Sashe 18
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ido cikin ido suke duban juna itada Yazeed, ga tsananin bugu da k’irjinta keyi, tamkar ta tsatta ma wannan fuskar tasa miyau haka takeji... Shiko sosai ya had’e rai yanai mata wane irin duba.. K’aran tafiyar mutane da suka soma jiyowa ya sanya tsoro ya kuma bayyana a fuskar Muhibbah tai k’ok’arin sa kai zata rab’a ta gefen Yazeed saidai tuni ya fizgota sun shige tsakankanin gini hakan yai daidai da d’aukewar wutan lantarki...K’irjinta yaci gaba da bugawa, duhu ya soma shigowa dan haka kana iya ganin mutum amma duru duru, tana iya hango Farin fuskan Yazeed cikin duhun yanai mata alamu da tai shiru....
Zuciyarta taci gaba da tsinkewa sanda taji tafiyar yana nufosu sosai, tai saurin rintse idanunta a hankali yayinda Yazeed yaci gaba da k’are mata kallo from head to toe dan tsaf yana iya ganinta cikin duhun nan dashike shi Allah yayisa mai idon kallon mata...
Giwa ce da Jakadiya suka taho zasu shige wani k’ofar, saida suka d’an tsaya kusan yanda Yazeed da Muhibbah Ke lab’e suna tatauna wasu al’amararsu da suka shafi cikin gidan
Muhibbah najin sanda suka ci gaba da tafiya suka shige wata k’ofar ta sauk’e ajiyan zuciya a hankali...
Suna shigewa Muhibbah tai saurin matsawa baya tana sakin huci a hankali, lokaci guda take k’ok’arin saka kai zata shige dan ko takan Yazeed bata kuma bi ba tamkar wani babu abinda ya faru...Yazeed da ya kafeta da mayun idanunsa yana k’are mata kallo saurin tare gabanta yai da hannunsa guda kana yace “And just where do you think you are going..? Fad’a min zakiyi mai kikazo yi nan... Wacece Ke....? mai ya kawoki wajen nan..?!”
Banda bugu babu abinda k’irjinta keyi, tsananin tsanarsa ne kwance cikin idanunta, bata d’ago fuskarta ba har lokacin saima bugu da k’irjinta Ke ci gaba da yi..
Mamaki ya cika Yazeed ganin tai masa banza kaman bataji abinda yake fad’i ba.... Wacece ita...? Yai tambayar a zuciyarsa... Ga duhu da ya gauraye wajen saiko hasken walk’iya dake haskawa lokaci zuwa lokaci...
A hankali yake k’ok’arin mik’a hannunsa da niyyan d’ago fuskarta... K’irjinta yaci gaba da bugawa, zuciyarta naci gaba da mata zafi.... K’iris ya rage hannunsa bai sauk’a samar fuskarta ba wayarsa dake aljihun wandonsa ya d’auki ruri... Yai saurin mik’a hannu ya ciro wayar hasken wayar ya haske fuskarsa tarau, tai saurin karkatar da fuskarta sabida tsananin k’yank’yaninsa da ya sauk’o mata dikda Uban gayun dake jikinsa....
A yayinda hankalinsa ya ya karkata kan wayar salulansa Muhibbah ta hangi fad’uwan abu mai kamada sark’a ta mata daga aljihun nasa... Tana ganin sanda ya d’aga wayar yana mai juya baya, hakan ya bata daman silalewa tai saurin d’aukar sarkar tana mai sakar masa muguwar kallo kana ta juya cikin sauri ta fice daga wajen k’irjinta sai bugu yake tamkar ana iza mata guduma....
Sauri sauri ta nufo k’asa zuciyarta bata daina tsinkewa ba, dik wani motsin da zatai sai taji tamkar yanzu ne suka bangaji juna ita da Yazeed, uwa uba hannunta da takeji tamkar ba a jikinta yake ba har yanzu... Ji take tamkar ta guntile hannun ta jefar idan ta tuna sanda ya fizgo hannun nata suka b’oye... Takai dubanta ga hannun nata, sai lokacin ta tina ashe akwai sark’a rik’e a hannun nata... Idan bata b’ata gani ba wannan design d’in jewelry d’in irinsa ta gani a kunnen Rahima yau da safe da suka had’u a k’ofar Bayi...Toh kodai nata ne..? Ya akai yazo hannun Yazeed..? Tambayar dataji na tasowa daga k’asar zuciyarta... Ta saki murmushi a hankali dan ko babu komai ta sami wani abin...
