← Book details Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 162

Sashe 5

Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Isowarsu Fadar kenan suka tadda wata mata sai gudu take wasu mutane na biye da ita, gashin matar yayi duguzun alamun hauka, yanayin yanda take gudu kad’ai zai tabbatar maka babu hankali jikin matar.....

Dikda bata iya ganin fuskar matar gaba d’aya ba, tsikar jikinta sosai ya tashi da ganin wannan mahaukaciyar matar, suna a haka wani Bafaje ya k’araso dan yi masu iso zuwa cikin Fada....

SameenaAleeyou📚
[5/21, 10:47 PM] +234 703 453 9908: *👑✨MUHIBBA✨👑*

*004*

*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*

Muhibba bata ida firgita da lamarin matar nan ba saida matar ta k’araso ta tsaya cak gabanta tana binta da wani irin duba da idanunta masu matuk’ar firgitarwa, suffar matar kad’ai abin firgitarwa ne.... Tamkar irin bayin da aka ciwosu a zamanin farko...Gashi bata furta koda kalma ba sai duba irinta k’urilla da take binta dashi...
K’irjin Muhibba yaci gaba da bugu a daidai lokacinda wasu dogarai k’arfafa har guda uku suka k’araso a guje suka capke matar nan daketa zillewa tana waigowa tana kuma duban Muhibbah.... Itama Muhibbar duban matar take har suka b’acewa ganinta

Ansar ne ya d’an sunkuyo kad’an kana yace “Are you okay...?”
Ta jinjina masa kai a hankali a daidai sanda aka bud’e masu wani tapkeken gate mai d’aukeda kuyangi sahu sahu, dik yanda suka Zo wucewa sai kuyangi Sun risina Sun gaidasu.... Tafiya mai d’an tsawo sukai kafin suka soma hango asalin cikin Masarautar....
Dogarin da yai masu rakiya ya sadda kansa cikeda risinawa kana yace a nan zai barsu akwai wad’anda zasu Zo su k’arasa dasu ciki....

Ansar ya jinjina masa kai murmushi saman fuskarsa had’ida masa godiya...
Maidoda dubansaga Muhibba yai wacce har yanzu tamkar bata a cikin hayyacinta kana ya d’anyi gyaran murya yace “Hibbah, are you sure about this...? Hibbah kodai mu koma gida... I don’t know... But I’ve a bad feeling about this....!” Ya k’arashe cikeda kulawa...

K’ak’aro murmushi tai kana tace “There’s no going back, I’ve already started... Dole na k’arasashi...” Ta d’anyi still kana taci gaba da fad’in “Ganin matar nan ya firgitani... Sam batai kamanni da bil’adama ba...”

D’an dubanta kad’an Ansar yai kana yace “Da gani bamai hankali bace, mahaukaciya ce... Kiga yanda tazo ta tasamu a gaba da kallo tamkar mai san yi mana magana, musamman ke.... “

Muhibbah ta jinjina kai a hankali “Allah kad’ai yasan silan haukar matar nan...” Tai maganar a hankali...

Sauk’e ajiyan zuciya Ansar ya d’anyi kana yace “Muhibbah Fada gida ne mai k’unshe da halittu iri daban daban, wanda ido ka iya gani dama wanda idanuwanmu bazasu iya gani ba, Muhibbah Fada babban gida ne wanda komai ka iya faruwa cikinta, dik yanda aka ce miki akwai mulki da sarauta Toh zai matuk’ar wahala ace babu zalunci sai wad’anda Allah ya kiyayesu.... Akan neman mulki da sarauta ta duniya wasu mutanen babu abinda bazasu iya ba... Shisa sam banso Ki dage da k’udirin nan naki ba... Dan dai kawai babu yanda na iya ne....!”
Fuzar da fuci tai a hankali kana tace “Ansar mecece makomar rayuwata... Shin da wata fuska kake duban rayuwata a halin yanzu...?”

Matsowa kusanta kad’an yai kana yai mata K’uri na wasu dak’ik’ai....

“Gwarzuwar mace, Jaruma a filin daga, Mace k’wara d’aya tak data tari gungun mayak’a Majiya k’arfi masu d’aukeda manyan makamai.... TAKWABI d’aya tak da zatai zarra Ta kwantar da dubban takwabban da suka zagayeta sukai mata kawayanta...SARAUNIYA k’wara d’aya tak a illahirin Masarautar nan....!” Ido cikin ido yake dubanta sanda yake furta mata kalaman....

