Sashe 128
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Waziri da tuni ya ciro rawani ya nad’eta kan hannunsa, cikin rawar murya yake furta “Duk abinda Yarima Jafaru ya fad’i gaskiya ne babu k’arya ko d’aya cikinta..! Dashi da d’an uwansa Yarima Mahmooda Sune ‘ya’yan Sarauniya Turai kuma Giwar Amale ta asali..! Wacce kuka sani a matsayin Sarauniya Turai ba ta gaskiya bace... Hadimarta ce ta sace komai nata, ciki harda mijinta da kuma ‘ya’yanta guda biyu... Yarima Mahmood Ta maidasa nata don ta kashesa a gaba..! K’udirinta shine Bokanta ya sanar da ita cewa duk d’an Sarki da ya soma mulki zai mutu shiyasa Ta dage sai Yarima Mahmood ya soma hawa mulki..! Ta tilasta masa dawowa daga k’asar sifaniya Kawai domin Ta cika burinta akansa..! Shi kuma Ja’afaru Ta canzasa da d’an Bawa Almu, Ja’afaru d’an mai Martaba ne.. A lokacin da ta fahimci Ja’afaru ka iya sanin wani abu sai ta nemi rayuwar Jafaru wanda hakan ya sanyashi guduwa daga Masarautar..!”
Muryar shi na rawa yaci gaba da furta “Mun fahimci Mai Martaba yasan gaskiya duk abubuwan da suka faru dashi sabida wasik’a da muka tsinta wanda matar Mahmood Aliya Ta bar masa, cikin wasik’ar ba komai bane face duk wasu abubuwa da Giwa tayi wanda mahaifiyarta Ta sanar da ita a lokacin da tazo barin duniya..!”
Ya d’ago yana duban Mahmood wanda ya koma tamkar bashi a wajen kana yaci gaba da fad’in “Idan baka mance ba Rankaidad’e, ka kawo ziyara k’asar nan bada jimawa ba aka tura sak’on mutuwar mahaifinka..! A wannan kawo ziyarar da kayi a lokacin Aliya Ta rubuta wannan wasiya fa mai Martaba Wanda Mahaifiyarta da ta kasance Hadima ga mahaifiyarka Gimbiya Turai ta asali itace ta sanar da ita domin kuwa Mahaifiyar tata a gabata komai ya faru duk abubuwan da suka faru da Gimbiya da yanda aka salwantar da ‘ya’yanta...!”
Zuciyar Mahmood taci gaba da bugawa yana tuna tun bayan da suka kawo ziyarar da Waziri yake fad’i bai kuma gane kan Aliya ba har kawo zuwansu sanda Mai Martaba ya rasu wanda a lokacin itama aka tsinci gawarta a d’aki..! Ashe Giwa ce ta kasheta sabida tasan wani dark secret nata..!
Turaki dake jin abin kaman a shirin finafinai, saurin tsayawa a gefensa yayi dan yasan komai ka iya faruwa dudka k’arfin zuciya na abokin nasa..! Abu ne mai matuk’ar tayar da hankali komin k’arfin hali da mutum yakedashi..! Ta yaya za’ace matar da ka girma ka santa matsayin mahaifiya k’arya ta jima tana shera maka tsawon rayuwarka...! Babu komai cikin Rayuwar face k’Arya da zalunci..!! Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..!!
Muryar Waziri ya sinkaya yana mai ci gaba da furta “A lokacin da kuka Zo k’asar sanda mahaifinka Sarki ya rasu a lokacin Giwa Ta fahimci cewa matarka Aliya ita ta sanar da Mai Martaba ta hanyar ajiye masa wasik’a.. Kuma kaima zata iya sanar dakai shiyasa ta kasheta..!!”
Baikai aya ba yaji sauk’an naushi ta ko ta ina Yazeed dake tsananin kuka yana naushinsa da duka k’afafunsa yake furta “K’arya kake..! Mahaifiyata itace Gimbiya Turai..! K’arya kake Mahaifiyata Gimbiya ce kuma sarauniya ce..!!! Ka bud’e baki kace k’Arya kake Waziri..! Har abada bazan tab’a zama jinin Bauta ba..! K’arya kake Waziri..!!”
