Sashe 98
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kaman yanda Sarki Mahmood ya tsara hakan ce ta kasance, shiga irinta Buzaye sukai daga shi har abokinsa Turaki harmada amintaccen Hadiminsa Barde, baka hango komai cikin nad’in fuskokinsu face karan hancinsu da k’wayan idanunsu...
Suna zaune cikin Mota suna hango dandatson mutane a k’ofar gidan Yawale sai kai komo suke, Mahmood yai k’uri wa mutanen da suke kaiwa da kawowa, Turaki ya d’an kaikaito ya dubi Mahmood dake zaune bayan Mota yace “Rankaidad’e mun iso..!”
Jinjina masa kai Mahmood yai ba tareda yace komai ba, saima sak’on da yake k’ok’arin turawa cikin waya... Yana ida tura sak’on yasa k’afafunsa ya fito daga cikin motar Barde dake zaune gaban Mota ya fito da sauri ya bud’ewa Ubangidan nasa...
Mahmood ya dubesa yace “Barde a nan dani dakai d’aya muke har sai mun koma masarauta...!”
Barde kai a k’asa yace “Allah shi taimakeka bawa bazai tab’a zama kaman kai ba... Tuba nake ka gafarceni Rankaidad’e bazan iya abinda kake fad’i ba...!”
Mahmood yai gyaran murya kad’an yace “Umarni nake baka Barde, ba shawarinka nake nema ba..!”
Barde ya jinjina kai a hankali yace “Tuba nake Allah shi taimakeka, yanda duk kace haka za’ayi...!!”
Mahmood ya jinjina kai yace dasu su k’arasa cikin Zauren taron...
Turaki da k’irjinsa ke ci gaba da bugu yasa kai suka soma tafiya...
A can gidan Mommy kuwa Gudidi da Mommy sun baiwa Ango Ansar da Amarya Muhibbah maganin bacci, K’awayen Muhibbah na nan cike d’akinta amma basuga idanun Amarya ba sun kulleta can d’akin Mommy tana shek’an bacci Tamkar macecciya.... Shima Ansar a nan d’akin dake gefe da na Mommy suka kullesa abokansa dake jiransa a sashensa Mommy ta isa ta taddasu sai trying layin Ansar suke bai shiga... Suna ganin Mommy suka soma gaidata suna sanar da ita abindake faruwa..
Damuwa k’arara saman fuskar Mommy take fad’in “A’a Wai dama bai sanar daku ba..? Ai jiya ya bar gidan nan zai kama d’aki a hotel sabida cunk’oson taron mata na biki... Kunsan akwai Amarya d’aya gidan nan bai kamata ango yana tsakani ba... Kai Musbahu ai na zaci tare kukaje kai ka masa rakiya ya kama otel d’in...?!”
Musbahu ya girgiza kai yace “Mommy wllhi ni bamuyi wannan zancen dashi ba... Kuma ga wayoyinsa duka basu shiga, mun fara damuwa da halinda ka iya kasancewa ciki...!”
Mommy ta d’an murmusa tace “Kayya Babu wani abu zumud’i ne kawai irinta sabon ango, kasan tagwayen mata garesa... Kaima satin baya akayi Naka bukin ai ya kamata ka fahimci haka...! Kudai yanzu kuyi maza ku tafi ku sami d’aurin auren k’ila yama tafi tuntuni ya mance wayoyin nasa a d’aki....!”
Abokan suka jinjina kai sukace Eh kuma hakan ka iya kasancewa, sauri sauri suka fice dan kar su rasa d’ahtoh aure...
K’awayen Muhibbah ma dake zaman jiranta a d’aki Gudidi ce ta shiga ta samesu tace Amarya tana can ana kintsata bazasu sami ganinta yanzu ba.. Hakan yasa K’awayen sukaci gaba da sabgoginsu, masu ciye ciye nayi masu tad’i nayi... Gudidi ta rakasu da harara da gefen idanu tana mai ayyanawa cikin zuciyarta “K’awarku kam kun rabu da ita kenan har abada dan mu kanmu bamusan duniyar da za’a kaita ba..!!” Ta fice tana sakin murmushin jin dad’i....
**
A can Masarautar su Raheema kuwa wata Kuyanga ce ta shigo a fujajan ta zube gaban Raheema tana fad’in “Ki gafarceni ya Shugabata wani labari na kawo...!”
