Sashe 7
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har saida su Yarima Mahmood da Fu’ad suka shige babban gwanin Giwa (Parlorn Giwa) kana Muhibbah ta d’an saki hannun Zahra had’ida sadda idanunta kad’an murmushin k’arfin hali saman fuskarta take furta “A.... Ki gafarceni ranki shi dad’e.... A ganina bai kamata Ki tunk’ari mahaifinki a halinda yake ciki ba... Kaman ransa ya b’ace yake... Allah shi taimakeki.... Ki gafarceni...!” Ta k’arashe tana mai sadda idanunta k’asa..:
Gyara tsayuwa sosai Zahra tai tana dubanta kana tace “Wait... And who do think you’re... Wacece Ke da har kike fad’in ra’ayinki akan abinda ya dace nayi da kuma wanda bai dace nayi ba...
Quién crees que eres..” (Kina tunanin Ke wacece) Ta k’arashe tana mai tsare Muhibbah da idanunta.....
Umaima ce ta d’anyi gyaran murya kana ta kamo hannun Zahra tace “Zahra I think Muhibbah is right... Bakinsan mai ya b’ata ran Paa d’inki ba, kuma kinga bashi kad’ai bane... Besides nan gidan sarauta ne Zahra bazakiyi komai kai tsaye a bainar jama’a ba kaman yanda kikeyi a Spain... Abu k’ank’ani a nan sai ya zama scandal... Kuma nasan bazakiso Ki baiwa mahaifinki kunya ba... Muhibbah taimakonki tai Zahra... Godiya ya kamata Ki mata a ganina....” Ta k’arashe murmushi saman fuskarta tana mai dubansu duka biyu daga Zahran har Muhibbar....
Shiru Zahra tai ba tareda ta furta komai ba sai d’an sadda idanunta k’asa da tai tana mai jinjina maganar... Lokaci guda ta d’ago ta d’an dubi Muhibbah kaman zatai magana sai kuma ta dubi Umaima tace “Aunty Umaima ni na shige ciki...” Tana kaiwa nan tasa kai tai shigewarta zuciyarta a b’ace....
Suka bitada kallo har ta b’acewa ganinsu kana Umaima ta maidoda dubantaga Muhibbah... Lokaci guda suka sakarwa juna murmushi kana Umaima tace “Ina fata kiyi hak’uri da d’abi’un Zahra... She’s going through a lot, bata jima da rasa mahaifiyarta ba, sannan bata son dawowa k’asar nan... Akan dole take zaune a k’asar nan shisa take wasu abubuwan da take, shisa take jin haushin kowa da kuma komai a k’asar., You know a teenagers are, a gab’ar take....Amma Zahra yarinyar kirkice ina mai tabbatar miki... Zaki k’aunaceta sannu a hankali....” Ta k’arashe kyakkyawan murmushi saman fuskarta...
Murmusawa kad’an Muhibba ma tai kana tace “Karki damu, na fahimceta... Kallo d’aya nai mata na fahimci ita d’in yarinya ce mai saurin shiga rai... Kuma inaji a jikina we would get along someday...!”
Umaima ta kuma murmusawa kana tace “Muje koh...!”
Muhibbah ta jinjina kai murmushi saman fuskarta kana suka nufi dogon ginin....
***
Daga yanayin tafiyar da suke zaka fahimci ba lafiya ba, hakan yasa suna shigowa Babban gwanin Giwa Kaga yanda kuyangi Ke darewa suna basu waje... Kaf suka fice waje suna masu kwasan gaisuwa, tuni Mahmood da Fu’ad sun nufi upstairs yanda suka tadda Giwa da Jakadiya suna tattaunawa....
Tuni Jakadiya ta risina tana kwasan gaisuwa, Giwa ta jinjina mata kai alamun ta fice ta basu waje.... Take Jakadiya ta nufi k’ofa kai a k’asa tana mai kuma kirariwa yaran Sarkin....
Yanayinsu kad’ai ya tabbatarwa Giwa wani abu na faruwa, kan Fu’ad a k’asa har lokacin bai daina sakin huci a hankali ba....
Giwa tai gyaran murya tana mai furta “Lafiya Sadauki meke faruwa... Ya na ganku haka..? Wani abin ne ya faru...?!”