Waziri na hawaye yake furta “Gaskiyar kenan Yazeed Mahaifiyarka Baiwa ce datayi k’wace da fin k’arfiwa Uwargijiyarta wacce ta aminta da ita bata kuma nufeta da komai ba face alkhairi..! Mahaifiyarka butulu ce mai saka alkhairi da sharri..!!”
Yazeed dake cazgan kuka ya kuma kai masa naushi yana furta “K’arya kake mak’aryaci..! Babu wanda zai yarda da kalamanka sabida kaid’in maci amana ne kuma mayaudari..! Kaci amanan abokinka Sarki AbdulJabbar ka nemi Mahaifiyata da aurensa akanta.. Wazai yarda da kalamanka..!!”
Cikin kuka Waziri ya katsesa da fad’in “Banci amanan Abokina ba..! Mahaifiyarka babu aurensa akanta, bai aureta ba makircinta kawai tayi Ta rabasa da matarsa da ‘ya’yansa Ta haukatar da ita.. Kai a Naka tunanin Yazeed matar Sarki zatabi wani namijin ne..! Mahaifiyarka ba matar Sarki bace Baiwa ce k’ask’antacciya wacce ni nai mata sutura cikin Masarautar nan har Ta haifoka gudan jinina Ta kuma dangantaka ga Sarki AbdulJabbar..! Badon ni ba da bata haifoka ma Sarki ba..!!”
Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..! Wad’annan bayin Allah haka sukayita kwance ma kansu zannuwa a kasuwa, sunzo wajen domin su kwancewa Mahmood zani a kasuwa su sanyashi yaji kunyar duniya sai gashi reshe ta juya da mujiya sai bankad’o asirai suke Wanda suka jima a bisne babu wanda yasan dasu saiko su sai mahaliccinsu... wannan rayuwa da mai yayi kama..! Shuka kirki domin ka girba gobenka..!!
Haka aka dinga silalewa a wajen cikeda wane irin Al’ajabi, Yazeed bai daina naushin Waziri yana fad’in har abada bazai tab’a zama mahaifinsa ba shid’in d’an Sarki AbdulJabbar ne..!
Raheemah da Gimbiya Zeenat sukaga tashin hankalin da yafi k’arfinsu, sosai Raheema Ke kuka tana fad’in Ta cuci kanta ta zalunci kanta, Tabbas Zina babban laifi ne wanda tin daga duniya zai kaika ga k’ask’anci, dukda kasancewarta d’iyar masu mulki gashi zina ya janyo mata Ta auri mutumin da aka haifesa ba Ta hanyar aure ba sannan kuma ba d’an sarauta ba d’an k’ask’antacciyar Baiwa maciya amana..! Laifin zina duk shine ya janyo mata wannan k’ask’anci da tozarci a rayuwa, yau ko da wanann tashin hankali aka barta tana cikin tsaka mai wuya, a duniya kenan balle ka isa masauk’i na har abada lahira..! Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..! Ya Allah kai mana katangar k’arfe da manyan alkaba’irai harma da k’ananan wanda bazasu kai mutum ga komai ba face halak’a..!
Ja’afar ya isa gaban Yazeed da Waziri yanda suke zube a k’asa Yazeed na kuma tsinewa mahaifinsa Waziri albarka su duka biyun suna kuka suna nadamar rayuwa..!
Ja’afar ya dubesu gaba d’aya sai kuma ya dubi Waziri yace “Dukda laifukan da ka aikata bazanso asirinka ya bankad’u haka a idon duniyaba amma saidai ka sani daga cikin sharrin zina da illolin Sa yana janyo jin kunya da zubar da mutunci tin daga duniya har izuwa lahira..! Da wannan kawai aka barka ya isheka hukuncin duniya Waziri..
