Sashe 6
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi kad’an Zahra tai a tak’aice tana mai jinjina masa kai ba tareda ta amsa ba.... Idanunta suka sauk’a kan Muhibbah dake binta da kallo irinta k’urilla...
D’an rausayar da idanu Zahra tai had’ida furtawa a hankali “¿Por qué ella me está mirando?” (Mai yasa take min kallon k’urilla) Gashi dik ita a tak’ure take da wad’ann kayan sarautar... Ita harga Allah ta gaji da k’asar da mutanenda ke cikinta, tana gani Ansar na introducing Muhibbah wa Umaima, had’ida dank’a mata amanar ‘yaruwarsa...
Umaima tace “Bakada matsala Dr, in sha Allah ‘yaruwarka tana hannu mai kyau... Nai maka alk’awari....”
Ansar ya jinjina kai a hankali kana ya mik’e daga zaune yana mai furta “Toh ni zan koma kar nai dare.....”
Umaima tace “Da wuri haka kaman ana korarka....”
Murmushi yai a fili a cikin zuciyarsa kaw tsantsan fargaban kewar Muhibbah ne da zaiyi Ke azalzalansa.... Suka dubi juna idanunsu suka had’e waje guda.....
Umaima ta dubi Muhibbah wacce itama Ansar d’in take duba cikeda kulawa kana tace “Hibbah bari mu barku kuyi sallama da yayan naki....Ki saki jikinki tamkar a gida kike.... Ki d’aukeni tamkar k’awa ko nace ‘yar uwa a gareki...”
Muhibbah ta jinjina mata kai fuska fal murmushi take furta “Godiya nake Rankishi dad’e....!”
Umaima ta kuma murmusawa kana tace “You don’t need to be too formal, kar Ki biye na wannan Yayan naki... Just call me Umaima....”
Jinjina kai Muhibbah ta kuma yi kana tace “Na gode Umaima...!”
Umaima ta kuma sakin murmushi kana ta janyo hannun Zahra suka d’an basu waje danyin sallama....
***
Ita kad’ai cikin katafaren d’akin nata, sai faman safa da marwa take, Takai mari takai bango.... Tana jiran bak’in labarin da yau d’in zai risketa dan dik randa mahaukaciyar nan ta bayyana toh ko shakka babu sai tayi gamo da labari mafi muni... Sai wani babban al’amari ya faru cikin Masarautar.... Tana a cikin wannan yanayi Jakadiya Ta turo k’ofa ta shigo cikeda risinawa ta zube k’asa.....
Gimbiya Turai, ko muce Giwa, ko muce Maibabban d’aki dan dika wad’annan sunayenta ne a cikin Masarautar.... Ta juyo tana watsawa Jakadiya wani irin duba, lokaci guda take takowa yanda Jakadiya ke zubewa tana kuma kwasan gaisuwa....
“Jakadiya Wani bak’in labari kikazo min dashi.....?” Giwa ta tambaya cikin kakkausar murya
Jakadiya ta kuma risinawa tana mai furta “Allah shi huci zuciyar Giwar Sarki.... Na bincika gabas da yamma kudu da arewa babu bak’in labari da ya bayyana a cikin Masarautar nan.... Da alama wannan karon bata fito da wani mummunan labari ba... Allah shi baki yawan rai amma saidai....” Tai burkiwa kalamanta sabida k’irjinta dake tsananin bugu....
Cikeda son jin mai Jakadiya keson fad’i Gimbiya Turai tace “Amma mai... Mai kuma ya faru Jakadiya...?”
Jakadiya ta had’iyi miyau kana tace “Allah shi baki yawan Rai, Ubandoma ya sanar dani Yarima Mahmood ya soma tambayar ko wacece wannan mahaukaciyar... Kuma daga yanda Ubandoma ya sanar dani Yarima bazai gajiya ba har sai ya gano ko wacece ita...”
Dakatar da ita Giwa tai da fad’in “Jakadiya akwai k’ofofin da D’ah na bai isa bud’esu ba a cikin Masarautar nan... Wannan kad’ai yayi kad’an ace Mahaukaciyar nan ta bayyana a Fada... Karki mance dik randa ta bayyana wani babban al’amari ne Ke faruwa wanda za’a iya dangantashi da rasa rai.... Tabbas akwai wani abinda ya faru a cikin Masarautar nan wanda bamuda masaniya...!!” Ta k’arashe tana duban Jakadiya wacce itama ita take duba cikeda damuwa mai gauraye da tsoro....