Raheema ta watsa mata harara, d’aya daga cikin Hadiman dake shiryata ta dubi Baiwar tace “Ke kuwa wani labari ne zai sa ki fad’o kan Gimbiya haka, bayan Kinsan yau d’in rananta ne ranan Farin ciki ne a gareta...!”
Baiwar naci gaba da haki take fad’in “Ki gafarceni ya Shugabata wani labari nakeji na Yawo cikin Fada..!”
Raheema da ta kai matuk’a wajen tunzura da wannan baiwa, fincika tai Ta mik’e tsaye tana fad’in “Ke k’ask’antacciyar Baiwa wane labari ne zaisa ki fice hayyacinki haka.. Labari guda d’aya ke yawo cikin Fada, labarin Farin ciki... Labarin auren Gimbiya Raheema da Sarki Mahmood... Shi kad’aine labarin dake yawo cikin Fada..!!”
Baiwar na haki take girgiza kai....
Raheema da k’irjinta ke bugu batasan sanda ta damk’o wuyar Baiwar tana fad’in Ta sanar da ita labarin dake tafe da ita... Batakaiga rufe baki ba suka sinkayo sautin algaita na tashi ana ambato sunan Gimbiya Raheemah da angonta matsayin ma’arauta.....
*MUHIBBAH*
*61*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Raheemah bata daina jijjiga Baiwar nan tana mulke mata fuska da k’unshin dake hannunta ga algaita na kuma tashi duk ya karad’e cikin Masarautar.... Daidai nan Gimbiya Zeenat Ta shigo a fusace hankali tashe tana fad’in “Raheemah mai nake ji, Wai Yazeed aka aura miki ba Mahmood ba... Ta yaya wannan abu ya kasance...?!!”
Raheemah na kuka tamkar mai tab’in hankali duk ta shafe jikinta da k’unshin da ake zana mata tace “Aunty wllhi k’arya ne... Wanda suka Zo d’aura auren su sukayi munafunci, Aunty Mahmood na sona nayi imani yana sona bazai tab’a barina ma k’aninsa ba... Aunty dan Allah tun kafin su tafi ki taresu su warware wannan auren wasan da sukayi su maida aurena kan mijina Mahmood... Aunty I can’t lose Mahmood... Wayyo na shiga uku.... Dan Allah Ki fita ki taresu wllhi dariya za’a mana cikin Masarautar nan... Sanin kanki kishiyoyin Ummah bazasu barmu musha iska da habaici ba..!!”
Gimbiya Zeenat naci gaba da huci take furta “Ai duk laifinki ne... Ga irinta nan..! Ga irin ranar da nake jiye miki, kin maida kanki tamkar wata kariya... Na tabbata Mahmood yasan Keda d’anuwansa kunada alak’a a b’oye shiyasa ya juya akalar auren ya koma kan d’anuwansa... Ai abin kiyi Farin ciki ne yanzu sai kuyi mai dalili.!!!”
Raheemah ta katseta da fad’in “Aunty dan Allah kije ki tari Hakiman nan kar su fice a Masarautar nan... Mishkila aka samu Mahmood ne mijin ba Yazeed ba..!!” Ta k’arashe tana mai nufan k’ofa kai babu ko rufi tsaban ta shiga tashin hankali maras misaltuwa... Gimbiya Zeenat tabi bayanta a fujajan tana k’ok’arin dakatar da ita inaa Raheema bataji bata gani tuni Ta tsallake bene ta nufi dandatson jama’an dake haraban Masarautar....
Abinka da babban gida sai aka samu abinyi, bayi na k’usk’us ‘yan gida kaw masu jimami nayi masu dariya na yi...
Haka Raheema ta fice tana fad’iwa masu algaita su dakata... Ta kutsa sosai har gaban su Galadima tana fad’in wannan auren bai d’auru ba... Sarki Mahmood ne mijinta ba Yarima Yazeed ba..!
Galadima ya girgiza kai yace “Rankidad’e kaman yanda Sarki Mahmood ya umarta hakan mukayi... Yarima Yazeed shine mijinki ba Sarki Mahmood ba...!”
Raheema ta shiga fatali da kayan kid’e kid’e dake wajen tana fad’in k’arya ne wannan auren bai d’auru ba...!