Ya kuma maida dubansaga Yazeed yace “Toh Yarima Yazeed ko ince Bawa d’an Baiwa Yazeed..! K’arshen tikatiki tik Inji masu iya magana..! Yau gaka nan a k’asa dani kana duk’e gabana, babu hannuwa babu mulki babu sarauta babu asali balle Tushe..! Babu babunka sunyi yawa Yazeed..! Ka sani Allah shi yake bada mulki ga wanda yaso ya kuma hana wanda yaso..! Bayan duk kalan abubuwan da mahaifiyarka ta aikata dan ta tarwatsa mahaifiyarmu da zuri’arta tayi iya k’ok’arinta wajen ganin Ta fitar dani da d’an uwana daga gidan mahaifinmu da sarautar da take gadonmu ne yau gashi nata ahalin sune suka tozarta..! Babu komai a cikin tsananin son mulki face halak’a..!”
Ya d’an tsagaita sai ya kuma duk’awa saitin kunnen Yazeed yake furta “Kai k’ask’antacce Bawa, namu dakai bata k’are ba bari duk wata k’ura Ta lafa..! Yarima zai kuma waiwayanka..!!” Ya k’arashe yana mai sakin murmushi saman fuskar Yazeed dake zuban hawaye..!
Ya dubi Waziri a hankali yace “Baba Kwarto ashe anko kukayi da d’an Naka shima d’in wani k’Aton Kwarto ne mai danne ‘ya’yan mutane aje gida a masa tarbiya akwai ‘ya’yan bayi cikin Masarautar nan, Masarautar bazata lamunci mummunan d’abi’a irin wannan daga d’aya cikin Bayinta ba..!” Ya k’arashe yana mai had’e girnsa had’ida tsimewa sosai wanda tuni yasa Waziri soma jinjina kai yana mai ci gaba da matsan k’walla..!
Ya mik’e yana gyara rigarsa Ta sarauta had’ida daidaita tsayuwarsa...
Har ya soma tafiya ya juyo ya dubi Dakarun dake gefe yace su kame Waziri su rufe a nan fursunan cikin Masarauta dan sai yazo ya sanar dashi yanda akai ya kashe mahaifinsa Sarki in details..!
Dakaru suka risina suna furta “An gama Rankaidad’e Yarima..!!”
Suka k’arashe suna masu tattaro Waziri dake faman magiya yana Baiwa Yarima Ja’afar hak’uri...
Yazeed dake duk’e wajen bayan Ja’afar yabi da kallo Hawaye na kuma gangaro masa yana tuna babu irin cin kashin da baiyiwa Ja’afar d’in ba a matsayinsa na d’an Sarki wanda Ja’afar d’in Ke k’asansa, yau sai gashi Wai Ja’afar shine a sama dashi shine suka canza title shi ya koma Bawa wanda yake k’asa da J’afar yayinda Ja’afar d’in ya Koma jinin Saraki wanda yake sama dashi..! Da rarrafe Yazeed yake k’ok’arin mik’ewa yana huci yana dararawa bayin dake tsaye wajen suna kallonsa tsawa..!
Bawa guda ya bud’e murya yace “Kai billahillazim idan ka kuma zaginmu zakaji a jikinka dan damu da kai babu banbanci, kai gwara mu ma da aure aka haifo mu..! Duk fad’in Masarautar nan babu wulak’antaccen Bawa irinka dan haka kana kuma cewa fit wllhi zamu tara maka na gajiyya mu k’arasa karya sauran k’afafunka..! Tashi ka b’ace mana a nan kafin mu k’arasa ka..!!”
Yazeed ya soma jada baya ganin gungun bayin na yunk’urin nufosa..! Cikin wane irin tashin hankali ya nufi b’angarensa wanda bai tab’a tsintar kansa ciki ba tsawon rayuwarsa..!
**
Zahra da har wannan lokaci bata dawo hayyacinta ba kwance take zazzabi na neman rufeta, Umaima wacce itama k’arfin hali kurum take itace a gefen Zahran tana kula da ita.. Bacci har ya soma d’aikam Zahra Ta farka a firgice tana ambaton sunan Muhibbah da k’arfin gaske, mafarki take Jamal na binsu itada Muhibbah, suna gudu ya kama Muhibbah dake ambata mata sunan takarda da yaren Spanish..!
Take ta nanata sunan takardan a fili “Papel..!!” Ta shiga tuno kalaman Muhibbah a gareta cewa Ta baiwa Paa d’inta Takardun data d’auka cikin rigarta..!
Babu shiri Zahra Ta zira hannu cikin rigarta Ta ciro takardun wanda har sun soma d’an diddigewa sabida damshin ruwa da ya tab’a su...