Da idanunsa masu firgitarwa ya tsare Fu’ad, hannayensa hard’e Ta baya, lokaci guda yake furta “Maami what’s wrong with your son...? Wasu irin labari nakeji cewa zaman da yayi a Cyprus babu abinda ya tsinana... Shin da gaske ne baida wani sana’a sai shan kayan maye..?!!” Ya k’arashe cikin kakkausar murya....
Daidai lokacin Yarima Jamal ya shigo yana mai dubansu d’aya bayan d’aya yanda sukai tsaye carko carko....
Yarima Mahmood yaci gaba da fad’in “Maami Wai meke faruwa ne a Masarautar nan.... Meke faruwa cikin gidan nan....? I need answers...!!” Ya k’arashe wannan karon yana duban mahaifiyar tasu....
Jamal dake tsaye yana rarraba idanu cikin wane irin yanayi k’arasowa yai a hankali had’ida d’an dafa hannun Mahmood.. Lokaci guda yake furta “Calm down Yaya... Babu wani abin tashin hankali dake wakana a Masarautar nan, I promise you....” Yana maganar yana duban mahaifiyar tasu data tsare Mahmood da idanu....
Duban mahaifiyar tasu Mahmood ya kumayi kaman zai magana, saidai tuni ta mik’e tsaye ta iso garesa, lokaci guda ta sakar masa murmushi hannayensa rik’e cikin nata take furta “Haka ne D’ah na, ka yarda da batun d’an uwanka babu wani abindake wakana wanda ya canza a Masarautar nan.... Kada ka soma d’iban jita jitan babban gida kaji d’ah na... Kaine Magajin mahaifinku, a zaman gida irin wannan na sarauta da d’inbin al’umma dole kak’i gani kak’i ji....”
Girgiza kai Mahmood yai kana yace “Maami ba wannan ba... Mai Fu’ad yake nufi da yace Yazeed Keda alhakin kasancewarsa haka...? Menene suka faru da bana nan...??!”
Wannan karon harta Fu’ad saida ya d’ago yana duban Mahmood tsoro da firgici k’arara saman fuskarsa, Wani irin bugu Giwa taji a k’irjinta tamkar an aza mata guduma....Ta ware idanunta sosai tana aikawa Fu’ad wani irin duba na tuhuma....
Jamal ne ya katse shirun da yin gyaran murya kana yace “Yaya kasan halin Yazeed, kasan among us all babu wanda yake shiri dashi face ni da nake tolerating d’insa da halayyarsa... Yaya kasan Fu’ad nada zuciya matuk’a.... So ya fad’i haka ne kawai to get back at Yazeed, sabida yasan idan yace haka bazaka k’yale Yazeed ba, Bawai da wani nufi ya fad’i hakan ba... And one more thing Yaya... Yes, Fu’ad ya had’uda iftila’ai da jarabawa na shan kayan maye, but that was tin yana Cyprus, yeah koda ya dawo he was depressed sabida gani yake ya k’arar da rayuwarsa a iska ba tareda yayi abinda ya kaisa Cyprus din ba, wannan ya kuma Sa Fu’ad ya koma ruwa tsundum shaye shayen miyagun k’wayoyi to get rid of his problems... Anyi ta k’ok’arin ya rabu da abin gaba d’aya don har Rehab a Abuja an kaishi... Allah ya taimaka a cen Rehabilitation center d’in ya rabu da abin completely...ya dawo bai shan komai, ina mai tabbatar maka Fu’ad bai shan komai a halin yanzu Yaya....!” Ya k’arashe cikin tsananin sanyin murya...
A hankali Giwa ta sauk’e wani irin ajiyan zuciya cikeda jin dad’i, dama ta sani idan ba Jamal ba babu mai iya gyarota, shi d’in d’an albarka ne mai tsananin sanyin zuciya a tsakanin yaranta....
K’uri Mahmood yai masa, dan gaba d’aya cikin ‘yan uwan nasa ya sani Jamal is different, tun tasowarsu mutum ne da ko mai zai fad’a maka iyakacin gaskiyarsa kenan dan haka take yaji sanyi can k’asar zuciyarsa... Tausayin Fu’ad ya kamasa....
A hankali ya soma takowa ya k’araso gaban Fu’ad d’in, ya d’an saka hannu saman kafad’arsa ya dafasa.... Fu’ad ya d’ago idanunsa masu zuban hawaye yana duban Mahmood...