Tabbas sai taji tsoron da ya lullub’eta ya yaye, ji tai ya bata wani irin k’arfin gwiwa wanda ko a baya bata sami hakan ba, tabbas sanda Ta saka k’afarta cikin Masarautar nan abubuwan da suka faru shekarun baya sun shiga dawo mata daki daki, sannan tsoro da firgici sun mamaye zuciyarta, koda yanzu Ansar yai mata wad’annan kalamai saiji tai zuciyarta Ta kuma samun k’warin gwiwa....
A hankali ta jinjina masa kai kana tace “Na gode daka d’aukeni matsayin Jaruma, kuma in sha Allah bazan baka kunya ba... Zakai alfahari dani a lokacinda na kawar da mulkin Zalunci da wad’ann azzaluman bayi na Allah suka gina a doron k’asa.... Labarin Masarautar da kalan zalunci da sukai bazai shafe a tarihi ba... Zan zamto sanadin bank’ado wasu bak’ak’en sirrikansu da suka jima da bisnewa... Labarinsu zai zamto izna ga wata Al’umma da zatazo a gaba....!!” Ta k’arashe tana goge hawayen zafin Rai da ya gangaro mata....

Ansar ya sauk’e ajiyan zuciya a hankali, dan ko babu komai yanzu hankalinsa ya d’an kwanta, ya cirewa Muhibbah dik wani sauran burbud’in tsoro dake kwance cikin zuciyarta, yak’i ta tara wanda shi kansa bai isa yace ga yanda zata kaya ba, dan haka dole ya k’arfafa mata gwiwa domin kaw Muhibbah tana tsananin buk’atar hakan daga garesa....
“Yanzu ne naga asalin Muhibbar da na sani, wacce bata failing dik abinda Ta saka gabanta da izinin Allah... Always remember we are in this together, dik sanda kikaji wani abu ya canza, don’t forget I’ll always be here... Muhibbah ina sonki... With all my heart, bayan labarin gaba d’aya da naji yau, kin kuma zama tauraruwa d’aya tak a birnin zuciyata... I’ll wait for you till the end of this...!” Ya k’arashe cikin tsananin sanyin murya wanda ya sanya wani b’angare na zuciyar Muhibbah tsananin tausayin Ansar d’in... Ansar da mahaifiyarsa sune komai na rayuwarta... Mutanen da suka bud’e mata k’ofofin Alkhairai a lokacinda Duniya tai mata d’aurin goro... Mutanen da suka zamto shimfid’a mai taushi a gareta a lokacinda dik yanda ta saka hak’ark’arinta kaya ne mai tsananin suka... Shin ta yaya zata mance halarcin wad’ann bayin Allah a gareta... Da izinin Allah bazata tab’a watsa masu k’asa a idanu ba... Zasu sameta mai rik’oda Alk’awari.... Suna nan a haka muryar wasu kuyangi ‘yanmata guda biyu ya katse masu nisar da sukai a duniyar tunani su duka biyun....

Cikin ladabi irinta babban gida Kuyangin suka gaidasu kana guda d’aya Ta d’auki luggage d’in Muhibbah dake gefen k’afar Ansar yayinda guda d’aya tai masu jagoranci zuwa sashen Gimbiya Turai Giwar Sarki kuma uwar Taurari Hud’u dake a wannan masarauta....

***

Daga yanda yake tsaye saman bene hannayensa hard’e yana kuma nazarin mahaukaciyar matar da ya hango dogarai na kokawan kamata, shin wacece ita...? Tambayar da yai masa karan tsaye a zuciyarsa.... Yana nan a haka Ubandoma ya shigo cikeda risinawa had’ida fad’uwa k’asa yana kwasan gaisuwa....

Yarima Mahmood ya jinjina masa kai ba tareda ya amsa gaisuwar tasa ba, lokaci guda ya soma takowa gaban Ubandoma had’ida yin gyaran murya kad’an
“Ubandoma...!” Yarima Mahmood ya ambato sunansa cikin muryarsa mai cikeda k’warjini....

Ubandoma ya amsa a lada ce yana mai furta “Allah shi taimakeka...”

Yarima Mahmood yaci gaba da fad’in “Wacece mahaukaciyar cen da d’azu naga dogarai suna kokawan kamata....?”

