← Book details Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 90 OF 162

Sashe 90

Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jamal ya tsareta da idanu yana mai ci gaba da karantarta, lokaci guda ya gyara tsayuwarsa jikin crutches d’insa kana yace “Jakadiya a matsayinki na Sarauniya saman karagarki wani hukunci zaki yanke wa bawan da yaci amanarki...?!”

Jakadiya Ta jinjina kai tace “Hukunci mai tsauri, hukuncin da nan gaba bazai sake tunanin cin amanan bawa d’an uwansa ba balle Ubangidansa...!!”

Jamal ya murmusa yace “Da kyau Jakadiya... Naji dad’in wannan shawari naki...!”
Ya isa jikin ‘yar k’aramar jakan ya bud’e... Equipments d’in da ake operation ma dabba sune a jejjere cikin jakan....

Jakadiya ta ware idanu tana kallan k’araffan dake shirye cikin wannan ‘yar jaka.... Wata k’usa ya d’auko mai kamada noti ya k’araso kusan Jakadiya yana mai sakin murmushi yake furta “Nasan zaki tuna a zamanin da can baya kakanninku an masu huji a labb’an bakunansu yanda ake gark’ame bakunan nasu da kwad’o koh...?!”

Jikin Jakadiya ya d’auki rawa, Ta shiga rawar d’ari tana mai furta “Rankaidad’e Yarima amin rai... Tuba nake...! Wllhi bani k’aunar zama Sarauniya... K’arya nake Rankaidad’e... Kaji k’aina kada ka azabtar dani... Wayyo ni Talle k’arshena yazo....!!” Ta k’arashe cikin murya irinta mai kuka...

Tsawa ya daka mata yace tai masa shiru...! Jakadiya ta had’iyi kukanta tana mai rintse idanunta had’ida jinjina kai alamun tayi shiru....

**

A wane irin hautsine ya shigo ya tadda Ubangidan nasa... Mahmood ya mik’e daga kishingid’en da yake yana mamakin yanda Barde ya fad’o kansa haka...

Har k’asa ya risina yana fidda haki yake fad’in “Tuba nake Allah shi baka yawan rai... A gafarceni...!!”

Mahmood yace “Lafiya ka shigo haka nan...?!”

“A gafarceni Rankaidad’e kira na samu daga matuk’i....!!”

Sosai wannan karon ya kuma gyara zamansa yanda Barde yaci gaba da fad’in “Matuk’i ya nemi Gimbiya Zahrau ya rasata...!!”

Baikai aya ba sak’o ya shigo cikin wayar Salulan Mahmood d’in wanda ba kowa Keda layin ba sai amintattun mutane...

Bai kuma tsayawa sauraren Barde ba sai duba Sak’on da yake
_We’ve your daughter your Highness, and if you want to see her alive you need to do exactly as we say.._

Cikin sauri ya shiga k’ok’arin dialing layin amma bata shiga... Wani sak’on ya kuma shigo masa
_Don’t try anything foolish your Highness... Don’t involve cops, Kai even watchmen na cikin Fada do not involve them.... Kai d’aya mukeso kazo.._
Take aka rubuto masa address d’in location d’in da ake so yajesa....

Barde na gani Ubangidan nasa ya mik’e ya fice ba tareda yacedashi komai ba...

Mota ya shige yana k’ok’arin dialing layin Zahra amma bai shiga... Cikin tsananin k’unan zuciya yake tuk’a motar yana falfala gudu saman kwalta...
Bai zarce ko ina ba sai k’ofan gidan Turaki...

Turaki na ganin wayar aminin nasa ya saki murmushi a hankali dan yasan dole Mahmood d’in ya nemesa, d’aya bazai Iya babu d’aya ba haka abotansu yake... Kaman bazai d’aga ba sai kuma ya d’aga shima babu wani walwala taredashi ya gaida Rankaidad’e...

Daga d’aya b’angaren Mahmood yace “Ka fito Ina jiranka waje..!”
Daga haka bai kuma cewa komai ba saima katse kiran da yai...