K’uri Mahmood yai masa cikeda tausayawa kana yace “Is okay Fu’ad... Mu ‘yan Adam ne masu kuskure... We ain’t perfect, dukkanmu muna kuskure... Mafi alkhairi a cikinmu Sune wad’anda idan suka fahimci laifinsu sai su komaga Allah su tuba.... Ko wane irin abin kunya ka jawowa Masarautar nan ya riga ya wuce Fu’ad... Its all in the past now, ba’a amfani da abinda ya riga ya shud’e..!”
Kaman daga sama suka sinkayo muryar Yazeed yana fad’in “Correction brother!!”
Gaba d’aya suka juyo suna duban Yazeed dake takowa cikin d’akin cikeda isa da k’asaita, lokaci guda Yazeed yaci gaba da fad’in “Unfortunately a rayuwa irinta babban gida kaman Fada, dik abinda kayi a baya zai cimmaka a gaba... Baya tab’a shud’ewa haka nan kawai ya b’ace a tarihi bai bar wani sign ba....Am I right...?!” Ya k’arashe shu’umin murmushin nan nasa saman fuskarsa....
Giwa dai K’uri tai masa tana jin kalaman d’an nata tamkar da ita yakeyi.... Yayinda Fu’ad ya mik’e cikin hawaye yana duban Mahmood, lokaci guda yake furta “Im sorry Yaya..!!” Daga haka bai kuma cewa komai ba sai sa kai da yai ya fice Daga parlorn cikin sauri....
Mahmood ya dubi Yazeed da wasu irin idanu saidai a b’angaren Yazeed d’in ko a jikinsa saima shu’umin murmushin nasa dake bisa fuskarsa, lokaci guda yama k’arasa saman d’aya daga cikin hanshak’an kujerun da sukaima parlorn k’awanya ya hakince kan guda d’aya had’ida bud’e hannayensa ya bazasu cikin kujerar kana ya d’auki k’afarsa guda ya aza bisa d’ayan... Ya daiyi zama irinta masu jin mulki da kuma isa... Ya tasasu gaba yana binsu da kallo murmushin bai bar saman fuskarsa ba, saima juya zoben azirfa dake yatsarsa guda da yakeyi a hankali....
Tamkar tv haka Jamal da Giwa Ke dubansa, shid’inma suke yake duba yana mai ci gaba da kad’a k’afarsa da ya azata saman guda..
Girgiza kai kurum Mahmood yai kana yasa kai yai ficewarsa shima, yayinda Jamal ya janyo hannun Mahaifiyarsu ya nufi bedroom da ita yana fad’in “Muje ki huta Maami....!” Babu musu tabi umarnin d’an nata, zuciyarta na wane irin yankewa, dan tinda taji labarin bayyanar mahaukaciyar nan a fada tasan wannan sharan fage ne, dole akwai wani babban al’amari da ya faru cikin Masarautar, fatanta Jakadiya Ta dawo mata da batu mai dad’i...
***
Muhibbah na zaune tana rarraba idanu tana duban kyau da tsarin d’akinda aka sauk’eta cikinsa Umaima ta turo k’ofa ta shigo... Cikin sauri Muhibbah ta mik’e tsaye su duka biyu suna sakin murmushiwa junansu...
Umaima taci gaba da fad’in “Kiyi hak’uri na barki Ke kad’ai... Gashi ban samu ganin Maami ba, ta riga ta haura sama, Ina tunanin wani abin ne ya faru, zai wuya Ta sauk’o k’asa a yau d’un saidai ko zuwa gobe idan Allah ya kaimu....”
Girgiza kai Muhibbah tai a hankali kana tace “Babu komai Ranki shi dad’e, har dai Ina cikin gidan zamu gaisa ai, kinsan masu mulki basa son tak’ura inaga zaifi kyau ki k’yaleta har zuwa wani lokacin....!” Ta k’arashe kyakkyawan murmushi kwance saman black beauty face d’inta da yake tas dashi babu alamun koda k’warzani...
Umaima ta murmusa kana tace “Muhibbah Ina mamakin ya akai kika San abubuwa da dama gameda masu mulki da kuma babban gida... Saikace a gidan sarauta kika girma... Kodai a babban gida kika girma ne...?”