Juya takardun ta shigayi tana duban Umaima take fad’in “Paa..! I need to give this to Paa..! I need to go Paa right now..!!” Bata kuma tsayawa sauraren Umaima ba Ta fice a guje tana neman Mahaifinta, Umaima na d’ingisawa take k’ok’arin bin bayanta saidai bazata iya ba sabida gurd’a mata k’afa da Jamal sabida d’aureta da yayi Ta jima a d’aure.. Haka Ta koma ta zauna da k’yar tana kame k’afarta...
Zahra kaw tuni ta fantsama Masarauta a guje...!
**
Muryar shi na rawa yaci gaba da furta “Mun fahimci Mai Martaba yasan gaskiya duk abubuwan da suka faru dashi sabida wasik’a da muka tsinta wanda matar Mahmood Aliya Ta bar masa, cikin wasik’ar ba komai bane face duk wasu abubuwa da Giwa tayi wanda mahaifiyarta Ta sanar da ita a lokacin da tazo barin duniya..!”
Ya d’ago yana duban Mahmood wanda ya koma tamkar bashi a wajen kana yaci gaba da fad’in “Idan baka mance ba Rankaidad’e, ka kawo ziyara k’asar nan bada jimawa ba aka tura sak’on mutuwar mahaifinka..! A wannan kawo ziyarar da kayi a lokacin Aliya Ta rubuta wannan wasiya fa mai Martaba Wanda Mahaifiyarta da ta kasance Hadima ga mahaifiyarka Gimbiya Turai ta asali itace ta sanar da ita domin kuwa Mahaifiyar tata a gabata komai ya faru duk abubuwan da suka faru da Gimbiya da yanda aka salwantar da ‘ya’yanta...!”
Zuciyar Mahmood taci gaba da bugawa yana tuna tun bayan da suka kawo ziyarar da Waziri yake fad’i bai kuma gane kan Aliya ba har kawo zuwansu sanda Mai Martaba ya rasu wanda a lokacin itama aka tsinci gawarta a d’aki..! Ashe Giwa ce ta kasheta sabida tasan wani dark secret nata..!
Turaki dake jin abin kaman a shirin finafinai, saurin tsayawa a gefensa yayi dan yasan komai ka iya faruwa dudka k’arfin zuciya na abokin nasa..! Abu ne mai matuk’ar tayar da hankali komin k’arfin hali da mutum yakedashi..! Ta yaya za’ace matar da ka girma ka santa matsayin mahaifiya k’arya ta jima tana shera maka tsawon rayuwarka...! Babu komai cikin Rayuwar face k’Arya da zalunci..!! Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..!!
Muryar Waziri ya sinkaya yana mai ci gaba da furta “A lokacin da kuka Zo k’asar sanda mahaifinka Sarki ya rasu a lokacin Giwa Ta fahimci cewa matarka Aliya ita ta sanar da Mai Martaba ta hanyar ajiye masa wasik’a.. Kuma kaima zata iya sanar dakai shiyasa ta kasheta..!!”
Baikai aya ba yaji sauk’an naushi ta ko ta ina Yazeed dake tsananin kuka yana naushinsa da duka k’afafunsa yake furta “K’arya kake..! Mahaifiyata itace Gimbiya Turai..! K’arya kake Mahaifiyata Gimbiya ce kuma sarauniya ce..!!! Ka bud’e baki kace k’Arya kake Waziri..! Har abada bazan tab’a zama jinin Bauta ba..! K’arya kake Waziri..!!”
Waziri na hawaye yake furta “Gaskiyar kenan Yazeed Mahaifiyarka Baiwa ce datayi k’wace da fin k’arfiwa Uwargijiyarta wacce ta aminta da ita bata kuma nufeta da komai ba face alkhairi..! Mahaifiyarka butulu ce mai saka alkhairi da sharri..!!”
Yazeed dake cazgan kuka ya kuma kai masa naushi yana furta “K’arya kake mak’aryaci..! Babu wanda zai yarda da kalamanka sabida kaid’in maci amana ne kuma mayaudari..! Kaci amanan abokinka Sarki AbdulJabbar ka nemi Mahaifiyata da aurensa akanta.. Wazai yarda da kalamanka..!!”
