Sashe 119
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Ta d’an dubeni kad’an sai kuma tace “Ummah ta batada lafiya, ta kusa haifa min k’aramin k’ani bazata jure fitowa kasuwa ba..!”
“Na jinjina kai nace toh inane gidanku..?! Daga yanda muke tsaye tamin nuni da wani gida can da yake arewa da yanda muke tsaye, gidan shi kad’ai ne a wajen tol ko mak’ota basu dashi..! Na jinjina kai nace ni kuma cikin Masarauta ne gidanmu kuma sunana Ja’afar...! Ni ba mugu bane kaman yanda kikayi zato, kiyi hak’uri da zubar miki kayan miya da nayi..! Wani ikon Allah sai gani nayi ta murmusa tace “Shikenan Babu komai nima kayi hak’uri da zubar maka harawarka da nayi..!”
“Na kuma murmusawa Ina dubanta sai kuma nace “Basai kin bani hak’uri ba ni na hak’ura... Ki tafi gida kar a soma nemanki..! Ki wuce har ki shige gida ina kallonki bazan bari wani ya cutar dake ba..! Ta murmusa tace min na gode, zan iya kiranka Yaya Ja’afar tunda banida kowa a garin nan kuma ba’a barina na fita ko ina sai kasuwa kasuwan ma sai ranakun sati..!”
“Na kuma murmusawa nace “Toh ai ban wani girmeki sosai ba ni kar ki tsufar dani ki kirani Yaya..! Ta kuma murmusawa tace “Amma ai ka girmeni, kuma nasan k’anwarka ce tsarata kaga ni banida wani Yaya banida kowa sai Ummah na da Abbah na saiko k’aramin k’anin da zata haifo min..!”
“Tayi maganan cikeda yarinta, na murmusa nace “Toh shikenan tinda bakida Yaya Ki kirani Yaya nima tinda banida k’anwa kin zamto k’anwata...Hakan yayi miki..!?”
“Ta jinjina kai tana kuma murmusawa tace yayi min.. Yaya Ja’afar..! Daga haka d’aga min hannu tayi ta shige tana waigowa har ta kusan isa gida Ina nan tsaye Ina dubanta, sai kuma na dakatar da ita nace “Gashi kuma Yaya baisan sunan k’awarsa ba har zata shige..!” Ta murmusa kad’an tace “Sunana SAUDATU..!”
“Na jinina kai nace “K’anwata Saudatu..! Tai gajeren murmushi Ta kuma d’ago min hannu tace sai anjima...! Har saida naga shigarta gida kafin nasa kai nima na d’auki ciyawata na shige...! Toh tin daga wanann lokacin Sabo ya shiga tsakaninmu da Saudatu, nakan mata rakiya har zuwa gida, a haka bukin sallah ya k’arato na kula tana son zuwa taga hawan Dawakai amma baza’a barta ba a gida tinda ba’a barinta taje ko ina... Nayita bata labarin yanda hawan bukin sallah yake kasancewa, sosai yake sakata nishad’i yanda kasan ta had’a jini da sarauta... Kullum bata da labari da ya wuce na Dawakai da gidan sarauta... Tace min tana son ta shigo Masarautar nan wata ran taga yanda ginin gidan sarauta yake.. sabida idan tanama Abbanta labarin sarauta da abinda ya shafi gidan sarauta sai yayita mata fad’a yace koda wasa babu abinda ya had’ata da sarauta, babu komai cikin gidan sarauta sai zalunci... Dukda kuwa tsananin son kasancewa gidan sarauta da Saudatu keyi... Wata Rana Nace ta biyoni na shiga da ita taga yanda gidan sarauta yake ko sau d’aya ne a rayuwarta...haka kuwa akayi wani rana ta biyoni a tsorace na nuna mata cikin Masarauta, tayita mamakin girman gidan sarauta da yanda ake gudanar da al’amaran cikin Masarauta.. Naga yanda take matuk’ar son gidan sarauta da abinda ya shafi sarauta... Nace tinda ga k’aramar Sallah ta gabato ta fita taga yanda ake wasan Dawakai masu mulki suna hawa dawaki kuma suyi wasan saman dawaki su nuna bajintarsu.. Tace dani Aiko duk yanda za’ayi zata nemi hanya ta fito dukda ba sanin gari tayi ba, amma tana matuk’ar son ganin wasan doki... Nace zanso nayi mata rakiya tinda batasan kan gari ba amma saidai nid’in Bawa ne banida iko sai abinda Iyayen gidana sukace.. Na bata hak’uri nace bazan samu mata rakiya ba domin kuwa ni ne nake jan linzamin dokin D’an Sarki k’arami Wato Yarima Fu’ad sabida bai iya rik’e linzami..! A haka dai tace toh shikenan amma tabbas zata fita taga yanda wasan Doki yake kasancewa...!”
J’afar ya sauk’e nannauyan ajiyan zuciya hawaye naci gaba da gangaro masa yake furta “A ranan bukin wannan sallan tabbas wani al’amari ya faru... A hanyarmu ta komawa dani da yaran Sarki gaba d’aya wanda mune mukai dare sabida wasan doki da yaran sarki suka tsaya yi... A hanyarmu muka tsinci Saudatu ta b’ata sabida batasan kan gari ba... Yarima Mahmood wanda duk cikin yaran Sarki yafisu jin k’an mutane shi yayi umarni mu d’auketa mu maidota gida dan na sanar dashi na santa kuma har gidansu na sani.. Hakan yasa muka d’aukota muka nufo Masarauta... Na tafi na barta tareda yaran Sarki..!!” Muryarsa ya carke hawaye naci gaba da zubo masa...! Lokaci guda ya kuma d’agowa yana duban Gimbiya Turai wacce itama hawayen take... Cikin rawar murya yake furta “Kenan sun lalata rayuwar Saudatu..! Sunci zarfinta.. Sun tarwatsa ahalinta..!!! Tabbas daga baya na daina ganinta a kasuwa na kuma tadda gidansu su Saudatu ya k’one babu kowa cikinsa ya zama kango... Kuma babu wanda ya sansu balle naji labarun ina suka koma.! Ashe abinda Giwa da ‘ya’yanta suka aikata ma Saudatu kenan..!!” Ya k’arashe cikin wane irin huci lokaci guda ya mik’e yana furta “Wllhi sai na d’au fansa akan abinda suka mata..! Sai nayi ajalinsu d’aya bayan d’aya koda nima za’a d’auki nawa a matsayina na k’ask’antaccen Bawa..!!” Ya k’arashe cikin wane irin karaji...