Murmusawa kad’an Muhibbar ma tai kana tace “Ni kuwa Ta ina zan girma cikin gidan sarauta Ranki shi dad’e, bayan gidanmu mu uku tak muke rayuwa cikinta, daga ni sai Mummy saiko Yayana Ansar...”
Gyara tsayuwa sosai Zahra tai tana dubanta kana tace “Wait... And who do think you’re... Wacece Ke da har kike fad’in ra’ayinki akan abinda ya dace nayi da kuma wanda bai dace nayi ba...
Quién crees que eres..” (Kina tunanin Ke wacece) Ta k’arashe tana mai tsare Muhibbah da idanunta.....
Umaima ce ta d’anyi gyaran murya kana ta kamo hannun Zahra tace “Zahra I think Muhibbah is right... Bakinsan mai ya b’ata ran Paa d’inki ba, kuma kinga bashi kad’ai bane... Besides nan gidan sarauta ne Zahra bazakiyi komai kai tsaye a bainar jama’a ba kaman yanda kikeyi a Spain... Abu k’ank’ani a nan sai ya zama scandal... Kuma nasan bazakiso Ki baiwa mahaifinki kunya ba... Muhibbah taimakonki tai Zahra... Godiya ya kamata Ki mata a ganina....” Ta k’arashe murmushi saman fuskarta tana mai dubansu duka biyu daga Zahran har Muhibbar....
Shiru Zahra tai ba tareda ta furta komai ba sai d’an sadda idanunta k’asa da tai tana mai jinjina maganar... Lokaci guda ta d’ago ta d’an dubi Muhibbah kaman zatai magana sai kuma ta dubi Umaima tace “Aunty Umaima ni na shige ciki...” Tana kaiwa nan tasa kai tai shigewarta zuciyarta a b’ace....
Suka bitada kallo har ta b’acewa ganinsu kana Umaima ta maidoda dubantaga Muhibbah... Lokaci guda suka sakarwa juna murmushi kana Umaima tace “Ina fata kiyi hak’uri da d’abi’un Zahra... She’s going through a lot, bata jima da rasa mahaifiyarta ba, sannan bata son dawowa k’asar nan... Akan dole take zaune a k’asar nan shisa take wasu abubuwan da take, shisa take jin haushin kowa da kuma komai a k’asar., You know a teenagers are, a gab’ar take....Amma Zahra yarinyar kirkice ina mai tabbatar miki... Zaki k’aunaceta sannu a hankali....” Ta k’arashe kyakkyawan murmushi saman fuskarta...
Murmusawa kad’an Muhibba ma tai kana tace “Karki damu, na fahimceta... Kallo d’aya nai mata na fahimci ita d’in yarinya ce mai saurin shiga rai... Kuma inaji a jikina we would get along someday...!”
Umaima ta kuma murmusawa kana tace “Muje koh...!”
Muhibbah ta jinjina kai murmushi saman fuskarta kana suka nufi dogon ginin....
***
Daga yanayin tafiyar da suke zaka fahimci ba lafiya ba, hakan yasa suna shigowa Babban gwanin Giwa Kaga yanda kuyangi Ke darewa suna basu waje... Kaf suka fice waje suna masu kwasan gaisuwa, tuni Mahmood da Fu’ad sun nufi upstairs yanda suka tadda Giwa da Jakadiya suna tattaunawa....
Tuni Jakadiya ta risina tana kwasan gaisuwa, Giwa ta jinjina mata kai alamun ta fice ta basu waje.... Take Jakadiya ta nufi k’ofa kai a k’asa tana mai kuma kirariwa yaran Sarkin....
Yanayinsu kad’ai ya tabbatarwa Giwa wani abu na faruwa, kan Fu’ad a k’asa har lokacin bai daina sakin huci a hankali ba....
Giwa tai gyaran murya tana mai furta “Lafiya Sadauki meke faruwa... Ya na ganku haka..? Wani abin ne ya faru...?!”
Da idanunsa masu firgitarwa ya tsare Fu’ad, hannayensa hard’e Ta baya, lokaci guda yake furta “Maami what’s wrong with your son...? Wasu irin labari nakeji cewa zaman da yayi a Cyprus babu abinda ya tsinana... Shin da gaske ne baida wani sana’a sai shan kayan maye..?!!” Ya k’arashe cikin kakkausar murya....
