allah shi baka yawan rai suna nan waje suna jiran umarninka...!”
Nan ma jinjina kai yayi yace “Kasan sashen da na ajeta ai..?!”
Barde ya jinjina kai yace “K’warai Rankaidad’e...!”
Mahmood ya kuma daidaita tsayuwarsa yace “Akai Kuyangin wajen, aikinsu kenan su dinga kula da ita, kama daga abinda zataci zuwa komai na buk’atarta... Koda wasa kada a bari ta lek’o koda k’ofa ne har sai idan ni ne na umarta..!”
Barde ya kuma risinawa yace “An gama Allah shi taimakeka...! Jaaa zamaninka dogon Sarki mai dogon zamani..!” Ya gama kirariwa Ubangidan nasa kana ya mik’e ya fice...
Barde na ficewa Turaki da har lokacin bai daina sakin murmushi a hankali ba yace “Rankaidad’e ango yanzu haka za’ai hidimar nan bazaai shelan auren mai Martaba cikin Fada ba..! Ko Haka zaka tare ne bazaka bari ahalin Fada su shaida ba..!” Ya k’arashe cikin sigan zolaya yana sosa kai...
Wani irin duba kurum Mahmood d’in ya aika masa, Turaki yai murmushi da tafi kama da yak’e yace “Tuba nake Allah shi taimakeka...!!”
Girgiza kai kurum Mahmood d’in yayi yace “Kanada gaggawa Turaki... Sau nawa zan ce maka Ina buk’atarta cikin Masarautar nan shiyasa na aurota kafin su aurarta ga wani... Idan amfaninta ya k’are a cikin Masarautar nan zan sawwak’e mata taje ta auri wanda take so.. Babu wani abu da zai shiga taakanina da ita.. Hakan yasa na killaceta b’angare guda..! Ka fahimta..?!”
Turaki ya jinjina kai yana mai k’ok’arin matse dariyarsa dan ko babu komai gaban Sarki yake... Shidai yanzu hankalinsa ya kwanta tinda bai aurarta ga wani cikin Masarautar ba ya aurawa kansa, yasan daga baya zai yarda da batunsa cewa sonta yake... Sallama Turaki yai masa dan shi kam ba baisan auren Raheema da Yazeed Mahmood ya umarta a d’aura ba... Hakan yasa baibi takan ahalin masaeautar ba yai tafiyarsa gida dan huta gajjiya daga baya yazo yayiwa Jamal murnan aure...
**
Yazeed dake zaune spot d’insu shida abokansa su Zayyad suna kuma kid’asa dan ya sanar dasu daga yau ya zama Sarki, sabida ana d’aura auren Mahmood zai d’auki matarsa su koma Spain... Abokan sai kuma haukatasa suke suna duk’awa gabansa suna fad’in Allah shi taimakeka Rankaidad’e Mai Martaba Sarki Mai talakawa...!
Zayyad ne ya koma gefe yana amsa waya da alama labarin ta iso masa da d’umi d’uminta... Dama a ido ne suke nuawa Yazeed suna sonsa cikin zuciyarsu kuwa har kullum downfall d’insa suke son gani shiyasa duk abotan da ba’a gina cikin tsoron Allah ba ka guji irin wannan abota da wad’annan miyagun abokai wanda zasu kaika su baroka...
Babu shiri Zayyad ya k’araso yana labarta masu labarin da yaji...
Tamkar sauk’an aradu haka Yazeed yaji abun, ya mik’e ya cakumo Zayyad yana fad’in “K’arya kake... K’arya kake Zayyad Mahmood ne ya auri Raheema kuma d’aukanta zai su tafi Spain ni ne nan zan zama Sarki..!!”
Zayyad ya finciki wuyarsa daga hannun Yazeed yana furta “Ka zaci zan maka k’arya ne haka kawai, ai taimakonku yayi daga kai har Raheemar ya aura maku juna yanzu sai kuyi wanda babu zunubi sai Lada Your Highness ko ya kukace guys..?!” Ya k’arashe yana duban sauran abokan...