Sanda ta sauk’o k’asa ta tadda kuyangi da dama wannan karon sai kai komo suke, dik wanda tazo giftawa cikin Kuyangin sai sun risina Sun gaidata, itama har ta koya daga wajensu Umaima saidai ta jinjina masu kai murmushi saman fuskarta alamun amsawa... Tana tafe cikin kantamemen parlorn mai tsawo da fad’in gaske ta hango Umaima tsaye daga waje ta cikin glass d’in sliding door.... Sauk’e ajiyan zuciya tai a hankali kana ta nufi k’ofar da take hango Umaima, saidai tana isa jikin k’ofar ta hango Fu’ad zaune saman wasu kujeru na shak’atawa yayi zama irinta masu mulki k’afafu d’aya bisa d’aya, da alama magana sukeda Umaimar...
Fu’ad ya murmusa kad’an kana yace “Kawai tambayarki nake, a ina kika samota...?”
Umaima ta murmusa kad’an itama kana tace “Prince F kenan, ai abin ne ya bani mamaki, naga friends d’ina da dama sukan Zo Masarautar nan, baka tab’a tambayar koda sunayensu ba dikda cewa su sukan damu da zancen Princes d’in Masarautar nan... Kaga kuwa bazakaga laifina ba dan na tambaya kodai kodai....?” Ta k’arashe da sigar zolaya tana kashe masa idanu...
Ya murmusa a hankali kana yace “I can’t deny that she’s kind of.... Beautiful...!” Ya k’arashe yana alamu da hannayensa tamkar wani mai describing irin kyaun da ya hango tattareda ita....
Umaima tai murmushi mai d’an sauti wannan karon kana tace “Prince F kenan kaidai kawai ka nad’ani matsayin campaign director d’inka dan Muhibbah k’anwarmu ce tinda k’anwar Ansar ce...”
“Muhibbah..!” Ya nanata sunan a hankali kana yace “Beloved..!” Yana maganan yana jinjina kai lokaci guda yaci gaba da fad’in “Ta dace da sunanta.....!”
Sabon bugun zuciya ne ya sauk’arwa Muhibbah tai saurin jada baya tana maida numfashi a hankali had’ida lumshe idanunta, wayoyin kanta suna k’ok’arin kwancewa... Anya zata iya k’arasa abinda ta fara... Wata zuciya taceda ita “Ke Saudatu what have you gotten yourself into...?”
Take kuma taji wani b’angare na zuciyar nata na fad’i mata “Toh mahaifinki fah... Ta yaya zaki San asalin abinda ya samesa idan baki dawo ba...? Sannan mahaifiyarki da kika rasa fah.... Dik uk’uba da masifa da kika shiga a baya fah...? Shikenan sunci banza suna rayuwarsu cikin jin dad’i da zaluntar wasu al’umman... Saudatu zaki iya... Zaki iya abinda kika riga kika fara... Tabbas zaki iya...!!”
Da wannan shawari na zuciyarta taji natsuwa na zuwa mata a hankali... Ta waiga gefe ta hangi wata Kuyanga zata shige... K’arasawa tai gareta ta tareta tana tambayarta ko ina d’akin Zahra yake....?
Kuyangar ta nuna mata wani b’angare nan cikin parlorn da shima benen za’a d’ale kana tace “Ta nan ne Rankishi dad’e...” Tai mata nuni da b’angaren benen dake kallon hagu, dashike irin babban matakalan nan ne mai kunne biyu d’aya na kallon b’angaren dama yanda ta sauk’o bada jimawa ba saman d’ayan na kallon b’angaren hagu...
Muhibbah ta jinjina kai kana tace “Muje ki nuna min....”