Daidai lokacin Yarima Jamal ya shigo yana mai dubansu d’aya bayan d’aya yanda sukai tsaye carko carko....
Yarima Mahmood yaci gaba da fad’in “Maami Wai meke faruwa ne a Masarautar nan.... Meke faruwa cikin gidan nan....? I need answers...!!” Ya k’arashe wannan karon yana duban mahaifiyar tasu....
Jamal dake tsaye yana rarraba idanu cikin wane irin yanayi k’arasowa yai a hankali had’ida d’an dafa hannun Mahmood.. Lokaci guda yake furta “Calm down Yaya... Babu wani abin tashin hankali dake wakana a Masarautar nan, I promise you....” Yana maganar yana duban mahaifiyar tasu data tsare Mahmood da idanu....
Duban mahaifiyar tasu Mahmood ya kumayi kaman zai magana, saidai tuni ta mik’e tsaye ta iso garesa, lokaci guda ta sakar masa murmushi hannayensa rik’e cikin nata take furta “Haka ne D’ah na, ka yarda da batun d’an uwanka babu wani abindake wakana wanda ya canza a Masarautar nan.... Kada ka soma d’iban jita jitan babban gida kaji d’ah na... Kaine Magajin mahaifinku, a zaman gida irin wannan na sarauta da d’inbin al’umma dole kak’i gani kak’i ji....”
Girgiza kai Mahmood yai kana yace “Maami ba wannan ba... Mai Fu’ad yake nufi da yace Yazeed Keda alhakin kasancewarsa haka...? Menene suka faru da bana nan...??!”
Wannan karon harta Fu’ad saida ya d’ago yana duban Mahmood tsoro da firgici k’arara saman fuskarsa, Wani irin bugu Giwa taji a k’irjinta tamkar an aza mata guduma....Ta ware idanunta sosai tana aikawa Fu’ad wani irin duba na tuhuma....
Jamal ne ya katse shirun da yin gyaran murya kana yace “Yaya kasan halin Yazeed, kasan among us all babu wanda yake shiri dashi face ni da nake tolerating d’insa da halayyarsa... Yaya kasan Fu’ad nada zuciya matuk’a.... So ya fad’i haka ne kawai to get back at Yazeed, sabida yasan idan yace haka bazaka k’yale Yazeed ba, Bawai da wani nufi ya fad’i hakan ba... And one more thing Yaya... Yes, Fu’ad ya had’uda iftila’ai da jarabawa na shan kayan maye, but that was tin yana Cyprus, yeah koda ya dawo he was depressed sabida gani yake ya k’arar da rayuwarsa a iska ba tareda yayi abinda ya kaisa Cyprus din ba, wannan ya kuma Sa Fu’ad ya koma ruwa tsundum shaye shayen miyagun k’wayoyi to get rid of his problems... Anyi ta k’ok’arin ya rabu da abin gaba d’aya don har Rehab a Abuja an kaishi... Allah ya taimaka a cen Rehabilitation center d’in ya rabu da abin completely...ya dawo bai shan komai, ina mai tabbatar maka Fu’ad bai shan komai a halin yanzu Yaya....!” Ya k’arashe cikin tsananin sanyin murya...
A hankali Giwa ta sauk’e wani irin ajiyan zuciya cikeda jin dad’i, dama ta sani idan ba Jamal ba babu mai iya gyarota, shi d’in d’an albarka ne mai tsananin sanyin zuciya a tsakanin yaranta....
K’uri Mahmood yai masa, dan gaba d’aya cikin ‘yan uwan nasa ya sani Jamal is different, tun tasowarsu mutum ne da ko mai zai fad’a maka iyakacin gaskiyarsa kenan dan haka take yaji sanyi can k’asar zuciyarsa... Tausayin Fu’ad ya kamasa....
A hankali ya soma takowa ya k’araso gaban Fu’ad d’in, ya d’an saka hannu saman kafad’arsa ya dafasa.... Fu’ad ya d’ago idanunsa masu zuban hawaye yana duban Mahmood...