Gaba d’aya suka tuntsure da dariya suna jinjina k’arfin hali irin na Mahmood, kuma abinda Mahmood d’in yayi sosai ya burgesu... Sai dariya sukewa Yazeed suna fad’in karfa ya zama loser da gaske... Mahmood ya d’arasa a ko ina... Da alama sarautar nan bazai tab’a gadanta ba...
Jiki a sanyaye Salame ta k’arasa ta tallafi b’angare guda na Muhibbah Gudidi na rik’eda b’angare guda suka fito da ita suna janyota kanta rufe da mayafi....A haka suka fakaice idanun mutane da hankalinsu ya tafi ga masu busa dan tuni an soma dawowa daga wajen d’aurin aure ga labaru daban daban na tashi na irin d’aurin auren da akai.... Sai sannan ne Mommy take jin Wai ma wasu fataken Buzaye Yawale ya bada auren Muhibbah... Hankali tashe Mommy Ke kuma tambayar mutanen dake wajen yanda al’amarin auren ya kasance...
Tuni su Gudidi Sun fita Ta can bayan layin suna jan Muhibbah da k’yar da k’yar har dai suka hango Yawale tsaye jikin wata mota.... Yawale ya d’ago masu hannu yace su k’araso...
Tuni suka k’arasa yanda motar take... Take Barde ya fito ya bud’e masu d’aya b’angaren da babu kowa suka ajeta ciki gefeda Mahmood... Itadai Salame tsoron mutanen ne ma ya rufeta, jikinta har rawa yake tana alla alla su bar wajen... Suna ajeta Barde ya maida k’ofar mota ya rufe yai sallama da Yawale....
Suka koma gefe suna kallo aka tafi da Muhibbah Yawale na Washe baki yana fad’in “An yarda k’wallan mangoro an huta da k’uda...!” Harda d’aga hannu yana waving motar...
Guididi ma Ta tintsire da dariya tana tayasa da fad’in “A k’are can a duniyar matsafa dan wannan daga gani ‘yan shan jini ne suka sayi yarinyar nan...!”
Yawale yai shiru kaman mai nazari sai ya jinjina kai yana mai tabbatarda maganan Gudidi da tace ‘yan shan jini ne suka sayi Muhibbah dan ya tuna mak’udan zinarin da suka bada matsayin sadakinta, sai yanzu yake ciza yatsa dama ya saida masu ita da tsada da yanzu yayi dukiya, amma dukda haka ya samu ai, sannan ga Hameedarsa zata auri Ansar d’an Hajiya Murjah...
Mommy a fujajan ta nufi d’aki yanda aka kulle Muhibbah saidai babu Muhibbah babu dalilinta... Take taji wasu irin hawaye na zuwa mata, Ta shiga bud’e k’ofofi tana ambato sunan Muhibbah mutane na kallon ikon Allah...
Shigowarsu Salame da Gudidi yasa Mommy ta nufesu tana tambayarsu ko sunga Muhibbah... Salame na k’ok’arin danne kukanta take girgiza kai, lokaci guda take furta “Murjah Muhibbah ta tafi... Ta tafi kuma bazaki sake ganinta ba..!” Ta k’arashe hawaye na gangaro mata...
Tamkar mutum mutumi haka Mommy ke dubansu hawaye basu daina ambaliya a fuskarta ba... Cikin wane irin zabura tasa kai Ta nufi waje tana fad’in “Ina suke... Na fasa na fasa aura masu Muhibbah... Ku dawo min da d’iyata wllhi na fasa..!!”
Gudidi tai ta maza ta kamo Mommy ta dawo da ita cikin gida... Gidan biki dai ya kacame da maganganu da hargitsi... Wannan kenan..!