Ala dole wasu bayi ‘yanmata guda hud’u suka kamata aka shige da ita cikin gida sai hauka take wanda hakan sosai ya zubda Martaban masarautarsu... ‘Yanuba kuwa suka sami abin goriwa Zeenat dan sun tabbata wannan abin kunya da Raheema tayi tsaf sai ya koma Masarautar da Gimbiya Zeenat ke aure... Haka Gimbiya Zeenat ta aje shagalin buki a gefe ta shiga rara kuka tana kaico, shikenan Sarautar da take hari ta hanyar auren Mahmood da k’anwarta zatayi ya tashi a aiki... Har abada bazata tab’a samun hakan ba, wannan abin kunya ma da Raheemah tayi bai k’aresu da komai ba face fad’a zubda mata jima da tayi... Yanzu ko nan cikin masarautarsu mahaifarta batada wani kima balle aje can masarautarsu mijinta... Sosai Gimbiya Zeenat Ke kuka tana nadaman abubuwan da tayi a baya... Kaicon son zuciya, yau ga yanda son zuciya ya kaita... Dama komai zakayi ka saka tsoron Allah a ciki idan kuwa ba haka ba sai Kaga ba daidai ba...!
**
Bakin Turaki ya gaza rufuwa, Mahmood ya shammacesa... Wato dama kansa ya nemawa auren Muhibbah... Gashi kuma ya karb’awa kansa auren nata ba tareda wakilcin kowa ba... Kai sai a gaisheda Mahmood inji Turaki..
Fataken Buzaye sun amshi auren Muhibbah yanda suka buk’aci a basu amaryarsu su tafi can k’asarsu da ita...
Yawale yace kar suji komai su taho da motar da sukayo haya su biyosa suje har yanda zasu d’auke amaryarsu... Ba tareda b’ata lokaci ba kuwa sukabi bayan Yawale dake bisa babur d’insa, nan take suka nufo gidansu Muhibbah...
Aka bar mutane da jimamin abunda ya faru da jinjina lamarin, wasu daga cikin Baffanin Ansar da suke Uba d’aya da mahaifinsa suka titsiye Yawale suna fad’in rashin kyautawar da yayi ace baka San mutane ba baka San daga yanda suke ba ka d’auki mutum sukutum ka basu...!
Yawale yace Babu ruwansu tunda ba ‘yarsu bace kuma Ansar shine kad’ai dolensa basu ba...! Haka dai Yawale yai masu d’add’aya ya barsu nan suna jimamin wannan abinda ya faru wanda saikace wani wasan kwaikwayo... Abinda suke ganina wasannin kwaikwayo da littafai sai gashi zahiri a gabansu....
Shidai Mahmood sai karantar Yawale kurum yake da idanu.... Suna isa unguwar Yawale yace suyi Parking daga can nesa za’a fito da ita... Turaki yai parking daga nesa kaman yanda Yawale ya buk’ata...
Nan take Baffah Yawale ya ciro wayarsa a aljihu ya kirawo Gudidi yace da ita masu d’aukan Amarya sun iso Ta fito da Amarya...
Gudidi tace an gama gasu nan fitowa.... Cikin sand’a don ko Mommy bataso ta ganta ta kirawo k’awarsu Salame tace ta taimaka mata su fito da Muhibbah tinda dama bacci take....
Salame dai tsoro saman fuskarta tabi bayan Gudidi suka shiga d’akin yanda Muhibbah Ke yashe tana bacci, tausayin Muhibbah ya kama Salame... Idanunta sukai rau rau tana dubanta.... Gudidi kaw ko a jikinta saima d’auko mayafi da tai Ta rufawa Muhibbar tana k’ok’arin mik’ar da ita tsaye....
Ta dubi Salame dake tsaye tana duban Muhibbah cikeda tausayawa kana taja tsuka a hankali tace “Toh Sarkin tausayi da imani, dramar ya k’are taimaka min zakiyi mu fitar da ita daga cikin gidan nan....!”
Salame Tai k’ok’arin maida k’wallan da suka ciko idanunta tace “Gudidi babu wanda yasan duniyar da za’a kai yarinyar nan... Babu wanda yasan su waye suka auri yarinyar nan..? Wasu irin mutane ne... Na gari ne ko na banza... ‘Yan shan jini ne koma matsafa ne... Gudidi baki tausayin yarinyar nan..? Baki tsoron hakki..!!”