Tabbas zama bata gansu ba...
***
Yana fitowa bai zarce ko Ina ba sai bargan dawakin mahaifinsa.... A hankali yake takawa abubuwa da dama suna zuwa masa daki daki.... Wacece wannan matar...? Maiyasa yakeji kaman ya santa....? Dik yanda ya shige bayi sai sun risina Sun kwashi gaisuwa, Shiko Yarima Mahmood saidai ya jinjina masu kai alamun amsawa... Daga cen ya hango k’aramin k’aninsu Fu’ad yana k’arasowa....
Yarima Mahmood ya d’an fad’ad’a murmushinsa sanda Fu’ad ya k’araso gareshi, jerawa sukai su duka biyun suna ci gaba da takawa cikin bargan dawakin irin yanda masu mulki keyi....
“Barka da yammaci Yaya...” Fu’ad yace yana mai d’an sadda kai...
“Baka Yarima Fu’ad...!” Yarima Mahmood ya amsa cikeda kulawa....
Hira suka somayi irinta ‘yan uwa wanda suka jima basu tareda juna....
Daidai jikin wata farar doki Mahmood ya tsaya yana mai k’are mata kallo tamkar mai tunanin wani abu, hannu yasa yana shafa fuskar dokin a hankali... Fu’ad ya d’anyi gyaran murya had’ida furta “Dik ranan sallah ita yake hawa yaje masallacin idi bisa....Ana mata ado da kwalliya irinta amaren dawakai.... Yana tsananin k’aunar dokin nan....” Ya k’arashe murmushi saman fuskarsa yana mai shafa gadon bayan dokin...
Mahmood ya tari zancen da fad’in “Jafar ne kad’ai yake mata kwalliya irin wanda Maimartaba Ke so... Bai hawanta idan ba Jafar bane ya shiryata...!”
Shiru na d’an lokaci tamkar wanda ya tina wani abu kana yace “JA’AFAR....! Ina Ja’afar Fu’ad...? Tinda na dawo Masarautar nan ban sakashi a idanuna ba....?”
Fu’ad bai iya basa amsa ba saima sadda idanunsa k’asa da yai cikin wane irin sanyin jiki.... Kaman daga sama ya soma jiyo muryar Yazeed yana fad’in “Ta yaya kake tambayar mutumin da shi kansa bai jima da dawowa Masarautar nan ba... Idan zaka tambayi wani abu gameda Masarautar nan toh kada ka tambayi wannan k’anin naka...!” Ya k’arashe yana mai aikawa Fu’ad da kansa Ke k’asa muguwar kallo irinta k’ask’anci....
Yarima Mahmood ya kaikaito sosai yana duban Yazeed kana ya kuma duban Fu’ad....
Cruel smile d’in nan nasa saman fuskarsa yake d’aga gira alamun jaddadawa....
Dafa kafad’an Fu’ad Mahmood ya d’anyi kana yace “Fu’ad tell me, meke faruwa... Mai Yazeed yake nufi da yace baka jima da dawowa Masarautar nan ba... Ina ka tafi... Ko akwai course d’in da baka gama bane a Cyprus...?”
Fu’ad bai iya amsashi ba sai kuma sadda fuskansa k’asa da yayi...
Yazeed dake ci gaba da shu’umin murmushin nan nasa yai karaf ya soma fad’in “Tell him Fu’ad... Tell your big brother how you wasted time and resources a k’asar Cyprus ba tareda ka dawo da koda kwalin tsire ba... Koda shike ka dawo da ciwon shaye shaye na kayan maye... Hodar iblis Ta kusan illata maka kwanya gaba d’aya....!”
Baikai aya ba Mahmood ya katsesa da fad’in “Enough Yazeed..!! Wasu irin kalamai kake jifan d’an uwanka dasu haka...”
Murmushi da gefen baki Yazeed Ke ci gaba da yi kana yace “Gashi nan... Ask him... Ka tambayeshi idan k’arya na mishi.... Shekarunsa 28 amma baisan ina rayuwarsa Ta dosa ba... Ka tambayeshi kalan abin kunya da ya janyowa wannan masarauta... Ka tambayeshi gashi nan... Akanshi k’iris ya rage mulki Masarautar nan bata kufce daga gidan nan ba... Fu’ad you’re nothing but a great disappointment...”