Turaki ya tsaya juya wayar cikeda mamaki, yana nanata abinda Mahmood d’in ya fad’i masa... Bai ida tinanin ba ya soma jiyo sautin horn alamun dai da gaske yana k’ofar gidansa...
Girgiza kai kurum Turaki yai ya mik’e ya nufo waje...

Yana K’arasowa Mahmood da tuni ya hangosa Ta mirror ya zuge glass d’in “Get in the car..!”

Turaki yai masa k’uri cikeda mamaki lokaci guda ya girgiza kai, lokaci guda kuma ya d’an saki murmushi yace “Rankaidad’e nasan gaba d’aya fad’in garin nan talakawan ka ne amma bazakazo har k’ofan gidana ka nuna min iko ba..!”

Mahmood ya kaikaito yanai masa wane irin duba lokaci guda ya bud’e security lock yana mai furta “We don’t have much time... Please get in..!”

Yanayin da yai maganan yasa jikin Turaki d’anyin sanyi, sai kuma ya gyara tsayuwarsa yace “I’m sorry your Highness but I’m not going anywhere har sai kamin bayanin ina zamuje...!”

Izuwa lokacin Mahmood ya soma k’osawa da taurin kan Turaki.... Bai amsasa ba sai mik’a masa wayar da yayi daidai kan sak’on da aka turo masa...

Turaki ya karance, lokaci guda ya d’ago yana duban Mahmood d’in a d’an firgice... Babu shiri ya finciki marfin motar ya shige, cikin ‘yar daburcewa yake furta “Your Highness bazamu biye tasu ba... We need to inform the authority right away..!”

Katsesa Mahmood yai da fad’in “No Turaki hukuma bazata sani ba... can’t you see my daughter’s life is at stake here...! What if they did something to her... No bazamu kira kowa ba... We do exactly as they say..!!”

Turaki ya jinjina kai a hankali yace “Toh mai suke buk’ata... Did they ask for Ransom..?!”

Girgiza masa kai yai alamun a’a sai kuma yace “Ina zaton ba kud’i suke buk’ata ba nid’in suke buk’ata... Kuma duk bazai wuce akan wannan banzan sarautar ba... Mai yuwa rayuwata suke nema domin su cimma burinsu na d’akewa Karagar nan... Turaki son duniya da Mulki ba abinda ba zaisa mutane suyi ba...!”

Turaki ya jinjina kai yace “Tabbas it might be a trap... Rayuwarka suke buk’ata ba kud’in Fansa ba... Rankaidad’e shisa nace muyi abin in the right way... Let’s call the cops right away...!”

Saurin dakatar dashi Mahmood yai da fad’in “Have you ever lost your loved one...? Turaki rayuwar d’iyata muke magana a nan... No one must know about this... I’ll submit myself to them idan hakan zaisa su sakar min d’iyata..!!” Ya k’arashe yana mai sakin huci...

Turaki ya jinjina kai cikeda tausayin abokin nasa yace “I’m sorry your Highness, I understand where you’re coming from... Amma abinda nakeso yanzu muyi before mu confronting kidnappers d’in let’s check the hospital first... Maybe sunga wani abu... Ko ma su nuna mana CCTV footage d’insu watak’ila mu samu wani clue gameda kidnappers d’in kuma shima driver d’in da ya kaita dole Mu bincikesa tinda kace tareda Jakadiya ka had’asu suka fita..!”

Mahmood ya jinjina kai ba tareda yace komai ba... Ganin irin driving d’in da yake yasa Turaki karb’an motar yaci gaba da tuk’asu...