Suna zaune cikin Mota suna hango dandatson mutane a k’ofar gidan Yawale sai kai komo suke, Mahmood yai k’uri wa mutanen da suke kaiwa da kawowa, Turaki ya d’an kaikaito ya dubi Mahmood dake zaune bayan Mota yace “Rankaidad’e mun iso..!”
Jinjina masa kai Mahmood yai ba tareda yace komai ba, saima sak’on da yake k’ok’arin turawa cikin waya... Yana ida tura sak’on yasa k’afafunsa ya fito daga cikin motar Barde dake zaune gaban Mota ya fito da sauri ya bud’ewa Ubangidan nasa...
Mahmood ya dubesa yace “Barde a nan dani dakai d’aya muke har sai mun koma masarauta...!”
Barde kai a k’asa yace “Allah shi taimakeka bawa bazai tab’a zama kaman kai ba... Tuba nake ka gafarceni Rankaidad’e bazan iya abinda kake fad’i ba...!”
Mahmood yai gyaran murya kad’an yace “Umarni nake baka Barde, ba shawarinka nake nema ba..!”
Barde ya jinjina kai a hankali yace “Tuba nake Allah shi taimakeka, yanda duk kace haka za’ayi...!!”
Mahmood ya jinjina kai yace dasu su k’arasa cikin Zauren taron...
Turaki da k’irjinsa ke ci gaba da bugu yasa kai suka soma tafiya...
A can gidan Mommy kuwa Gudidi da Mommy sun baiwa Ango Ansar da Amarya Muhibbah maganin bacci, K’awayen Muhibbah na nan cike d’akinta amma basuga idanun Amarya ba sun kulleta can d’akin Mommy tana shek’an bacci Tamkar macecciya.... Shima Ansar a nan d’akin dake gefe da na Mommy suka kullesa abokansa dake jiransa a sashensa Mommy ta isa ta taddasu sai trying layin Ansar suke bai shiga... Suna ganin Mommy suka soma gaidata suna sanar da ita abindake faruwa..
Damuwa k’arara saman fuskar Mommy take fad’in “A’a Wai dama bai sanar daku ba..? Ai jiya ya bar gidan nan zai kama d’aki a hotel sabida cunk’oson taron mata na biki... Kunsan akwai Amarya d’aya gidan nan bai kamata ango yana tsakani ba... Kai Musbahu ai na zaci tare kukaje kai ka masa rakiya ya kama otel d’in...?!”
Musbahu ya girgiza kai yace “Mommy wllhi ni bamuyi wannan zancen dashi ba... Kuma ga wayoyinsa duka basu shiga, mun fara damuwa da halinda ka iya kasancewa ciki...!”
Mommy ta d’an murmusa tace “Kayya Babu wani abu zumud’i ne kawai irinta sabon ango, kasan tagwayen mata garesa... Kaima satin baya akayi Naka bukin ai ya kamata ka fahimci haka...! Kudai yanzu kuyi maza ku tafi ku sami d’aurin auren k’ila yama tafi tuntuni ya mance wayoyin nasa a d’aki....!”
Abokan suka jinjina kai sukace Eh kuma hakan ka iya kasancewa, sauri sauri suka fice dan kar su rasa d’ahtoh aure...
K’awayen Muhibbah ma dake zaman jiranta a d’aki Gudidi ce ta shiga ta samesu tace Amarya tana can ana kintsata bazasu sami ganinta yanzu ba.. Hakan yasa K’awayen sukaci gaba da sabgoginsu, masu ciye ciye nayi masu tad’i nayi... Gudidi ta rakasu da harara da gefen idanu tana mai ayyanawa cikin zuciyarta “K’awarku kam kun rabu da ita kenan har abada dan mu kanmu bamusan duniyar da za’a kaita ba..!!” Ta fice tana sakin murmushin jin dad’i....
**
A can Masarautar su Raheema kuwa wata Kuyanga ce ta shigo a fujajan ta zube gaban Raheema tana fad’in “Ki gafarceni ya Shugabata wani labari na kawo...!”