Fu’ad da tuni idanunsa sun kad’a sunyi jazir yana fidda wane irin huci na tsananin k’unan zuciya... Lokaci guda ya d’ago rinannun idanunsa masu zuban ruwa yana duban Yazeed yake furta “Yes..! Yes Yazeed... Ban dawo da ko wanne takarda ba sai na shan kayan maye kaman yanda ka fad’i.... Amma kar ka mance kaine sila... Kaine sanadi... Kaine Kai jagoranci wajen ruguza rayuwar innocent boy.....”
Ganin Fu’ad ya soma sakin layi ya sanya Yazeed yowa kansa yana mai furta “Shut up... Shut the hell up...!! Don’t you dare put the blame on me...!!”
Ganin bayi sun soma dubansu suna yaface had’ida nunasu wa junansu da baki ya sanya Mahmood daka masu tsawa da fad’in “Enough!! Ya isheku haka... Kusan a yanda kuke kun kuma San mai kuke fad’iwa junanku....?”
Gaba d’aya sukai shiru suna maida huci tamkar wasu zakuna....
Yarima Mahmood ya dubi Fu’ad yace “Lets go Fu’ad.....!!!” Yai maganar cikin tsananin dakewa.....Babu musu Fu’ad ya take masa baya suna masu b’allawa juna harara shida Yazeed....
Suna shigewa Yazeed ya dakawa kuyangin dake zube a wajen muguwar tsawa da fad’in “Ku kuma mai kukeyi a nan... Ku b’ace min da gani kafin duk rasa rayukanku....!”
Tuni suka mik’e suna k’ok’arin barin wajen cikin sauri har kaman zasu kifa...
Hauni amintaccen bawan Yazeed yai kansu da k’atotuwar dorina yana zabga masu had’ida kwashe masu albarka....
Yazeed sai faman cika yake yana huruwa shi kad’ansa... Lokaci guda ya kuma sakin wata murmushi da shi kad’ai yasan ma’anarta.... Ya wani d’an gyara zaman rigar sarautarsa dake sanye jikinsa cikeda Izza wanda yin hakan d’abi’arasa ce
**
Cikin sassarfa suke tafe, Mahmood na gaba yayinda Fu’ad Ke biye dashi, kaida ka gansu kasan babu lafiya, a haka suka nufi sashen mahaifiyar tasu...
A daidai lokacinda Umaima, Zahra da kuma Muhibbah suka doson mashigar parlorn, cak suka tsaya suna duban Mahmood da Fu’ad dake tafe tamkar zasu kifa k’asa....
Tin Daga k’ololuwar kanta taji wani abu har izuwa tafin k’afarta.... Dikda fuskar Fu’ad ya canza sabida girma da yai ba kaman lokacinda Ta sanshi yana k’aramin yaro mai k’anan shekaru ba, kaman yanda nata fuskar ma ya canza hakan bai hana ta gane kamanninsa domin kaw kamaninsa da Mahmood ya kuma bayyana wanda shi Mahmood d’in babu abinda ya canza a kamanninsa da shike sanin matashi tai masa, saiko alamun girma da ya sauk’o masa.....
Take idanunta suka kad’a sukai jazir tana duban Mahmood tana tina shine mutumin da ya d’auketa da hannunsa ya azata saman doki kyakkyawan fuskarsa d’aukeda murmushi a lokacin, fuskar da take gani a idanunta tamkar bak’ar k’umurcin macijiya mai mummunar guba....Lokaci guda Ta rintse idanunta da k’arfin gaske tana jin zuciyarta na wani irin fizga tamkar zai fice daga cikin k’irjinta....
SameenaAleeyou📚
[5/23, 6:41 PM] +234 703 453 9908: *👑✨MUHIBBAH✨👑*
*006*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Suna k’arasowa kaga yanda Kuyangi ke k’amewa suna zubewa k’asa alamun girmamawa..... Zahra ta dubi Umaima fuska fal damuwa take fad’in “Aunty Umaima meke faruwa... Mai ya sami Paa da Uncle Best....?” Girgiza mata kai Umaima tai alamun itama bata sani ba... Lokaci guda Zahra tasa kai da zummar bin bayan iyayen nata ba tareda ta jira amsar Umaima ba... Saidai tuni Muhibbah ta rik’o hannunta alamun dakatarwa....
Zahra ta dubi hannunta da tsananin mamaki ganin wacece ta rik’eta... Ta kuma d’agowa sosai tana duban Muhibbah dake rik’eda hannunta guda alamun dakatar da ita..... Daidai da Umaima duban mamaki take bin Muhibbah dashi had’ida jinjina k’arfin hali irinta Muhibbah wacce zuwanta Masarautar kenan amma har tanada k’arfin halin dakatar da jinin sarauta daga gudanar da wani abu...