Kuyangar ta d’an d’ago tana dubanta kana ta kuma sadda idanunta tana fad’in “Kiyi hak’uri Rankishi dad’e bana d’aya daga cikin amintattun dake haurawa d’akin Gimbiya Zahra’u... Amma idan kika haura d’akin nata a nan yake...”
Jinjina mata kai Muhibbah tai kana tace “Kina iya tafiya..”
Kuyangar ta jinjina kai alamun amsawa kana Muhibbah ta nufi benen kaman yanda Kuyangar ta sanar da ita...
Matsakaicin wajene mai kyaun gaske Shima, Muhibbah ta tsaya daga parlorn tana k’arema wajen kallo, tabbas sai a b’adda mutum b’att ba’aji d’uriyarsa ba a gida irin wannan... D’akuna guda biyu ta hango nan ta nufi d’akin dake daga gefen dama.. Ta d’anyi knocking a hankali sallama saman bakinta... Jin ba’a amsata ba ya sanyata d’an tura k’ofar a hankali... Nan ta hangota kwance saman royal bed da akai ma d’akin ado dashi wanda yake d’an tsurut a tsakiyar d’akin sabida girma da d’akin kedashi... Tai K’uri tana duban yarinyar dake baccinta hankali kwance... Ta tsinci kanta tana mai sakin murmushi, lokaci guda ta shigo d’akin had’ida tura k’ofar a hankali kaman mai tsoron kada ta tasheta...
Muhibbah ta k’araso gaban gadon tana k’arewa Zahra kallo k’aunar yarinyar na kuma shigarta, batasan dalili ba amma dik tsanar da taiwa mahaifin yarinyar bata hango tsanar tattareda yarinyar saima k’aunarta da takeji na shigarta a hankali musamman dataji cewa ta rasa mahaifiyarta, kaman yanda itama ta rasa mahaifiyarta sannan a kusan shekaru irinta Zahran Ta rasa nata mahaifiyar itama... Janyo bargo tai ta rufawa Zahra kasancewar anyi ruwa garin ya d’anyi sanyi kana ta d’auki remote control d’in AC ta rage mata... Lokaci guda ta zauna a gefenta tana dubanta...
A hankali Zahra ke bud’e idanunta har ta bud’esu tarau tana duban Muhibbah dake sakar mata murmushi...
Zahra Ta mik’e sosai ta zauna murmushi saman fuskarta...Kafin ta sami zarafin magana Muhibbah tace da ita “How are you feeling now...?”
Yarinyar ta d’anyi mata K’uri murmushin bai bar fuskarta ba kana tace “Much better...”
Muhibbah ta d’an jinjina kai alamun rashin sabo kana tace “Akwai yanda ke maki ciwo kuma...?”
Kanta ta kuma girgizawa alamun a’a...
“Kin sha maganinki na dare...?”
Take annurin fuskar yarinyar ya d’an d’auke alamun basu shiri da magani...
Muhibbah takai dubanta ga yanda magungunan Ke aje bisa ruwa a gefe, kana ta isa ta d’auko...
Zahra tai raurau kana tace “Paa ke sakani nasha dole... Banson drugs...”
Gefe da ita Muhibbah ta zauna kana tace “Let me teach you something...” Tai maganan tana mai b’alle maganin kana tace “Oya close your eyes now and open your mouth... Just think of your favorite candy, kiyi tunanin shi kike sha... There....!” Ta k’arashe tana mai saka maganin bakin Zahra...
Dik yanda Muhibbah tace Zahra tai hakan takeyi, a haka har Ta ida bata magungunan.... Su duka biyun fuskokinsu ya cika da annuri...
Tsaye yai nan jikin k’ofa yana dubansu... It’s been a while since he saw his daughter as happy as she’s right now, akwai wani murmushi da takeyi wanda tun bayan rasuwar mahaifiyarta bai kuma hangowa a fuskarta ba sai yau.... So yake budurwar da suke tareda Zahra ta juyo yaga fuskarta don bayanta kawai yake hangowa amma sai bugu k’irjinsa keyi a hankali lokaci guda yana hango tsananin Farin ciki dake tattareda d’iyar tasa...