Cikin kuka Waziri ya katsesa da fad’in “Banci amanan Abokina ba..! Mahaifiyarka babu aurensa akanta, bai aureta ba makircinta kawai tayi Ta rabasa da matarsa da ‘ya’yansa Ta haukatar da ita.. Kai a Naka tunanin Yazeed matar Sarki zatabi wani namijin ne..! Mahaifiyarka ba matar Sarki bace Baiwa ce k’ask’antacciya wacce ni nai mata sutura cikin Masarautar nan har Ta haifoka gudan jinina Ta kuma dangantaka ga Sarki AbdulJabbar..! Badon ni ba da bata haifoka ma Sarki ba..!!”
Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..! Wad’annan bayin Allah haka sukayita kwance ma kansu zannuwa a kasuwa, sunzo wajen domin su kwancewa Mahmood zani a kasuwa su sanyashi yaji kunyar duniya sai gashi reshe ta juya da mujiya sai bankad’o asirai suke Wanda suka jima a bisne babu wanda yasan dasu saiko su sai mahaliccinsu... wannan rayuwa da mai yayi kama..! Shuka kirki domin ka girba gobenka..!!
Haka aka dinga silalewa a wajen cikeda wane irin Al’ajabi, Yazeed bai daina naushin Waziri yana fad’in har abada bazai tab’a zama mahaifinsa ba shid’in d’an Sarki AbdulJabbar ne..!
Raheemah da Gimbiya Zeenat sukaga tashin hankalin da yafi k’arfinsu, sosai Raheema Ke kuka tana fad’in Ta cuci kanta ta zalunci kanta, Tabbas Zina babban laifi ne wanda tin daga duniya zai kaika ga k’ask’anci, dukda kasancewarta d’iyar masu mulki gashi zina ya janyo mata Ta auri mutumin da aka haifesa ba Ta hanyar aure ba sannan kuma ba d’an sarauta ba d’an k’ask’antacciyar Baiwa maciya amana..! Laifin zina duk shine ya janyo mata wannan k’ask’anci da tozarci a rayuwa, yau ko da wanann tashin hankali aka barta tana cikin tsaka mai wuya, a duniya kenan balle ka isa masauk’i na har abada lahira..! Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..! Ya Allah kai mana katangar k’arfe da manyan alkaba’irai harma da k’ananan wanda bazasu kai mutum ga komai ba face halak’a..!
Ja’afar ya isa gaban Yazeed da Waziri yanda suke zube a k’asa Yazeed na kuma tsinewa mahaifinsa Waziri albarka su duka biyun suna kuka suna nadamar rayuwa..!
Ja’afar ya dubesu gaba d’aya sai kuma ya dubi Waziri yace “Dukda laifukan da ka aikata bazanso asirinka ya bankad’u haka a idon duniyaba amma saidai ka sani daga cikin sharrin zina da illolin Sa yana janyo jin kunya da zubar da mutunci tin daga duniya har izuwa lahira..! Da wannan kawai aka barka ya isheka hukuncin duniya Waziri..
Ya kuma maida dubansaga Yazeed yace “Toh Yarima Yazeed ko ince Bawa d’an Baiwa Yazeed..! K’arshen tikatiki tik Inji masu iya magana..! Yau gaka nan a k’asa dani kana duk’e gabana, babu hannuwa babu mulki babu sarauta babu asali balle Tushe..! Babu babunka sunyi yawa Yazeed..! Ka sani Allah shi yake bada mulki ga wanda yaso ya kuma hana wanda yaso..! Bayan duk kalan abubuwan da mahaifiyarka ta aikata dan ta tarwatsa mahaifiyarmu da zuri’arta tayi iya k’ok’arinta wajen ganin Ta fitar dani da d’an uwana daga gidan mahaifinmu da sarautar da take gadonmu ne yau gashi nata ahalin sune suka tozarta..! Babu komai a cikin tsananin son mulki face halak’a..!”
Ya d’an tsagaita sai ya kuma duk’awa saitin kunnen Yazeed yake furta “Kai k’ask’antacce Bawa, namu dakai bata k’are ba bari duk wata k’ura Ta lafa..! Yarima zai kuma waiwayanka..!!” Ya k’arashe yana mai sakin murmushi saman fuskar Yazeed dake zuban hawaye..!