Koda sukaje asibiti suka tadda driver d’in duk a rikice nan yake sanar dasu Zahra ita kad’ai ta fito ba tareda rakiyar Jakadiya ba, sannan masu kula da majinyata na cikin asibitin sun tabbatar masu Zahra ta shiga wajen Fu’ad tareda wata mace... Saidai babu wanda yasan macen da Zahra Ta shigo da ita amma kam tabbas ba Jakadiya bace... Koda suka shiga wajen Fu’ad suka tambayesa ko zai iya tuna matar da Zahra Ta shigo tareda ita Fu’ad d’in bai iya cewa komai ba sabida halinda yake ciki dukda cewa gashi kaman so yake ya masu magana... Mahmood ya matso jikin gadon Fu’ad ya d’an rank’wafo kad’an yana kuma tambayarsa cikin tsanaki “Fu’ad try to remember something... Who’s that woman..? Please Fu’ad your niece’s life is in danger... Please try to remember something..!!”

Kallonsa kurum Fu’ad yake hawaye na gangaro masa yana son yin magana babu hali.. Lokaci guda ya shiga buge buge yana tak’urewa waje guda... Babu shiri nurses d’in suka k’araso suna rok’on Mahmood ya fice sabida jikin Fu’ad d’in da ya kuma rikicewa...

Turaki yai k’ok’arin janyo Mahmood d’in suka fice waje, shi kansa Turaki tsananin tausayin ahalin Mahmood ke d’awainiya dashi....

Suna fitowa daga wajen Fu’ad Mahmood ya buk’aci a nuna masu CCTV footage na asibtin saidai akai rashin sa’a Cameras d’insu gaba d’aya basa aiki...

Huci kurum yake sakarwa yana fad’ida Turaki “You see... K’asarmun kenan, komai babu maintenance babu management mai kyau... Ba dole ta’addanci yayi yawa ba..!!”

Turaki ya jinjina kai yace “Hakane Rankaidad’e saidai muyi addu’an Allah ya kawo mana sauk’i... Shisa muke so mu samu shuwagabanni ire irenku wanda zasu kawo mana sauyi... Ka bar batun komawa Spain d’in nan ka karb’i ragamar mulkin Masarautarmu..!”

Bai tsaya sauraren Turaki ba ya nufi mota.. Tuni Turakin ya take masa baya, daidai sanda sak’o ya kuma shigowa Mahmood cewa idan yana son sake ganin d’iyarsa da rai yazo address d’in da aka turo masa nan da mintoci da basu gaza arb’ain ba idan kuma ba haka ba ya shirya d’aukan gawar d’iyarsa... Time ya soma reading tik tok..!!

Jifa da wayar yai ya finciki d’an makullin hannun Turaki ya shige Mota ba tareda ya kuma bi takan Turakin ba... Turaki na k’ok’arin tsaidashi inaa tuni ya kwali motar ya fice daga cikin asibitin... Haka Turaki yai tsaye yana duban motar har ya fice... Yana ficewa Turaki yai saurin ficewa daga asibitin ya tari motar haya dukda baida tabbacin location d’in da Mahmood ya nufa....

SameenaAleeyou 📚*MUHIBBAH*

*57*

*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*

Mamaki ne ya cikasa ganin motar Yazeed pake farfajiyan gidan da aka tura masa adireshin... Toh meke faruwa..? Badai tsanar da Yazeed yai masa har ya kawo wannan munzanin ya nemi cutar da d’iyarsa ba... Kai Yazeed bazai haka ba, dikda cewa yasan baida hali akasarin lokuta amma zai wuya ace zai aikata abu makamancin wannan... Jiki babu laka Mahmood yaci gaba da takowa yana k’arema gidan kallo har ya iso jikin k’ofar da zai sadaka da asalin cikin gidan... Shewan mutane mace da namiji da ya soma saurare ne ya sanyasa d’an dakatawa kad’an daga jikin k’atoton window na parlorn...

“Gaskiya zanyi kewarki... Wai haka kika k’ara sugar, tab lallai da bakizo ba dana tapka babban asara dan wannan garan tsaf Mahmood ne zai kwashe... Amma ko yanzu saidai ya sami saurana..!” Ya k’arashe shu’umin murmushin nan nasa saman fuskarsa...
Chapter 90 · 0% Book details