Yai k’asaitaccen murmushi a hankali, bazaiso wani abu ya gifta tsakanin wannan Farin ciki da Zahra Ke ciki ba... A hankali yasa kai kaman zai juya, saidai tuni Zahra ta hangosa... Ta d’an bud’e murya had’ida kiran sunansa...
Dummm!!! Haka k’irjin Muhibbah ya buga...
Zahra taci gaba da fad’in “Paa ka shigo ku gaisa da Aunty Muhibbah...!”
Zuciyarta taci gaba da tsinkewa sanda taji tafiyar yana nufosu sosai, tai saurin rintse idanunta a hankali yayinda Yazeed yaci gaba da k’are mata kallo from head to toe dan tsaf yana iya ganinta cikin duhun nan dashike shi Allah yayisa mai idon kallon mata...
Giwa ce da Jakadiya suka taho zasu shige wani k’ofar, saida suka d’an tsaya kusan yanda Yazeed da Muhibbah Ke lab’e suna tatauna wasu al’amararsu da suka shafi cikin gidan
Muhibbah najin sanda suka ci gaba da tafiya suka shige wata k’ofar ta sauk’e ajiyan zuciya a hankali...
Suna shigewa Muhibbah tai saurin matsawa baya tana sakin huci a hankali, lokaci guda take k’ok’arin saka kai zata shige dan ko takan Yazeed bata kuma bi ba tamkar wani babu abinda ya faru...Yazeed da ya kafeta da mayun idanunsa yana k’are mata kallo saurin tare gabanta yai da hannunsa guda kana yace “And just where do you think you are going..? Fad’a min zakiyi mai kikazo yi nan... Wacece Ke....? mai ya kawoki wajen nan..?!”
Banda bugu babu abinda k’irjinta keyi, tsananin tsanarsa ne kwance cikin idanunta, bata d’ago fuskarta ba har lokacin saima bugu da k’irjinta Ke ci gaba da yi..
Mamaki ya cika Yazeed ganin tai masa banza kaman bataji abinda yake fad’i ba.... Wacece ita...? Yai tambayar a zuciyarsa... Ga duhu da ya gauraye wajen saiko hasken walk’iya dake haskawa lokaci zuwa lokaci...
A hankali yake k’ok’arin mik’a hannunsa da niyyan d’ago fuskarta... K’irjinta yaci gaba da bugawa, zuciyarta naci gaba da mata zafi.... K’iris ya rage hannunsa bai sauk’a samar fuskarta ba wayarsa dake aljihun wandonsa ya d’auki ruri... Yai saurin mik’a hannu ya ciro wayar hasken wayar ya haske fuskarsa tarau, tai saurin karkatar da fuskarta sabida tsananin k’yank’yaninsa da ya sauk’o mata dikda Uban gayun dake jikinsa....
A yayinda hankalinsa ya ya karkata kan wayar salulansa Muhibbah ta hangi fad’uwan abu mai kamada sark’a ta mata daga aljihun nasa... Tana ganin sanda ya d’aga wayar yana mai juya baya, hakan ya bata daman silalewa tai saurin d’aukar sarkar tana mai sakar masa muguwar kallo kana ta juya cikin sauri ta fice daga wajen k’irjinta sai bugu yake tamkar ana iza mata guduma....
Sauri sauri ta nufo k’asa zuciyarta bata daina tsinkewa ba, dik wani motsin da zatai sai taji tamkar yanzu ne suka bangaji juna ita da Yazeed, uwa uba hannunta da takeji tamkar ba a jikinta yake ba har yanzu... Ji take tamkar ta guntile hannun ta jefar idan ta tuna sanda ya fizgo hannun nata suka b’oye... Takai dubanta ga hannun nata, sai lokacin ta tina ashe akwai sark’a rik’e a hannun nata... Idan bata b’ata gani ba wannan design d’in jewelry d’in irinsa ta gani a kunnen Rahima yau da safe da suka had’u a k’ofar Bayi...Toh kodai nata ne..? Ya akai yazo hannun Yazeed..? Tambayar dataji na tasowa daga k’asar zuciyarta... Ta saki murmushi a hankali dan ko babu komai ta sami wani abin...