Ya dubi Waziri a hankali yace “Baba Kwarto ashe anko kukayi da d’an Naka shima d’in wani k’Aton Kwarto ne mai danne ‘ya’yan mutane aje gida a masa tarbiya akwai ‘ya’yan bayi cikin Masarautar nan, Masarautar bazata lamunci mummunan d’abi’a irin wannan daga d’aya cikin Bayinta ba..!” Ya k’arashe yana mai had’e girnsa had’ida tsimewa sosai wanda tuni yasa Waziri soma jinjina kai yana mai ci gaba da matsan k’walla..!
Ya mik’e yana gyara rigarsa Ta sarauta had’ida daidaita tsayuwarsa...
Har ya soma tafiya ya juyo ya dubi Dakarun dake gefe yace su kame Waziri su rufe a nan fursunan cikin Masarauta dan sai yazo ya sanar dashi yanda akai ya kashe mahaifinsa Sarki in details..!
Dakaru suka risina suna furta “An gama Rankaidad’e Yarima..!!”
Suka k’arashe suna masu tattaro Waziri dake faman magiya yana Baiwa Yarima Ja’afar hak’uri...
Yazeed dake duk’e wajen bayan Ja’afar yabi da kallo Hawaye na kuma gangaro masa yana tuna babu irin cin kashin da baiyiwa Ja’afar d’in ba a matsayinsa na d’an Sarki wanda Ja’afar d’in Ke k’asansa, yau sai gashi Wai Ja’afar shine a sama dashi shine suka canza title shi ya koma Bawa wanda yake k’asa da J’afar yayinda Ja’afar d’in ya Koma jinin Saraki wanda yake sama dashi..! Da rarrafe Yazeed yake k’ok’arin mik’ewa yana huci yana dararawa bayin dake tsaye wajen suna kallonsa tsawa..!
Bawa guda ya bud’e murya yace “Kai billahillazim idan ka kuma zaginmu zakaji a jikinka dan damu da kai babu banbanci, kai gwara mu ma da aure aka haifo mu..! Duk fad’in Masarautar nan babu wulak’antaccen Bawa irinka dan haka kana kuma cewa fit wllhi zamu tara maka na gajiyya mu k’arasa karya sauran k’afafunka..! Tashi ka b’ace mana a nan kafin mu k’arasa ka..!!”
Yazeed ya soma jada baya ganin gungun bayin na yunk’urin nufosa..! Cikin wane irin tashin hankali ya nufi b’angarensa wanda bai tab’a tsintar kansa ciki ba tsawon rayuwarsa..!
**
Zahra da har wannan lokaci bata dawo hayyacinta ba kwance take zazzabi na neman rufeta, Umaima wacce itama k’arfin hali kurum take itace a gefen Zahran tana kula da ita.. Bacci har ya soma d’aikam Zahra Ta farka a firgice tana ambaton sunan Muhibbah da k’arfin gaske, mafarki take Jamal na binsu itada Muhibbah, suna gudu ya kama Muhibbah dake ambata mata sunan takarda da yaren Spanish..!
Take ta nanata sunan takardan a fili “Papel..!!” Ta shiga tuno kalaman Muhibbah a gareta cewa Ta baiwa Paa d’inta Takardun data d’auka cikin rigarta..!
Babu shiri Zahra Ta zira hannu cikin rigarta Ta ciro takardun wanda har sun soma d’an diddigewa sabida damshin ruwa da ya tab’a su...
Juya takardun ta shigayi tana duban Umaima take fad’in “Paa..! I need to give this to Paa..! I need to go Paa right now..!!” Bata kuma tsayawa sauraren Umaima ba Ta fice a guje tana neman Mahaifinta, Umaima na d’ingisawa take k’ok’arin bin bayanta saidai bazata iya ba sabida gurd’a mata k’afa da Jamal sabida d’aureta da yayi Ta jima a d’aure.. Haka Ta koma ta zauna da k’yar tana kame k’afarta...
Zahra kaw tuni ta fantsama Masarauta a guje...!
**