**
Tunda suka d’au hanya ya kasa janye idanunsa daga kanta, tsananin tausayinta yakeji na taso masa daga can k’asar zuciyarsa.... Idan da ace bai aureta ba tabbas wad’annan mugayen mutane da Sun bayar da ita ma ko wane irin mutum, tabbas zasu iya salwantar da rayuwarta sabida son zuciya... A hankali harshensa ya furta “You’re safe now..!” Dai dai lokacin da aka d’ale speed bump abinka da mai bacci sai ta fad’o cikin jikinsa tai matashi da k’irjinsa... Dukda bacci take yana Iya jin bugun zuciyarta cikin nasa k’irjin, tamkar zukatan nasu lokaci guda suke bugawa... Yanayin da ya jima bai tsinci kansa ciki ba ya ziyarcesa.... A hankali yake k’ok’arin kai hannu jikinta yana son gyara mata kwanciyar zuciyarsa naci gaba da harbawa... Wai fah ita d’in matarsa ce yanzu, ji yake kaman idan ya tab’ata zata farka.... Ya maida hannunsa ya ajesu ba tareda ya gyara mata kwanciyar ba, tana nan kwance cikin k’irjinsa.... Burki da Turaki ya d’an ja ne ya sanyata zamowa daga kan k’irjinsa zuwa cinyarsa.... Yai mata K’uri yana dubanta, wane irin duba yake mata wanda ko iya janye idanunsa baiyi, a hankali ya kai hannunsa yana k’ok’arin yaye rufin dake fuskarta.... Sannu a hankali yake janye mayafin hardai fuskarta ya bayyana... Zuciyarsa ta kuma bugawa lokaci guda, fuskar nata fayu babu ko kwalliya tamkar ba Amarya ba, hasalima a kod’e fuskar tata take irin na wanda yaci kuka harda sauran busassun hawaye a fuskar nata... Dogayen bak’ak’en gashin idanunta da sukayi marfi wa manyan idanun nata duk sun shige cikin juna alamu kuka taci sosai, idanunsa suka sauk’o kan labb’anta masu d’an duhu kad’an wanda kaman an zane k’arshensu da liner... A hankali ya lumshe idanunsa yana mai k’ok’arin janye fuskarsa daga barin dubanta, nan idanunsa suka sauk’a kan hannunta da yasha zanen flowers na lalle dunk’ule da wata ‘yar takarda... Yai K’uri yana duban hannun nata... Duk wannan bacci da take takardan na nan mak’ale cikin hannunta bai fad’i ba... Daga gani ba rik’on wasa taiwa takardan ba...
Mahmood yakai hannunsa yana k’ok’arin bud’e hannun nata dake dunk’ule da takardar...
A hankali ya warware hannun nata har ya ciro takardan... Gabansa ya buga kikaci guda sanda ya warware takardan... Zanen ginin gidan sarautar nan ya gani... Take mafarkin da yayi da ita tana guduwa da zanen ya shiga dawo masa... Ikon Allah..! Wato dai mafarkinsa ta tabbata gaskiya... Yarinyar nan tanada wani agenda d’inta cikin gidan...! Toh ya akai irin zanen da Wambai ya basa ya fad’o hannunta... Mai takeyi da zanen..? Kuma a ina Ta samu..?! Tambayoyin da suka tsaya masa a rai har suka isa masarauta...
Lokacinda suka hankulan d’aukacin jama’an Masarautar naga hidindimun bikukuna da ake sannan wata labari da d’umi d’umi ta iso Masarautar cewa auren Raheemah dai ba da Mahmood aka d’aura ba da K’aninsa Yazeed aka d’aura...
Wannan hargitsi yasa har Mahmood ya ciccib’i amaryarsa ya shige da ita sashen da ya tanada na musamman Don ajeta ciki...
Yana fitowa ya tadda Barde da Turaki har sun sauya shiga suma, take ya kuma jaddada masu cewa babu wanda zaisan batun aurensa da Muhibbah..!
Barde ya jinjina kai cikeda risinawa yana mai tabbatar masa amincinsa garesa...!
Mahmood ya jinjina kai yace “Ina Kuyangin dana ce ka ware mun su...?!”
Barde ya kuma risinawa yace “Allah shi baka yawan rai suna nan waje suna jiran umarninka...!”
Nan ma jinjina kai yayi yace “Kasan sashen da na ajeta ai..?!”
Barde ya jinjina kai yace “K’warai Rankaidad’e...!”