Tambayar da ya haifarwa Ubandoma fad’uwar gaba....
Gumi ya shiga karyo masa ya rasa mai zai furta domin kaw Giwa tai masa kashedi mai tsananin kan irin sirrukan da zai bayyanawa d’anta Mahmood wanda a bayan tafiyarsa abubuwa da dama sun faru cikin Masarautar....

Gyaran murya da Yarima Mahmood yai ne ya dawo da Ubandoma daga duniyar tinaninda ya tafi, ya shiga furta “Tuba nike Allah shi baka yawan rai.... Ai wannan mahaukaciya da kake gani, yau shekaru goma sha biyar kenan tana fama da jinyar tab’in kwanya.....”

“Shekaru goma sha biyar.....?” Yarima Mahmood ya maimaita da sigar tambaya...

Kan Ubandoma a k’asa yake jinjinawa alamun tabbatarwa kana yaci gaba da fad’in “K’warai kuwa Allah shi taimakeka....”

Shiru na d’an lokaci ya gifta kana Yarima Mahmood ya kuma d’an takawa kad’an har lokacin hannayensa hard’e Ta baya kana ya d’an dakata a daidai jikin gini yana mai k’arewa kampacecen masarautar nasu kallo iya ganinsa sabida tsananin girma da fad’i da Masarautar kedashi.....
Yanada tarin tambayoyi da suke buk’atar amsa....

Kaikaitowa yai yana duban Ubandoma wanda Ke zube k’asa kana yace “Wacece wannan matar...? ‘Yantacciya ce kokuwa baiwace...?”

SameenaAleeyou 📚
[5/22, 9:35 PM] +234 703 453 9908: *👑✨MUHIBBAH✨👑*

*005*

*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*

Ubandoma ya had’iyi miyau da k’yar kana ya kuma risina yana mai furta “Allah shi taimaki Babban Yariman wannan masarauta, ita wannan mata ina tsammanin ba cikin Masarautar nan take ba... Randa dik ta b’alle ne sai ta shigo cikin Masarautar nan....” Ya k’arashe cikin sark’ewar harshe...

Da wasu irin idanu Mahmood Ke dubansa, ba don ya aminta da kalaman dake fita daga bakin Ubandoma ba....
Lokaci guda ya juyo sosai yana duban Ubandoma, saida ya d’ibi wasu dak’ik’ai a haka kana yace “Ya akai har ta tsallake manyan k’ofofi dake a cikin Masarautar nan ta shigo...?”
Ubandoma ya kuma had’iyan wani miyau d’in da k’yar kana yai k’ok’arin had’o kalamai saman harshensa....

“Allah shi baka yawan rai.... Kasan idan akace mutum nada tab’in hankali komai zai iyayi... Ba yau ce rana ta farko da mahaukaciyar nan ta k’wace ta shigo Fadar nan ba... Dik randa ta k’wace daga turun ta takan fantasmo cikin Masarautar nan aita kokawan fitar da ita.....!” Ya k’arashe yana mai kuma d’aga hannu alamun jinjina yana mai furta “Allah shi baka yawan rai.....!”

Shiru ya kuma biyowa kana Yarima Mahmood ya kumayin gyaran murya, wannan karon sunan Ubandoma ya kirawo cikin wane irin siga mai firgitarwa kana yaci gaba da fad’in “Idan na samu cikin zancenka akwai abinda ba gaskiya ba, zanyi maka horo mai tsanani....!”
Daga haka yasa kai ya nufo k’asa cikin sassarfa da zafin nama...

***

Sashen bak’i Umaima ta sauk’esu, kafin ta iso tuni an cika gabansu da kayan motsa baki, sai bayan shud’ewar wani lokaci Umaima ta k’araso fuskarta d’aukeda murmushin nan nata mai kyau, gefe da ita Zahra ce suna tafe tare dukansu cikin shiga irinta mulki da sarauta....
Tin daga nesa gaban Muhibbah ke fad’uwa, su Umaima da Zahara suna ci gaba da k’arasowa cikin parlorn k’irjinta na tsananta bugu..... Lokaci guda taji k’afafunta sun rinjayeta Ta mik’e tsaye tana dubansu yanda suke k’arowa garesu....
Ansar d’in ma mik’ewa tsaye yai murmushi kwance saman fuskarsa...

Maraba da juna Umaima da Ansar suka somayi kana Umaima ta gabatar masa da Zahra d’iyar d’an uwanta....
Ansar ya d’an risinar da kansa fuska fal murmushi yana mai furta “Barkanki ranki shi dad’e, da fatan mun sameku lafiya...”
Chapter 5 · 0% Book details