D’an rausayar da idanu Zahra tai had’ida furtawa a hankali “¿Por qué ella me está mirando?” (Mai yasa take min kallon k’urilla) Gashi dik ita a tak’ure take da wad’ann kayan sarautar... Ita harga Allah ta gaji da k’asar da mutanenda ke cikinta, tana gani Ansar na introducing Muhibbah wa Umaima, had’ida dank’a mata amanar ‘yaruwarsa...
Umaima tace “Bakada matsala Dr, in sha Allah ‘yaruwarka tana hannu mai kyau... Nai maka alk’awari....”
Ansar ya jinjina kai a hankali kana ya mik’e daga zaune yana mai furta “Toh ni zan koma kar nai dare.....”
Umaima tace “Da wuri haka kaman ana korarka....”
Murmushi yai a fili a cikin zuciyarsa kaw tsantsan fargaban kewar Muhibbah ne da zaiyi Ke azalzalansa.... Suka dubi juna idanunsu suka had’e waje guda.....
Umaima ta dubi Muhibbah wacce itama Ansar d’in take duba cikeda kulawa kana tace “Hibbah bari mu barku kuyi sallama da yayan naki....Ki saki jikinki tamkar a gida kike.... Ki d’aukeni tamkar k’awa ko nace ‘yar uwa a gareki...”
Muhibbah ta jinjina mata kai fuska fal murmushi take furta “Godiya nake Rankishi dad’e....!”
Umaima ta kuma murmusawa kana tace “You don’t need to be too formal, kar Ki biye na wannan Yayan naki... Just call me Umaima....”
Jinjina kai Muhibbah ta kuma yi kana tace “Na gode Umaima...!”
Umaima ta kuma sakin murmushi kana ta janyo hannun Zahra suka d’an basu waje danyin sallama....
***
Ita kad’ai cikin katafaren d’akin nata, sai faman safa da marwa take, Takai mari takai bango.... Tana jiran bak’in labarin da yau d’in zai risketa dan dik randa mahaukaciyar nan ta bayyana toh ko shakka babu sai tayi gamo da labari mafi muni... Sai wani babban al’amari ya faru cikin Masarautar.... Tana a cikin wannan yanayi Jakadiya Ta turo k’ofa ta shigo cikeda risinawa ta zube k’asa.....
Gimbiya Turai, ko muce Giwa, ko muce Maibabban d’aki dan dika wad’annan sunayenta ne a cikin Masarautar.... Ta juyo tana watsawa Jakadiya wani irin duba, lokaci guda take takowa yanda Jakadiya ke zubewa tana kuma kwasan gaisuwa....
“Jakadiya Wani bak’in labari kikazo min dashi.....?” Giwa ta tambaya cikin kakkausar murya
Jakadiya ta kuma risinawa tana mai furta “Allah shi huci zuciyar Giwar Sarki.... Na bincika gabas da yamma kudu da arewa babu bak’in labari da ya bayyana a cikin Masarautar nan.... Da alama wannan karon bata fito da wani mummunan labari ba... Allah shi baki yawan rai amma saidai....” Tai burkiwa kalamanta sabida k’irjinta dake tsananin bugu....
Cikeda son jin mai Jakadiya keson fad’i Gimbiya Turai tace “Amma mai... Mai kuma ya faru Jakadiya...?”
Jakadiya ta had’iyi miyau kana tace “Allah shi baki yawan Rai, Ubandoma ya sanar dani Yarima Mahmood ya soma tambayar ko wacece wannan mahaukaciyar... Kuma daga yanda Ubandoma ya sanar dani Yarima bazai gajiya ba har sai ya gano ko wacece ita...”
Dakatar da ita Giwa tai da fad’in “Jakadiya akwai k’ofofin da D’ah na bai isa bud’esu ba a cikin Masarautar nan... Wannan kad’ai yayi kad’an ace Mahaukaciyar nan ta bayyana a Fada... Karki mance dik randa ta bayyana wani babban al’amari ne Ke faruwa wanda za’a iya dangantashi da rasa rai.... Tabbas akwai wani abinda ya faru a cikin Masarautar nan wanda bamuda masaniya...!!” Ta k’arashe tana duban Jakadiya wacce itama ita take duba cikeda damuwa mai gauraye da tsoro....
Tabbas zama bata gansu ba...