Raheema ta watsa mata harara, d’aya daga cikin Hadiman dake shiryata ta dubi Baiwar tace “Ke kuwa wani labari ne zai sa ki fad’o kan Gimbiya haka, bayan Kinsan yau d’in rananta ne ranan Farin ciki ne a gareta...!”
Baiwar naci gaba da haki take fad’in “Ki gafarceni ya Shugabata wani labari nakeji na Yawo cikin Fada..!”
Raheema da ta kai matuk’a wajen tunzura da wannan baiwa, fincika tai Ta mik’e tsaye tana fad’in “Ke k’ask’antacciyar Baiwa wane labari ne zaisa ki fice hayyacinki haka.. Labari guda d’aya ke yawo cikin Fada, labarin Farin ciki... Labarin auren Gimbiya Raheema da Sarki Mahmood... Shi kad’aine labarin dake yawo cikin Fada..!!”
Baiwar na haki take girgiza kai....
Raheema da k’irjinta ke bugu batasan sanda ta damk’o wuyar Baiwar tana fad’in Ta sanar da ita labarin dake tafe da ita... Batakaiga rufe baki ba suka sinkayo sautin algaita na tashi ana ambato sunan Gimbiya Raheemah da angonta matsayin ma’arauta.....
*MUHIBBAH*
*61*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Raheemah bata daina jijjiga Baiwar nan tana mulke mata fuska da k’unshin dake hannunta ga algaita na kuma tashi duk ya karad’e cikin Masarautar.... Daidai nan Gimbiya Zeenat Ta shigo a fusace hankali tashe tana fad’in “Raheemah mai nake ji, Wai Yazeed aka aura miki ba Mahmood ba... Ta yaya wannan abu ya kasance...?!!”
Raheemah na kuka tamkar mai tab’in hankali duk ta shafe jikinta da k’unshin da ake zana mata tace “Aunty wllhi k’arya ne... Wanda suka Zo d’aura auren su sukayi munafunci, Aunty Mahmood na sona nayi imani yana sona bazai tab’a barina ma k’aninsa ba... Aunty dan Allah tun kafin su tafi ki taresu su warware wannan auren wasan da sukayi su maida aurena kan mijina Mahmood... Aunty I can’t lose Mahmood... Wayyo na shiga uku.... Dan Allah Ki fita ki taresu wllhi dariya za’a mana cikin Masarautar nan... Sanin kanki kishiyoyin Ummah bazasu barmu musha iska da habaici ba..!!”
Gimbiya Zeenat naci gaba da huci take furta “Ai duk laifinki ne... Ga irinta nan..! Ga irin ranar da nake jiye miki, kin maida kanki tamkar wata kariya... Na tabbata Mahmood yasan Keda d’anuwansa kunada alak’a a b’oye shiyasa ya juya akalar auren ya koma kan d’anuwansa... Ai abin kiyi Farin ciki ne yanzu sai kuyi mai dalili.!!!”
Raheemah ta katseta da fad’in “Aunty dan Allah kije ki tari Hakiman nan kar su fice a Masarautar nan... Mishkila aka samu Mahmood ne mijin ba Yazeed ba..!!” Ta k’arashe tana mai nufan k’ofa kai babu ko rufi tsaban ta shiga tashin hankali maras misaltuwa... Gimbiya Zeenat tabi bayanta a fujajan tana k’ok’arin dakatar da ita inaa Raheema bataji bata gani tuni Ta tsallake bene ta nufi dandatson jama’an dake haraban Masarautar....
Abinka da babban gida sai aka samu abinyi, bayi na k’usk’us ‘yan gida kaw masu jimami nayi masu dariya na yi...
Haka Raheema ta fice tana fad’iwa masu algaita su dakata... Ta kutsa sosai har gaban su Galadima tana fad’in wannan auren bai d’auru ba... Sarki Mahmood ne mijinta ba Yarima Yazeed ba..!
Galadima ya girgiza kai yace “Rankidad’e kaman yanda Sarki Mahmood ya umarta hakan mukayi... Yarima Yazeed shine mijinki ba Sarki Mahmood ba...!”
Raheema ta shiga fatali da kayan kid’e kid’e dake wajen tana fad’in k’arya ne wannan auren bai d’auru ba...!
