← Book details Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 162

Sashe 33

Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hankali tashe Giwa Ke fad’in “Ke Jakadiya Ki natsu Ki sanar dani abindake tafe dake cikin daren nan... Bana san shashanci da hauka...!”

Jakadiya na sauk’e haki take fad’in “Allah shi baki yawan rai Ina tinanin Izzatu ce ta bayyana dan ga Yarima Mahmood ya cika Fada da dakarai, ga dukkan alamu Masarautar babu lafia...!”

Giwa ta isa jikin window ta yaye labule nan ta hangi dogarai sai kaiwa da komowa suke... Juyowa tai tana duban Jakadiya kana tace “Kin tabbata Izzatu ce ta bayyana... Ko kuwa wani abinne daban...?!”

“Allah shi taimakeki idan ba Izzatu ce ta bayyana ba maizaisa Dakarai su bazama cikin masarauta...?!”

Giwa ta girgiza kai tana mai furta “Sam hakan bamai yuwa bane Jakadiya... Sanin kanki ne bayyanar matar nan na nufin tashin hankalinmu ne...Ina Ubandoma...?”

Jakadiya batakaiga bata amsa ba Jamal ya shigo yana tambayan Jakadiya abinda Ke faruwa cikin Masarautar nasu dan yaga Dakarai ta ko wani angle....

Jakadiya ta basa amsa da fad’in “Allah shi taimaki Gwarzon Giwa, ai Ina tsammanin cikin Fada ne Babu lafia...!”

Yarima Jamal ya jinjina kansa kad’an kana ya dubi mahaifiyarsa yace “Maami are you alright..?!”
Ta jinjina masa kai alamun lafia take... Lokaci guda Jamal ya nufi k’ofa yana fad’in bari ya duba meke faruwa cikin Masarautar....

Jinjina masa kai kurum Giwa tai ba tareda ta iya basa amsa ba... Yana ficewa Ta kuma duban Jakadiya kana tace “Maza kije ki nemi Ubandoma yanda ya shiga ya fita kiji abindake wakana cikin Masarautar sannan ki tabbata Mahmood baiga Izzatu ba....!!”

Jakadiya ta jinjina kai tana mai amsa mata kana Ta fice cikin sauri... Ta bar Giwa nan d’aki sai kaiwa da komowa take, ga hannunta dake rufe cikin safa sai mintsilinta yake a hankali, wannan alamace na cewa shirinta na iya backfiring d’inta kaman yanda Tal’udu yasha sanar da ita.... Sosai Ta matse hannun tana huci take furta “Turai nake, murucin kan Dutse ban fito ba saida na shirya, kayi kad’an Mahmood iyayenka ma sunyi kad’an... Na kassarasu balle kai... Na d’aid’aita ahalinka, kaid’in kayi kad’an kace zakajada Giwa.....!!”
Tana ida fad’in haka ta d’an zame safar hannun nata... Gabanta ya yanke ya fad’i ganin Yana nan a halittansa na launin bak’i... Tai saurin maida safar ta rufe kana takai dubanta ga d’aya hannun nata dake sarari shi d’in fari ne tas gwanin ban sha’awa.... A hankali ta fuzar da fuci tana jiran taji da mai Jakadiya zatazo mata....

A kusan k’ofan bayi Jakadiya ta had’uda Ubandoma... Ta d’an murmusa kad’an kana tace “Wai fushi kake dani har yanzu, kaima kasan bayin kaina bane.. Ya na ita da umarnin Giwa...”

Ubandoma ya kuma watsa mata harara kana yace “Wannan hannu naki da ya jeme ya sud’e dan bauta ba dole naji marin nan ba, har yanzu Jakadiya jinyar k’uncina nake...!”

Dariya yaso kubcewa Jakadiya, Ta d’anyi kad’an kana tace “Yanzu dai ba wannan ba, Giwa ce ta aikoni dan sanin meke wakana cikin Masarauta... Ko Izzatu ce ta bayyana...?!”

Ubandoma ya watsa mata muguwar kallo kana yace “Banda k’ask’anci da tozarci a rasa waye zai mareni sai Baiwa gajiyayya...!”

Jakadiya ta kastesa da fad’in “Kai Ubandoma... Zaka amsa tambayar Uwargijiyarka ce kokuwa wani marin kake so ka sake amsa...?!”