***
Yana fitowa bai zarce ko Ina ba sai bargan dawakin mahaifinsa.... A hankali yake takawa abubuwa da dama suna zuwa masa daki daki.... Wacece wannan matar...? Maiyasa yakeji kaman ya santa....? Dik yanda ya shige bayi sai sun risina Sun kwashi gaisuwa, Shiko Yarima Mahmood saidai ya jinjina masu kai alamun amsawa... Daga cen ya hango k’aramin k’aninsu Fu’ad yana k’arasowa....
Yarima Mahmood ya d’an fad’ad’a murmushinsa sanda Fu’ad ya k’araso gareshi, jerawa sukai su duka biyun suna ci gaba da takawa cikin bargan dawakin irin yanda masu mulki keyi....
“Barka da yammaci Yaya...” Fu’ad yace yana mai d’an sadda kai...
“Baka Yarima Fu’ad...!” Yarima Mahmood ya amsa cikeda kulawa....
Hira suka somayi irinta ‘yan uwa wanda suka jima basu tareda juna....
Daidai jikin wata farar doki Mahmood ya tsaya yana mai k’are mata kallo tamkar mai tunanin wani abu, hannu yasa yana shafa fuskar dokin a hankali... Fu’ad ya d’anyi gyaran murya had’ida furta “Dik ranan sallah ita yake hawa yaje masallacin idi bisa....Ana mata ado da kwalliya irinta amaren dawakai.... Yana tsananin k’aunar dokin nan....” Ya k’arashe murmushi saman fuskarsa yana mai shafa gadon bayan dokin...
Mahmood ya tari zancen da fad’in “Jafar ne kad’ai yake mata kwalliya irin wanda Maimartaba Ke so... Bai hawanta idan ba Jafar bane ya shiryata...!”
Shiru na d’an lokaci tamkar wanda ya tina wani abu kana yace “JA’AFAR....! Ina Ja’afar Fu’ad...? Tinda na dawo Masarautar nan ban sakashi a idanuna ba....?”
Fu’ad bai iya basa amsa ba saima sadda idanunsa k’asa da yai cikin wane irin sanyin jiki.... Kaman daga sama ya soma jiyo muryar Yazeed yana fad’in “Ta yaya kake tambayar mutumin da shi kansa bai jima da dawowa Masarautar nan ba... Idan zaka tambayi wani abu gameda Masarautar nan toh kada ka tambayi wannan k’anin naka...!” Ya k’arashe yana mai aikawa Fu’ad da kansa Ke k’asa muguwar kallo irinta k’ask’anci....
Yarima Mahmood ya kaikaito sosai yana duban Yazeed kana ya kuma duban Fu’ad....
Cruel smile d’in nan nasa saman fuskarsa yake d’aga gira alamun jaddadawa....
Dafa kafad’an Fu’ad Mahmood ya d’anyi kana yace “Fu’ad tell me, meke faruwa... Mai Yazeed yake nufi da yace baka jima da dawowa Masarautar nan ba... Ina ka tafi... Ko akwai course d’in da baka gama bane a Cyprus...?”
Fu’ad bai iya amsashi ba sai kuma sadda fuskansa k’asa da yayi...
Yazeed dake ci gaba da shu’umin murmushin nan nasa yai karaf ya soma fad’in “Tell him Fu’ad... Tell your big brother how you wasted time and resources a k’asar Cyprus ba tareda ka dawo da koda kwalin tsire ba... Koda shike ka dawo da ciwon shaye shaye na kayan maye... Hodar iblis Ta kusan illata maka kwanya gaba d’aya....!”
Baikai aya ba Mahmood ya katsesa da fad’in “Enough Yazeed..!! Wasu irin kalamai kake jifan d’an uwanka dasu haka...”
Murmushi da gefen baki Yazeed Ke ci gaba da yi kana yace “Gashi nan... Ask him... Ka tambayeshi idan k’arya na mishi.... Shekarunsa 28 amma baisan ina rayuwarsa Ta dosa ba... Ka tambayeshi kalan abin kunya da ya janyowa wannan masarauta... Ka tambayeshi gashi nan... Akanshi k’iris ya rage mulki Masarautar nan bata kufce daga gidan nan ba... Fu’ad you’re nothing but a great disappointment...”
Fu’ad da tuni idanunsa sun kad’a sunyi jazir yana fidda wane irin huci na tsananin k’unan zuciya... Lokaci guda ya d’ago rinannun idanunsa masu zuban ruwa yana duban Yazeed yake furta “Yes..! Yes Yazeed... Ban dawo da ko wanne takarda ba sai na shan kayan maye kaman yanda ka fad’i.... Amma kar ka mance kaine sila... Kaine sanadi... Kaine Kai jagoranci wajen ruguza rayuwar innocent boy.....”
