Sashe 150
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bud’e idanunta tai masu zuban ruwa Ta ware su tsaf saman kyakkyawan fuskarsa wanda ya cika da rauni a yanzu saikace ba Sarkin nata ba..
A hankali Ta soma furta “Rankaidad’e Maiyasa zaka ce haka, bayan bada ganganci ka aikata hakan ba.. Maiyasa zakace haka bayan kaid’in Allah ne ya k’addari had’uwarku da ita don ka zamto garkuwa ma jaririyarta wanda azzalumai suke neman ganin bayan ahalinmu a wancan lokacin.. Allah ya maido da Zahra cikin ahalinta ne shiyasa ya k’addari rik’onta a hannunka..! You’re like an Angel Your Highness..Ka bayyana a rayuwar Zahra kuma ka haskaka rayuwarta, ka bata dukkan kulawa da ya dace.. Rankaidad’e ka mance cewa buge Umma da kayi ko k’warzani bata samu ba, kawai kaid’in ka bayyana ne domin ka kula da Zahra..! Sannan Bawa baya shige ajalinsa, kowa ajalinsa a rubuce yake Rankaidad’e.. Kuma Idan akwai wad’anda zamuce sunyi sanadin mutuwar Umma toh ba kowa bane face Giwa da ‘ya’yanta domin kuwa tun bayan abinda ya sameni da mahaifina, zuciyar Umma yayi rauni bata kuma lafiya ba ga juna biyu da take d’aukedashi.. Koda Ta haifi Zahra cikin jinya take batayi lafiya ba.. Idan baka manta ba kaman yanda kace Likita yace her heart was weak toh haka d’in ne zuciyarta tayi matuk’ar rauni tun bayan wad’ancan iftila’i da suka auku mana.. Baka kashe Umma ba Rankaidad’e.. Lokacinta ne yayi sannan Giwa da ‘ya’yanta sune sanadi..!” Cikin tsananin rawar murya take ci gaba da fad’in “You gave my sister a life Rankaidad’e..! Thank you, thank you for taking care of my sister..? Thank you your Highness..!” Muryarta ya sark’e sabida kuka...Lokaci guda Mahmood ya janyota cikin jikinta cikin jikinsa kaman jira take nan kuma ta fashe da kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro... Ya matseta cikin jikinsa sosai yana lallashinta.. Haka yayita riritata yana bata baki had’ida jero mata kalaman k’auna masu sanyaya zuciya wanda har saida tayi mamakin Wai Dama ya iya fad’in kalmomi haka... Kaman dai ba Rankaidad’e d’in data sani ba...
Rayuwa ta kumayin dad’i abubuwa Sun kuma warwarewa, ahalin sun cika da Farin ciki maras misaltuwa... Tuni an soma gudanar da shirye shiryen bukin tarewar Muhibbah da Mahmood.. Shi Mahmood kam ma da anbi Ta nashi ne baza’a tsayawa wani biye wa al’ada ba zai tare da amaryarsa amma Ummi tak’i amincewa tace sai nan da sati guda bayan an ida yiwa Muhibbah duk wasu tanadi da ake na al’ada an kuma yi bukin yanda yake a al’adance.. Tuni ta killace Muhibbah yanda ko samun ganinta Mahmood baiyi, gaba d’aya ji yake wannan al’ada da sarautar ba k’aramin tak’urasa sukai ba... Mommy ma ta koma gida dan gudanar da ‘yan kintse kintse, a zaton Muhibbah mommy ta tafi kenan bazatazo Bikin ba, haka taita magiya tana cewa Mommy ta taya ayi da ita, Mommy tace bayan abubuwan da sukai musamman Yawale da Gudidi ita har kunyar Muhibbar take balle ahalinta, uwa uba kuma ga abinda Ansar yazo yayi daga baya... Da k’yar dai ta amince watak’ila ta dawo ayi da ita...
Zahra da Umaima basu sama basu k’asa, hidimar tasu ce ta ko ina... Ranan alhamis ake saka ran Amarya Muhibbah zata tare yayinda juma’a ake bukin nad’in sarki Mahmood..