Ubandoma ya sab’a babban riga yana mai kad’a Kai cikeda takaici kana yace “Wannan karon kam saidai kece zaki amsa marin dan kin sanar da Giwa abinda ba haka ba... Take ya sanar da Jakadiya abindake wakana cikin Masarautar da kuma yanda Yarima Mahmood ya bada umarnin binciko wannan mutumin cikin gaggawa... Babu b’ata lokaci Jakadiya ta shige Kai sak’owa shugabanta...
**

A babban haraban Masarautar Jamal ya tadda Mahmood, ya k’arasa gareshi suka gaisa yana tambayansa ko wani abu ne Ke wakana cikin Masarautar...
Mahmood ya sanar dashi abindake faruwa... A tare Mahmood da Jamal suka ci gaba da gudanar da binciken mutumin da aka gani cikin Masarautar wanda ba’a ita identifying kamanninsa ba sabida shiga Ta bak’ak’en tufafi da yakeyi... Haka nan suka umarta Dakarai da aci gaba da searching cikin Fada har zuwa wayewan gari don Mahmood ya tabbatar mutumin cikin Masarautar yake, babu yanda za’ai ace shigowa yai bayan irin tsaron dake a cikin Masarautar... Haka sukaita bincike har kusan asubahi babu wannan mutumi babu dalilinsa...

Yarima Mahmood ya d’an dafa kafad’ar Jamal kana yace “Kaje ka huta k’anina...!”

Jamal ya girgiza kai cikeda kulawa kana yace “A’a Yaya, bazan tafi na Barka kai kad’ai a nan ba... Kar ka damu dani, lafia lou nake..!” Ya k’arashe cikeda kulawa...

K’uri Mahmood yai masa kana ya jinjina kai a hankali alamun gamsuwa... Suna nan tsaye a wajen Sport car d’in Yazeed k’irar Lamborghini ta kutso Kai cikin masarautar... Suka bi motar da kallo har ya k’araso ya shige sashensa ... Girgiza kai kad’an Mahmood yai yana duba lokaci a wayar salulansa....

Jamal ya d’an kai dubansaga Mahmood d’in kana yai gyaran murya kad’an “Yaya ko zaka koma cikin gida ka huta, ka barni in charge zan kula da komai...!”

Baice komai ba sai sa kai da yai ya nufi sashen Yazeed... Ya tadda Yazeed d’in ya fito daga mota...
Kallo d’aya Yazeed yai masa ya watsar.... Ko a jikinsa ya nufi cikin gidan... Mahmood ya bud’e murya kad’an ya kirawo sunansa....

Cak ya tsaya ba tareda ya juyo ba...
Yarima Mahmood yaci gaba da takowa har ya k’araso kusan Yazeed d’in....

“Yazeed kakuwa San yanzu k’arfe nawa ne..?!” Ya tambaya yana duban Yazeed d’in...

Sai sannan Yazeed ya kaikaito yanaima d’an uwan masa wani irin duba... “Na sani... Why...Do you’ve problem with that...?!” Ya fad’i cikeda gadara ga tangad’i da yake alamun giyar bata sakeshiba dikda k’ok’ari da yake kar a gane a buge yake....

Mahmood ya girgiza kai a hankali kana yace “Yazeed mai ka d’auki rayuwar nan ne... Yazeed mata da giya duka biyu ka had’a...? Yazeed I thought ka canza, I thought ka aje duka wad’annan d’abi’un tuntuni.... Yazeed mai kake son maida rayuwarka data iyalanka...? A haka ne kake so ka zamto Shugaba a Masarautar nan...? Kana dawowa cikin Fada tsakar dare kuma a d’auke..? Wannan shine misalin dake so ka bayar a mulkin ka... Wannan shine misalin da kakeso ka baiwa yaranka...”

Katsesa Yazeed yai da fad’in “Cut the lecture please Yaya... Will you..?”
Lokaci guda yaci gaba da fad’in “Why do you even care.. Rayuwatace nayi yanda nake so da ita... Kuma wannan bashi zai hanani zamtowa Sarki na gaba ba... Wllhi kaji na rantse maka da Sarkin dake busan numfashi akan sarautar nan zan iya aiwatar da komai... Ko mene shi, and just so you know, I won’t hesitate to run over who ever gets in my way...!!” Yana k’arasa fad’in haka yasa kai ya shige yana mai ci gaba da tangad’i...