Sanda ta sauk’o k’asa ta tadda kuyangi da dama wannan karon sai kai komo suke, dik wanda tazo giftawa cikin Kuyangin sai sun risina Sun gaidata, itama har ta koya daga wajensu Umaima saidai ta jinjina masu kai murmushi saman fuskarta alamun amsawa... Tana tafe cikin kantamemen parlorn mai tsawo da fad’in gaske ta hango Umaima tsaye daga waje ta cikin glass d’in sliding door.... Sauk’e ajiyan zuciya tai a hankali kana ta nufi k’ofar da take hango Umaima, saidai tana isa jikin k’ofar ta hango Fu’ad zaune saman wasu kujeru na shak’atawa yayi zama irinta masu mulki k’afafu d’aya bisa d’aya, da alama magana sukeda Umaimar...
Fu’ad ya murmusa kad’an kana yace “Kawai tambayarki nake, a ina kika samota...?”
Umaima ta murmusa kad’an itama kana tace “Prince F kenan, ai abin ne ya bani mamaki, naga friends d’ina da dama sukan Zo Masarautar nan, baka tab’a tambayar koda sunayensu ba dikda cewa su sukan damu da zancen Princes d’in Masarautar nan... Kaga kuwa bazakaga laifina ba dan na tambaya kodai kodai....?” Ta k’arashe da sigar zolaya tana kashe masa idanu...
Ya murmusa a hankali kana yace “I can’t deny that she’s kind of.... Beautiful...!” Ya k’arashe yana alamu da hannayensa tamkar wani mai describing irin kyaun da ya hango tattareda ita....
Umaima tai murmushi mai d’an sauti wannan karon kana tace “Prince F kenan kaidai kawai ka nad’ani matsayin campaign director d’inka dan Muhibbah k’anwarmu ce tinda k’anwar Ansar ce...”
“Muhibbah..!” Ya nanata sunan a hankali kana yace “Beloved..!” Yana maganan yana jinjina kai lokaci guda yaci gaba da fad’in “Ta dace da sunanta.....!”
Sabon bugun zuciya ne ya sauk’arwa Muhibbah tai saurin jada baya tana maida numfashi a hankali had’ida lumshe idanunta, wayoyin kanta suna k’ok’arin kwancewa... Anya zata iya k’arasa abinda ta fara... Wata zuciya taceda ita “Ke Saudatu what have you gotten yourself into...?”
Take kuma taji wani b’angare na zuciyar nata na fad’i mata “Toh mahaifinki fah... Ta yaya zaki San asalin abinda ya samesa idan baki dawo ba...? Sannan mahaifiyarki da kika rasa fah.... Dik uk’uba da masifa da kika shiga a baya fah...? Shikenan sunci banza suna rayuwarsu cikin jin dad’i da zaluntar wasu al’umman... Saudatu zaki iya... Zaki iya abinda kika riga kika fara... Tabbas zaki iya...!!”
Da wannan shawari na zuciyarta taji natsuwa na zuwa mata a hankali... Ta waiga gefe ta hangi wata Kuyanga zata shige... K’arasawa tai gareta ta tareta tana tambayarta ko ina d’akin Zahra yake....?
Kuyangar ta nuna mata wani b’angare nan cikin parlorn da shima benen za’a d’ale kana tace “Ta nan ne Rankishi dad’e...” Tai mata nuni da b’angaren benen dake kallon hagu, dashike irin babban matakalan nan ne mai kunne biyu d’aya na kallon b’angaren dama yanda ta sauk’o bada jimawa ba saman d’ayan na kallon b’angaren hagu...
Muhibbah ta jinjina kai kana tace “Muje ki nuna min....”
Kuyangar ta d’an d’ago tana dubanta kana ta kuma sadda idanunta tana fad’in “Kiyi hak’uri Rankishi dad’e bana d’aya daga cikin amintattun dake haurawa d’akin Gimbiya Zahra’u... Amma idan kika haura d’akin nata a nan yake...”
Jinjina mata kai Muhibbah tai kana tace “Kina iya tafiya..”
Kuyangar ta jinjina kai alamun amsawa kana Muhibbah ta nufi benen kaman yanda Kuyangar ta sanar da ita...