Mahmood ya kuma daidaita tsayuwarsa yace “Akai Kuyangin wajen, aikinsu kenan su dinga kula da ita, kama daga abinda zataci zuwa komai na buk’atarta... Koda wasa kada a bari ta lek’o koda k’ofa ne har sai idan ni ne na umarta..!”
Barde ya kuma risinawa yace “An gama Allah shi taimakeka...! Jaaa zamaninka dogon Sarki mai dogon zamani..!” Ya gama kirariwa Ubangidan nasa kana ya mik’e ya fice...
Barde na ficewa Turaki da har lokacin bai daina sakin murmushi a hankali ba yace “Rankaidad’e ango yanzu haka za’ai hidimar nan bazaai shelan auren mai Martaba cikin Fada ba..! Ko Haka zaka tare ne bazaka bari ahalin Fada su shaida ba..!” Ya k’arashe cikin sigan zolaya yana sosa kai...
Wani irin duba kurum Mahmood d’in ya aika masa, Turaki yai murmushi da tafi kama da yak’e yace “Tuba nake Allah shi taimakeka...!!”
Girgiza kai kurum Mahmood d’in yayi yace “Kanada gaggawa Turaki... Sau nawa zan ce maka Ina buk’atarta cikin Masarautar nan shiyasa na aurota kafin su aurarta ga wani... Idan amfaninta ya k’are a cikin Masarautar nan zan sawwak’e mata taje ta auri wanda take so.. Babu wani abu da zai shiga taakanina da ita.. Hakan yasa na killaceta b’angare guda..! Ka fahimta..?!”
Turaki ya jinjina kai yana mai k’ok’arin matse dariyarsa dan ko babu komai gaban Sarki yake... Shidai yanzu hankalinsa ya kwanta tinda bai aurarta ga wani cikin Masarautar ba ya aurawa kansa, yasan daga baya zai yarda da batunsa cewa sonta yake... Sallama Turaki yai masa dan shi kam ba baisan auren Raheema da Yazeed Mahmood ya umarta a d’aura ba... Hakan yasa baibi takan ahalin masaeautar ba yai tafiyarsa gida dan huta gajjiya daga baya yazo yayiwa Jamal murnan aure...
**
Yazeed dake zaune spot d’insu shida abokansa su Zayyad suna kuma kid’asa dan ya sanar dasu daga yau ya zama Sarki, sabida ana d’aura auren Mahmood zai d’auki matarsa su koma Spain... Abokan sai kuma haukatasa suke suna duk’awa gabansa suna fad’in Allah shi taimakeka Rankaidad’e Mai Martaba Sarki Mai talakawa...!
Zayyad ne ya koma gefe yana amsa waya da alama labarin ta iso masa da d’umi d’uminta... Dama a ido ne suke nuawa Yazeed suna sonsa cikin zuciyarsu kuwa har kullum downfall d’insa suke son gani shiyasa duk abotan da ba’a gina cikin tsoron Allah ba ka guji irin wannan abota da wad’annan miyagun abokai wanda zasu kaika su baroka...
Babu shiri Zayyad ya k’araso yana labarta masu labarin da yaji...
Tamkar sauk’an aradu haka Yazeed yaji abun, ya mik’e ya cakumo Zayyad yana fad’in “K’arya kake... K’arya kake Zayyad Mahmood ne ya auri Raheema kuma d’aukanta zai su tafi Spain ni ne nan zan zama Sarki..!!”
Zayyad ya finciki wuyarsa daga hannun Yazeed yana furta “Ka zaci zan maka k’arya ne haka kawai, ai taimakonku yayi daga kai har Raheemar ya aura maku juna yanzu sai kuyi wanda babu zunubi sai Lada Your Highness ko ya kukace guys..?!” Ya k’arashe yana duban sauran abokan...
Gaba d’aya suka tuntsure da dariya suna jinjina k’arfin hali irin na Mahmood, kuma abinda Mahmood d’in yayi sosai ya burgesu... Sai dariya sukewa Yazeed suna fad’in karfa ya zama loser da gaske... Mahmood ya d’arasa a ko ina... Da alama sarautar nan bazai tab’a gadanta ba...