Fu’ad dake tsaye daga bayansu cikin sanyin jiki ya k’araso ga Mahmood...
“Yaya good evening...!” Ya fad’i yana d’an shafa sumarsa....

Mahmood ya dubesa da mamaki kana yace “Bakai bacci ba Fu’ad.... Mai kakeyi a nan...?!”

D’an shafa kansa Fu’ad ya kuma kana yace “Na farka ne Yaya sai nakeji kaman cikin Masarautar babu lafia... Can I be at any help..?”

Mahmood ya jinjina kansa a hankali kana yace “Is ok karka damu, ba wani abun damuwa bane... Guards are already taking care of the situation..!”

Fu’ad ya jinjina kai cikeda k’aunan d’an uwan nasa, Mahmood d’in ma murmushi ya saki masa kad’an yana mai d’an buga kafad’an Fu’ad yake tambayarsa ya yake Kwana biyun.... A haka suka jera gwanin ban sha’awa suka ratsa cikin Masarautar...
A haka suka k’araso suka tadda Jamal yanda yake ci gaba da umartan dakarun tsaron cikin gidan....

Jamal na hangosu ya k’araso yana tambayarsu ko akwai abinda ya canza... Yarima Mahmood ya girgiza masa kai a hankali alamun babu...
Gyaran murya kad’an Jamal yai kana yace “Yaya maybe idonka ne ya gane maka wannan mutumin, maybe wani ka gani cikin dakarun gidan nan kai tinanin ko wani daban ne ko wani mugu ne... Yaya I’m sure babu wanda zai iya haye manyan ginin Masarautar nan ya shigo kokuma ya tsallake dika Jami’an tsaron dake cikin gidan nan... I think babu kowa kaman yanda muke tinani....!” Ya k’arashe cikeda kulawa...

Fu’ad ya jinjina kai yana mai furta “I agree with Jamal Yaya... Maybe wani ka gani cikin dakaru...!”

D’an jim Yarima Mahmood yai kana ya jinjina kai yana mai fuzar da fuci a hankali “You’ve a point... But I’m sure naga mutum cikin bak’ak’en tufafi, sannan zuciyata bai kwanta da ganin wannan mutumin ba.. Na soma binshi sai naga tafiyar tasa kaman gudu gudu ne...! But is okay, let’s not think of the worse...”

Fu’ad ya jinjina kai alamun gamsuwa kana Jamal yace “I’ll check on Maami...”
Jinjina masa kai sukai a tare kana ya shige Mahmood da Fu’ad ma sukai ma juna sallama kowa ya nufi b’angarensa...

***

Sosai hankalin Giwa ya kwanta jin ba Izzatu bace Ta bayyana kaman yanda Jakadiya tazo mata da batun daga fari...
Washe gari sassafe sukai shirin zuwa ganin Izzatu itada Jakadiya...
Kasancewar Giwa takan fita rangadi a Masarautar yasa sam bazakai zaton wani mugun nufi ne da ita ba.... Dik yanda ta shige bayi sai Sun risina suna kwasan gaisuwa... Jakadiya Ke amsa masu...

Muhibbah da tin fitowarsu take biyedasu ba tareda sunyi noticing d’inta ba tana ganin sun nufi wata k’ofa daga cen b’angaren hagu dake gabashin Masarautar taji gaba d’aya jikinta bai aminta da yanda suke zuwa ba....

Mak’alewa tai jikin dogon gini tana mai sauk’e ajiyan zuciya a hankali, lokaci guda take k’arfafawa kanta gwiwa, zuciyarta na ayyana mata cewa zaki iya Saudatu... Zaki iya...
Lokaci guda taji wane irin k’warin gwiwa na zuwa mata... Abinka da gida na sarauta Kuyangi dik sabgogin gabansu suke babu mai noticing d’inta musamman dashike itama d’in shiga irinta mulki tai dan haka babu wanda zai kawo wani zargi ko shakku da kokonto a gameda ita....
Chapter 33 · 0% Book details