Matsakaicin wajene mai kyaun gaske Shima, Muhibbah ta tsaya daga parlorn tana k’arema wajen kallo, tabbas sai a b’adda mutum b’att ba’aji d’uriyarsa ba a gida irin wannan... D’akuna guda biyu ta hango nan ta nufi d’akin dake daga gefen dama.. Ta d’anyi knocking a hankali sallama saman bakinta... Jin ba’a amsata ba ya sanyata d’an tura k’ofar a hankali... Nan ta hangota kwance saman royal bed da akai ma d’akin ado dashi wanda yake d’an tsurut a tsakiyar d’akin sabida girma da d’akin kedashi... Tai K’uri tana duban yarinyar dake baccinta hankali kwance... Ta tsinci kanta tana mai sakin murmushi, lokaci guda ta shigo d’akin had’ida tura k’ofar a hankali kaman mai tsoron kada ta tasheta...
Muhibbah ta k’araso gaban gadon tana k’arewa Zahra kallo k’aunar yarinyar na kuma shigarta, batasan dalili ba amma dik tsanar da taiwa mahaifin yarinyar bata hango tsanar tattareda yarinyar saima k’aunarta da takeji na shigarta a hankali musamman dataji cewa ta rasa mahaifiyarta, kaman yanda itama ta rasa mahaifiyarta sannan a kusan shekaru irinta Zahran Ta rasa nata mahaifiyar itama... Janyo bargo tai ta rufawa Zahra kasancewar anyi ruwa garin ya d’anyi sanyi kana ta d’auki remote control d’in AC ta rage mata... Lokaci guda ta zauna a gefenta tana dubanta...
A hankali Zahra ke bud’e idanunta har ta bud’esu tarau tana duban Muhibbah dake sakar mata murmushi...
Zahra Ta mik’e sosai ta zauna murmushi saman fuskarta...Kafin ta sami zarafin magana Muhibbah tace da ita “How are you feeling now...?”
Yarinyar ta d’anyi mata K’uri murmushin bai bar fuskarta ba kana tace “Much better...”
Muhibbah ta d’an jinjina kai alamun rashin sabo kana tace “Akwai yanda ke maki ciwo kuma...?”
Kanta ta kuma girgizawa alamun a’a...
“Kin sha maganinki na dare...?”
Take annurin fuskar yarinyar ya d’an d’auke alamun basu shiri da magani...
Muhibbah takai dubanta ga yanda magungunan Ke aje bisa ruwa a gefe, kana ta isa ta d’auko...
Zahra tai raurau kana tace “Paa ke sakani nasha dole... Banson drugs...”
Gefe da ita Muhibbah ta zauna kana tace “Let me teach you something...” Tai maganan tana mai b’alle maganin kana tace “Oya close your eyes now and open your mouth... Just think of your favorite candy, kiyi tunanin shi kike sha... There....!” Ta k’arashe tana mai saka maganin bakin Zahra...
Dik yanda Muhibbah tace Zahra tai hakan takeyi, a haka har Ta ida bata magungunan.... Su duka biyun fuskokinsu ya cika da annuri...
Tsaye yai nan jikin k’ofa yana dubansu... It’s been a while since he saw his daughter as happy as she’s right now, akwai wani murmushi da takeyi wanda tun bayan rasuwar mahaifiyarta bai kuma hangowa a fuskarta ba sai yau.... So yake budurwar da suke tareda Zahra ta juyo yaga fuskarta don bayanta kawai yake hangowa amma sai bugu k’irjinsa keyi a hankali lokaci guda yana hango tsananin Farin ciki dake tattareda d’iyar tasa...
Yai k’asaitaccen murmushi a hankali, bazaiso wani abu ya gifta tsakanin wannan Farin ciki da Zahra Ke ciki ba... A hankali yasa kai kaman zai juya, saidai tuni Zahra ta hangosa... Ta d’an bud’e murya had’ida kiran sunansa...
Dummm!!! Haka k’irjin Muhibbah ya buga...
Zahra taci gaba da fad’in “Paa ka shigo ku gaisa da Aunty Muhibbah...!”