Fadah ta kacame gaba d’aya, matan masu mulki daga ta ko ina Zuwa suke, kama daga matan Su Talba Galadima Matawalle da dai sauran Hakimai, harta matar Baba Wambai tazo, Majidad’i kansa ya samu Mahmood ya risina gaba garesa ya basa hak’uri dan ya yarda idan Rana ta fito tafin hannu bata kareta, Zakaran da Allah ya nufa da cara ko Ana muzuru ko ana shaho toh fah sai yayi... Hassada taki ne ga mai rabo inji masu iya magana... Nan ya sanar da Mahmood d’in duk abubuwan da suka k’ulla masa shida Yazeed.. Ya kuma nemi gafara.. Mahmood yace bai tab’a rik’esa cikin zuciyarsa ba Allah yasa ya amfana da darasin rayuwa da ya d’auka bisa abubuwan da suka aikata.. Shi kuwa Ja’afar tsaresa da idanu yai yana fad’i a hankali daidai kunnen Majidad’in “Fadah bata marhaban da munafukai balle azzalumai, dan haka ka tabbata tuban gaske kayi ba tuban d’an muzuru ba dan idan na fahimci tuban d’an muzuru kayi.. Zaka amshi sakamako irin wanda ya dace dakai..!” Majidad’i ya d’an d’ago yana duban Ja’afar dake tsume da fuska yana dubansa shima.. Ubandoma ya dubguri k’eyar Majidad’i yace “Yarima yana magana amsa masa ake..! Hattara Majidad’i..!”
Majidad’i ya jinjina kai a hankali yace “In sha Allah Masarauta zata sameni da cika alk’awari.. Tuban k’warai nayi Yarima Ja’afar..!”
Ja’afar ya jinjina kai a hankali ba tareda ya furta komai ba...
Manyan masu sarautun gargajiya sai sanyawa ‘ya’yan Sarkin Albarka suke.. Tun ana sauran sati Tambura da algaita suke guguwa a masarautar... Ga duk wanda yasan Masarautar shekaru k’alilan baya ya kuma ganta yanzu yasan abubuwa da dama Sun sauya.. Wani ni’iman kwanciyar hankali da annashuwa ne zalla cikin d’inbin Masarautar...
A can b’angaren mata ma kowa ya hallara idan ka d’auke matan Waziri wanda abin kunyar da mijin su ya jaza masu ya hanasu shiga cikin mutane...
Yau ta kama laraba Washe gari ake saka ran gudanar da bukin aurensu itada Rankaidad’e... Tana zaune ana shafe tafin k’afafunta da lalle kaman yanda yake a al’ada, Umaima da Zahra suka shigo murmushi saman fuskokinsu... Zahra ta Ware idanu tana duban yanda ‘yaruwar tata ta k’ara shek’i da kyau a ‘yan kwanaki biyun da tayi a killace, tace “Kai Tia Wai Dama haka kikeda fitanennen kyau ne.. Black is gold, Kinga fuskarki kuwa.. Gaskiya Paa dole ya k’ara sadaki..!”
Umaima ta kai mata bugun wasa tana fad’in “Ja’irar yarinyar matar Baban naki ne abokiyar wasanki..”
Zahra ta d’anyi k’ara kad’an tana furta “Ouchh Aunty Umaima daga wasa.. Kuma ma ai Paa Yaya na ne ta wane b’angaren.. Ni daga yanzu ma Yaya Rankaidad’e Paapa angon Tia zanke kiransa..!” Harta da dattab’an matan dake zaune wajen saida suka nurmusa Umaima na kuma janyo kunnen Zahra guda.. Ita kaw Muhibbah shiru ta b’ace wajen tana jin wani bak’on al’amari tattareda ita, Wai bukin aurensu ake da Rankaidad’e... A tare Umaima da Zahra suka k’arasa gabanta suka duk’a, tausayinta sai ya kamasu... Umaima ta sanya hannu a robar lallen ta d’an lakata ta shafa mata a hanci tana mai furta “Be happy sister.. Coz you deserve all the happiness in the world..!” Muhibbah ta murmusa kad’an tana duban ‘yar uwar tata cikeda shauk’i... Zahra ma ta lakata lallen kad’an a yatsarta ta shafa mata a goshi tana furta “ Sé feliz hermana...!” (Ki kasance cikin Farin ciki ‘yar uwata.)