Ala dole wasu bayi ‘yanmata guda hud’u suka kamata aka shige da ita cikin gida sai hauka take wanda hakan sosai ya zubda Martaban masarautarsu... ‘Yanuba kuwa suka sami abin goriwa Zeenat dan sun tabbata wannan abin kunya da Raheema tayi tsaf sai ya koma Masarautar da Gimbiya Zeenat ke aure... Haka Gimbiya Zeenat ta aje shagalin buki a gefe ta shiga rara kuka tana kaico, shikenan Sarautar da take hari ta hanyar auren Mahmood da k’anwarta zatayi ya tashi a aiki... Har abada bazata tab’a samun hakan ba, wannan abin kunya ma da Raheemah tayi bai k’aresu da komai ba face fad’a zubda mata jima da tayi... Yanzu ko nan cikin masarautarsu mahaifarta batada wani kima balle aje can masarautarsu mijinta... Sosai Gimbiya Zeenat Ke kuka tana nadaman abubuwan da tayi a baya... Kaicon son zuciya, yau ga yanda son zuciya ya kaita... Dama komai zakayi ka saka tsoron Allah a ciki idan kuwa ba haka ba sai Kaga ba daidai ba...!
**
Bakin Turaki ya gaza rufuwa, Mahmood ya shammacesa... Wato dama kansa ya nemawa auren Muhibbah... Gashi kuma ya karb’awa kansa auren nata ba tareda wakilcin kowa ba... Kai sai a gaisheda Mahmood inji Turaki..
Fataken Buzaye sun amshi auren Muhibbah yanda suka buk’aci a basu amaryarsu su tafi can k’asarsu da ita...
Yawale yace kar suji komai su taho da motar da sukayo haya su biyosa suje har yanda zasu d’auke amaryarsu... Ba tareda b’ata lokaci ba kuwa sukabi bayan Yawale dake bisa babur d’insa, nan take suka nufo gidansu Muhibbah...
Aka bar mutane da jimamin abunda ya faru da jinjina lamarin, wasu daga cikin Baffanin Ansar da suke Uba d’aya da mahaifinsa suka titsiye Yawale suna fad’in rashin kyautawar da yayi ace baka San mutane ba baka San daga yanda suke ba ka d’auki mutum sukutum ka basu...!
Yawale yace Babu ruwansu tunda ba ‘yarsu bace kuma Ansar shine kad’ai dolensa basu ba...! Haka dai Yawale yai masu d’add’aya ya barsu nan suna jimamin wannan abinda ya faru wanda saikace wani wasan kwaikwayo... Abinda suke ganina wasannin kwaikwayo da littafai sai gashi zahiri a gabansu....
Shidai Mahmood sai karantar Yawale kurum yake da idanu.... Suna isa unguwar Yawale yace suyi Parking daga can nesa za’a fito da ita... Turaki yai parking daga nesa kaman yanda Yawale ya buk’ata...
Nan take Baffah Yawale ya ciro wayarsa a aljihu ya kirawo Gudidi yace da ita masu d’aukan Amarya sun iso Ta fito da Amarya...
Gudidi tace an gama gasu nan fitowa.... Cikin sand’a don ko Mommy bataso ta ganta ta kirawo k’awarsu Salame tace ta taimaka mata su fito da Muhibbah tinda dama bacci take....
Salame dai tsoro saman fuskarta tabi bayan Gudidi suka shiga d’akin yanda Muhibbah Ke yashe tana bacci, tausayin Muhibbah ya kama Salame... Idanunta sukai rau rau tana dubanta.... Gudidi kaw ko a jikinta saima d’auko mayafi da tai Ta rufawa Muhibbar tana k’ok’arin mik’ar da ita tsaye....
Ta dubi Salame dake tsaye tana duban Muhibbah cikeda tausayawa kana taja tsuka a hankali tace “Toh Sarkin tausayi da imani, dramar ya k’are taimaka min zakiyi mu fitar da ita daga cikin gidan nan....!”
Salame Tai k’ok’arin maida k’wallan da suka ciko idanunta tace “Gudidi babu wanda yasan duniyar da za’a kai yarinyar nan... Babu wanda yasan su waye suka auri yarinyar nan..? Wasu irin mutane ne... Na gari ne ko na banza... ‘Yan shan jini ne koma matsafa ne... Gudidi baki tausayin yarinyar nan..? Baki tsoron hakki..!!”