Ganin Fu’ad ya soma sakin layi ya sanya Yazeed yowa kansa yana mai furta “Shut up... Shut the hell up...!! Don’t you dare put the blame on me...!!”
Ganin bayi sun soma dubansu suna yaface had’ida nunasu wa junansu da baki ya sanya Mahmood daka masu tsawa da fad’in “Enough!! Ya isheku haka... Kusan a yanda kuke kun kuma San mai kuke fad’iwa junanku....?”
Gaba d’aya sukai shiru suna maida huci tamkar wasu zakuna....
Yarima Mahmood ya dubi Fu’ad yace “Lets go Fu’ad.....!!!” Yai maganar cikin tsananin dakewa.....Babu musu Fu’ad ya take masa baya suna masu b’allawa juna harara shida Yazeed....
Suna shigewa Yazeed ya dakawa kuyangin dake zube a wajen muguwar tsawa da fad’in “Ku kuma mai kukeyi a nan... Ku b’ace min da gani kafin duk rasa rayukanku....!”
Tuni suka mik’e suna k’ok’arin barin wajen cikin sauri har kaman zasu kifa...
Hauni amintaccen bawan Yazeed yai kansu da k’atotuwar dorina yana zabga masu had’ida kwashe masu albarka....
Yazeed sai faman cika yake yana huruwa shi kad’ansa... Lokaci guda ya kuma sakin wata murmushi da shi kad’ai yasan ma’anarta.... Ya wani d’an gyara zaman rigar sarautarsa dake sanye jikinsa cikeda Izza wanda yin hakan d’abi’arasa ce
**
Cikin sassarfa suke tafe, Mahmood na gaba yayinda Fu’ad Ke biye dashi, kaida ka gansu kasan babu lafiya, a haka suka nufi sashen mahaifiyar tasu...
A daidai lokacinda Umaima, Zahra da kuma Muhibbah suka doson mashigar parlorn, cak suka tsaya suna duban Mahmood da Fu’ad dake tafe tamkar zasu kifa k’asa....
Tin Daga k’ololuwar kanta taji wani abu har izuwa tafin k’afarta.... Dikda fuskar Fu’ad ya canza sabida girma da yai ba kaman lokacinda Ta sanshi yana k’aramin yaro mai k’anan shekaru ba, kaman yanda nata fuskar ma ya canza hakan bai hana ta gane kamanninsa domin kaw kamaninsa da Mahmood ya kuma bayyana wanda shi Mahmood d’in babu abinda ya canza a kamanninsa da shike sanin matashi tai masa, saiko alamun girma da ya sauk’o masa.....
Take idanunta suka kad’a sukai jazir tana duban Mahmood tana tina shine mutumin da ya d’auketa da hannunsa ya azata saman doki kyakkyawan fuskarsa d’aukeda murmushi a lokacin, fuskar da take gani a idanunta tamkar bak’ar k’umurcin macijiya mai mummunar guba....Lokaci guda Ta rintse idanunta da k’arfin gaske tana jin zuciyarta na wani irin fizga tamkar zai fice daga cikin k’irjinta....
SameenaAleeyou📚
[5/23, 6:41 PM] +234 703 453 9908: *👑✨MUHIBBAH✨👑*
*006*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Suna k’arasowa kaga yanda Kuyangi ke k’amewa suna zubewa k’asa alamun girmamawa..... Zahra ta dubi Umaima fuska fal damuwa take fad’in “Aunty Umaima meke faruwa... Mai ya sami Paa da Uncle Best....?” Girgiza mata kai Umaima tai alamun itama bata sani ba... Lokaci guda Zahra tasa kai da zummar bin bayan iyayen nata ba tareda ta jira amsar Umaima ba... Saidai tuni Muhibbah ta rik’o hannunta alamun dakatarwa....
Zahra ta dubi hannunta da tsananin mamaki ganin wacece ta rik’eta... Ta kuma d’agowa sosai tana duban Muhibbah dake rik’eda hannunta guda alamun dakatar da ita..... Daidai da Umaima duban mamaki take bin Muhibbah dashi had’ida jinjina k’arfin hali irinta Muhibbah wacce zuwanta Masarautar kenan amma har tanada k’arfin halin dakatar da jinin sarauta daga gudanar da wani abu...