Murmushi take tana dubansu lokaci guda itama ta lakaci lallen tana k’ok’arin shafa masu suka mik’e suna zagaye kampacecen d’akin suna cewa su ba amare bane bazata shafa masu lalle ba.. Aiko nan taita binsu tana fad’in saita shafa masu suma.. Haka saida suka sa Muhibbah taita ‘yar dariya kafin suka k’yaleta.. Zahra da Umaima suka dubi juna suna ‘yar murmushi...
Muhibbah ta dubesu tana Ware idanu “I know you two are up to something again..!”
Suka murmusa a tare kana Umaima tace “Manyan bak’i muke tafe miki dasu..”
Ta d’anyi Jim tace “Manyan bak’i..”
Zahra ta jinjina kai tace “K’warai kuwa.. Wait..!” Ta isa tana mai yin iso ma bak’in..
Ga mamakin Muhibbah ba kowa bane face Meenatu aminiyarta ai ko Meenatu tana shigowa ta tafi ta rungume Muhibbah cikin murnan tsalle, lokaci guda take k’ok’arin saita kanta had’ida furta “Wayyo Rankidad’e tuba nake.. I just couldn’t hold myself..!” Muhibbah ta dungureta kad’an tana mai fad’in “Zaki sani ne... Kai k’awata naji dad’i da zuwanki zaki halarci bikina ashe..!” Meenatu tace “Of course I wouldn’t miss your wedding for any thing in the world k’awata...!” Muhibbah ta kuma rungumeta cikeda Farin ciki, nan kuma annurin fuskarta ya d’an ragu tana fad’in “Mommy fah, batazo ba..? She’s not coming koh..?!” Bata kai aya ba ta sinkayo sallaman Mommy k’awayenta guda biyu kuma aminanta na biyeda ita, Aunty Gudidi da Aunty Salma..! Su Gudidi sai rarraba idanu ake yawa mage ta fad’a talge.. Sai kwantar dakai take tana ganin abin kaman a mafarki Wai Muhibbah itace sarauniyar wannan Masarautar gaba d’aya...
SameenaAleeyou 📚
[10/6, 2:34 PM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*85*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
A hankali Ta soma furta “Rankaidad’e Maiyasa zaka ce haka, bayan bada ganganci ka aikata hakan ba.. Maiyasa zakace haka bayan kaid’in Allah ne ya k’addari had’uwarku da ita don ka zamto garkuwa ma jaririyarta wanda azzalumai suke neman ganin bayan ahalinmu a wancan lokacin.. Allah ya maido da Zahra cikin ahalinta ne shiyasa ya k’addari rik’onta a hannunka..! You’re like an Angel Your Highness..Ka bayyana a rayuwar Zahra kuma ka haskaka rayuwarta, ka bata dukkan kulawa da ya dace.. Rankaidad’e ka mance cewa buge Umma da kayi ko k’warzani bata samu ba, kawai kaid’in ka bayyana ne domin ka kula da Zahra..! Sannan Bawa baya shige ajalinsa, kowa ajalinsa a rubuce yake Rankaidad’e.. Kuma Idan akwai wad’anda zamuce sunyi sanadin mutuwar Umma toh ba kowa bane face Giwa da ‘ya’yanta domin kuwa tun bayan abinda ya sameni da mahaifina, zuciyar Umma yayi rauni bata kuma lafiya ba ga juna biyu da take d’aukedashi.. Koda Ta haifi Zahra cikin jinya take batayi lafiya ba.. Idan baka manta ba kaman yanda kace Likita yace her heart was weak toh haka d’in ne zuciyarta tayi matuk’ar rauni tun bayan wad’ancan iftila’i da suka auku mana.. Baka kashe Umma ba Rankaidad’e.. Lokacinta ne yayi sannan Giwa da ‘ya’yanta sune sanadi..!” Cikin tsananin rawar murya take ci gaba da fad’in “You gave my sister a life Rankaidad’e..! Thank you, thank you for taking care of my sister..? Thank you your Highness..!” Muryarta ya sark’e sabida kuka...Lokaci guda Mahmood ya janyota cikin jikinta cikin jikinsa kaman jira take nan kuma ta fashe da kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro... Ya matseta cikin jikinsa sosai yana lallashinta.. Haka yayita riritata yana bata baki had’ida jero mata kalaman k’auna masu sanyaya zuciya wanda har saida tayi mamakin Wai Dama ya iya fad’in kalmomi haka... Kaman dai ba Rankaidad’e d’in data sani ba...