K’uri Mahmood yai masa cikeda tausayawa kana yace “Is okay Fu’ad... Mu ‘yan Adam ne masu kuskure... We ain’t perfect, dukkanmu muna kuskure... Mafi alkhairi a cikinmu Sune wad’anda idan suka fahimci laifinsu sai su komaga Allah su tuba.... Ko wane irin abin kunya ka jawowa Masarautar nan ya riga ya wuce Fu’ad... Its all in the past now, ba’a amfani da abinda ya riga ya shud’e..!”
Kaman daga sama suka sinkayo muryar Yazeed yana fad’in “Correction brother!!”
Gaba d’aya suka juyo suna duban Yazeed dake takowa cikin d’akin cikeda isa da k’asaita, lokaci guda Yazeed yaci gaba da fad’in “Unfortunately a rayuwa irinta babban gida kaman Fada, dik abinda kayi a baya zai cimmaka a gaba... Baya tab’a shud’ewa haka nan kawai ya b’ace a tarihi bai bar wani sign ba....Am I right...?!” Ya k’arashe shu’umin murmushin nan nasa saman fuskarsa....
Giwa dai K’uri tai masa tana jin kalaman d’an nata tamkar da ita yakeyi.... Yayinda Fu’ad ya mik’e cikin hawaye yana duban Mahmood, lokaci guda yake furta “Im sorry Yaya..!!” Daga haka bai kuma cewa komai ba sai sa kai da yai ya fice Daga parlorn cikin sauri....
Mahmood ya dubi Yazeed da wasu irin idanu saidai a b’angaren Yazeed d’in ko a jikinsa saima shu’umin murmushin nasa dake bisa fuskarsa, lokaci guda yama k’arasa saman d’aya daga cikin hanshak’an kujerun da sukaima parlorn k’awanya ya hakince kan guda d’aya had’ida bud’e hannayensa ya bazasu cikin kujerar kana ya d’auki k’afarsa guda ya aza bisa d’ayan... Ya daiyi zama irinta masu jin mulki da kuma isa... Ya tasasu gaba yana binsu da kallo murmushin bai bar saman fuskarsa ba, saima juya zoben azirfa dake yatsarsa guda da yakeyi a hankali....
Tamkar tv haka Jamal da Giwa Ke dubansa, shid’inma suke yake duba yana mai ci gaba da kad’a k’afarsa da ya azata saman guda..
Girgiza kai kurum Mahmood yai kana yasa kai yai ficewarsa shima, yayinda Jamal ya janyo hannun Mahaifiyarsu ya nufi bedroom da ita yana fad’in “Muje ki huta Maami....!” Babu musu tabi umarnin d’an nata, zuciyarta na wane irin yankewa, dan tinda taji labarin bayyanar mahaukaciyar nan a fada tasan wannan sharan fage ne, dole akwai wani babban al’amari da ya faru cikin Masarautar, fatanta Jakadiya Ta dawo mata da batu mai dad’i...
***
Muhibbah na zaune tana rarraba idanu tana duban kyau da tsarin d’akinda aka sauk’eta cikinsa Umaima ta turo k’ofa ta shigo... Cikin sauri Muhibbah ta mik’e tsaye su duka biyu suna sakin murmushiwa junansu...
Umaima taci gaba da fad’in “Kiyi hak’uri na barki Ke kad’ai... Gashi ban samu ganin Maami ba, ta riga ta haura sama, Ina tunanin wani abin ne ya faru, zai wuya Ta sauk’o k’asa a yau d’un saidai ko zuwa gobe idan Allah ya kaimu....”
Girgiza kai Muhibbah tai a hankali kana tace “Babu komai Ranki shi dad’e, har dai Ina cikin gidan zamu gaisa ai, kinsan masu mulki basa son tak’ura inaga zaifi kyau ki k’yaleta har zuwa wani lokacin....!” Ta k’arashe kyakkyawan murmushi kwance saman black beauty face d’inta da yake tas dashi babu alamun koda k’warzani...
Umaima ta murmusa kana tace “Muhibbah Ina mamakin ya akai kika San abubuwa da dama gameda masu mulki da kuma babban gida... Saikace a gidan sarauta kika girma... Kodai a babban gida kika girma ne...?”
Murmusawa kad’an Muhibbar ma tai kana tace “Ni kuwa Ta ina zan girma cikin gidan sarauta Ranki shi dad’e, bayan gidanmu mu uku tak muke rayuwa cikinta, daga ni sai Mummy saiko Yayana Ansar...”