Rayuwa ta kumayin dad’i abubuwa Sun kuma warwarewa, ahalin sun cika da Farin ciki maras misaltuwa... Tuni an soma gudanar da shirye shiryen bukin tarewar Muhibbah da Mahmood.. Shi Mahmood kam ma da anbi Ta nashi ne baza’a tsayawa wani biye wa al’ada ba zai tare da amaryarsa amma Ummi tak’i amincewa tace sai nan da sati guda bayan an ida yiwa Muhibbah duk wasu tanadi da ake na al’ada an kuma yi bukin yanda yake a al’adance.. Tuni ta killace Muhibbah yanda ko samun ganinta Mahmood baiyi, gaba d’aya ji yake wannan al’ada da sarautar ba k’aramin tak’urasa sukai ba... Mommy ma ta koma gida dan gudanar da ‘yan kintse kintse, a zaton Muhibbah mommy ta tafi kenan bazatazo Bikin ba, haka taita magiya tana cewa Mommy ta taya ayi da ita, Mommy tace bayan abubuwan da sukai musamman Yawale da Gudidi ita har kunyar Muhibbar take balle ahalinta, uwa uba kuma ga abinda Ansar yazo yayi daga baya... Da k’yar dai ta amince watak’ila ta dawo ayi da ita...
Zahra da Umaima basu sama basu k’asa, hidimar tasu ce ta ko ina... Ranan alhamis ake saka ran Amarya Muhibbah zata tare yayinda juma’a ake bukin nad’in sarki Mahmood..
Fadah ta kacame gaba d’aya, matan masu mulki daga ta ko ina Zuwa suke, kama daga matan Su Talba Galadima Matawalle da dai sauran Hakimai, harta matar Baba Wambai tazo, Majidad’i kansa ya samu Mahmood ya risina gaba garesa ya basa hak’uri dan ya yarda idan Rana ta fito tafin hannu bata kareta, Zakaran da Allah ya nufa da cara ko Ana muzuru ko ana shaho toh fah sai yayi... Hassada taki ne ga mai rabo inji masu iya magana... Nan ya sanar da Mahmood d’in duk abubuwan da suka k’ulla masa shida Yazeed.. Ya kuma nemi gafara.. Mahmood yace bai tab’a rik’esa cikin zuciyarsa ba Allah yasa ya amfana da darasin rayuwa da ya d’auka bisa abubuwan da suka aikata.. Shi kuwa Ja’afar tsaresa da idanu yai yana fad’i a hankali daidai kunnen Majidad’in “Fadah bata marhaban da munafukai balle azzalumai, dan haka ka tabbata tuban gaske kayi ba tuban d’an muzuru ba dan idan na fahimci tuban d’an muzuru kayi.. Zaka amshi sakamako irin wanda ya dace dakai..!” Majidad’i ya d’an d’ago yana duban Ja’afar dake tsume da fuska yana dubansa shima.. Ubandoma ya dubguri k’eyar Majidad’i yace “Yarima yana magana amsa masa ake..! Hattara Majidad’i..!”
Majidad’i ya jinjina kai a hankali yace “In sha Allah Masarauta zata sameni da cika alk’awari.. Tuban k’warai nayi Yarima Ja’afar..!”
Ja’afar ya jinjina kai a hankali ba tareda ya furta komai ba...
Manyan masu sarautun gargajiya sai sanyawa ‘ya’yan Sarkin Albarka suke.. Tun ana sauran sati Tambura da algaita suke guguwa a masarautar... Ga duk wanda yasan Masarautar shekaru k’alilan baya ya kuma ganta yanzu yasan abubuwa da dama Sun sauya.. Wani ni’iman kwanciyar hankali da annashuwa ne zalla cikin d’inbin Masarautar...
A can b’angaren mata ma kowa ya hallara idan ka d’auke matan Waziri wanda abin kunyar da mijin su ya jaza masu ya hanasu shiga cikin mutane...
Yau ta kama laraba Washe gari ake saka ran gudanar da bukin aurensu itada Rankaidad’e... Tana zaune ana shafe tafin k’afafunta da lalle kaman yanda yake a al’ada, Umaima da Zahra suka shigo murmushi saman fuskokinsu... Zahra ta Ware idanu tana duban yanda ‘yaruwar tata ta k’ara shek’i da kyau a ‘yan kwanaki biyun da tayi a killace, tace “Kai Tia Wai Dama haka kikeda fitanennen kyau ne.. Black is gold, Kinga fuskarki kuwa.. Gaskiya Paa dole ya k’ara sadaki..!”
Umaima ta kai mata bugun wasa tana fad’in “Ja’irar yarinyar matar Baban naki ne abokiyar wasanki..”
Zahra ta d’anyi k’ara kad’an tana furta “Ouchh Aunty Umaima daga wasa.. Kuma ma ai Paa Yaya na ne ta wane b’angaren.. Ni daga yanzu ma Yaya Rankaidad’e Paapa angon Tia zanke kiransa..!” Harta da dattab’an matan dake zaune wajen saida suka nurmusa Umaima na kuma janyo kunnen Zahra guda.. Ita kaw Muhibbah shiru ta b’ace wajen tana jin wani bak’on al’amari tattareda ita, Wai bukin aurensu ake da Rankaidad’e... A tare Umaima da Zahra suka k’arasa gabanta suka duk’a, tausayinta sai ya kamasu... Umaima ta sanya hannu a robar lallen ta d’an lakata ta shafa mata a hanci tana mai furta “Be happy sister.. Coz you deserve all the happiness in the world..!” Muhibbah ta murmusa kad’an tana duban ‘yar uwar tata cikeda shauk’i... Zahra ma ta lakata lallen kad’an a yatsarta ta shafa mata a goshi tana furta “ Sé feliz hermana...!” (Ki kasance cikin Farin ciki ‘yar uwata.)
Murmushi take tana dubansu lokaci guda itama ta lakaci lallen tana k’ok’arin shafa masu suka mik’e suna zagaye kampacecen d’akin suna cewa su ba amare bane bazata shafa masu lalle ba.. Aiko nan taita binsu tana fad’in saita shafa masu suma.. Haka saida suka sa Muhibbah taita ‘yar dariya kafin suka k’yaleta.. Zahra da Umaima suka dubi juna suna ‘yar murmushi...
Muhibbah ta dubesu tana Ware idanu “I know you two are up to something again..!”
Suka murmusa a tare kana Umaima tace “Manyan bak’i muke tafe miki dasu..”
Ta d’anyi Jim tace “Manyan bak’i..”
Zahra ta jinjina kai tace “K’warai kuwa.. Wait..!” Ta isa tana mai yin iso ma bak’in..
Ga mamakin Muhibbah ba kowa bane face Meenatu aminiyarta ai ko Meenatu tana shigowa ta tafi ta rungume Muhibbah cikin murnan tsalle, lokaci guda take k’ok’arin saita kanta had’ida furta “Wayyo Rankidad’e tuba nake.. I just couldn’t hold myself..!” Muhibbah ta dungureta kad’an tana mai fad’in “Zaki sani ne... Kai k’awata naji dad’i da zuwanki zaki halarci bikina ashe..!” Meenatu tace “Of course I wouldn’t miss your wedding for any thing in the world k’awata...!” Muhibbah ta kuma rungumeta cikeda Farin ciki, nan kuma annurin fuskarta ya d’an ragu tana fad’in “Mommy fah, batazo ba..? She’s not coming koh..?!” Bata kai aya ba ta sinkayo sallaman Mommy k’awayenta guda biyu kuma aminanta na biyeda ita, Aunty Gudidi da Aunty Salma..! Su Gudidi sai rarraba idanu ake yawa mage ta fad’a talge.. Sai kwantar dakai take tana ganin abin kaman a mafarki Wai Muhibbah itace sarauniyar wannan Masarautar gaba d’aya...
SameenaAleeyou 📚
[10/6, 2:34 PM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*85*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*