Muryar Ubandoma suka sinkaya cikin zuban hawaye yana furta “Kai ba k’ask’antacce bane Ranakaidad’e..! Kai d’in Mai Martaba ne jinin mai Martaba..! Kai d’in D’ah ne ga Sarki AbdulJabbar mai rasuwa kuma mahaifiyarka tana nan a wajen nan tareda Kai...!!!”
K’irajai suka shiga bugawa..!! Gaba d’aya idanu suka koma kan Ubandoma....
SameenaAleeyou 📚
*MUHIBBAH*
*72*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Ubandoma ya d’an tsagaita da kukan da yake ya d’ago ya dubi Gimbiya Turai ya kuma duban Ja’afar wanda su duka biyun hawaye ne Ke gangarowa daga idanunsu ya kuma saita dubansaga Gimbiya Turai ya duk’a gabanta had’ida risinar da kansa “Rankidad’e Jaririn da Giwa ko ince Izzatu ta canza da naki shine jaririn Malam Almu Sarkin Barga... Izzatu itace Ta kashe matar Malam Almu ta kuma kashe jaririn, tazo da da wani jariri rayayye ta canza da jaririn matar Almu, ni....!” Muryarsa ta soma rawa sosai sanda Ja’afar da tuni jikinsa ya soma rawa sosai ya duk’a gaban Ubandoma yana mai furta “Da wani jariri ka canza..! Kayi magana, ka sanar damu wanene jaririn..!!?”
Ubandoma yaci gaba da hawaye yana mai furta “Gaba d’aya cikin laifukan da nayi a baya bisaga umarnin Izzatu babu wanda ya tsaya min a rai irin wannan sabida ya k’unshi jariri wanda baida hakkin kowa... Bansan daga yanda ta samo rayayyen jariri a wancan lokacin ba Ta bani nayi musayen jaririn da na matar Malam Almu wanda tuni tayi tsafi ta kashesu daga shi har uwarsa...!” Ya kuma d’agowa yana duban Ja’afar da Gimbiya Turai kana yaci gaba da fad’in “Rankidad’e wannan jaririn da aka kai miki matsayin naki tabbas ba naki bane kaman yanda Fattu Ta gani kuma ta fad’i maki... Jaririnki yana nan da raye..! Rankidad’e jaririnki ba kowa bane face JA’AFARU..!!!” Ya k’arashe cikin wani irin kuka yana mai zama dirshan a dandamalin k’asa...!
“Na jinjina kai nace toh inane gidanku..?! Daga yanda muke tsaye tamin nuni da wani gida can da yake arewa da yanda muke tsaye, gidan shi kad’ai ne a wajen tol ko mak’ota basu dashi..! Na jinjina kai nace ni kuma cikin Masarauta ne gidanmu kuma sunana Ja’afar...! Ni ba mugu bane kaman yanda kikayi zato, kiyi hak’uri da zubar miki kayan miya da nayi..! Wani ikon Allah sai gani nayi ta murmusa tace “Shikenan Babu komai nima kayi hak’uri da zubar maka harawarka da nayi..!”
“Na kuma murmusawa Ina dubanta sai kuma nace “Basai kin bani hak’uri ba ni na hak’ura... Ki tafi gida kar a soma nemanki..! Ki wuce har ki shige gida ina kallonki bazan bari wani ya cutar dake ba..! Ta murmusa tace min na gode, zan iya kiranka Yaya Ja’afar tunda banida kowa a garin nan kuma ba’a barina na fita ko ina sai kasuwa kasuwan ma sai ranakun sati..!”
“Na kuma murmusawa nace “Toh ai ban wani girmeki sosai ba ni kar ki tsufar dani ki kirani Yaya..! Ta kuma murmusawa tace “Amma ai ka girmeni, kuma nasan k’anwarka ce tsarata kaga ni banida wani Yaya banida kowa sai Ummah na da Abbah na saiko k’aramin k’anin da zata haifo min..!”
“Tayi maganan cikeda yarinta, na murmusa nace “Toh shikenan tinda bakida Yaya Ki kirani Yaya nima tinda banida k’anwa kin zamto k’anwata...Hakan yayi miki..!?”
“Ta jinjina kai tana kuma murmusawa tace yayi min.. Yaya Ja’afar..! Daga haka d’aga min hannu tayi ta shige tana waigowa har ta kusan isa gida Ina nan tsaye Ina dubanta, sai kuma na dakatar da ita nace “Gashi kuma Yaya baisan sunan k’awarsa ba har zata shige..!” Ta murmusa kad’an tace “Sunana SAUDATU..!”
“Na jinina kai nace “K’anwata Saudatu..! Tai gajeren murmushi Ta kuma d’ago min hannu tace sai anjima...! Har saida naga shigarta gida kafin nasa kai nima na d’auki ciyawata na shige...! Toh tin daga wanann lokacin Sabo ya shiga tsakaninmu da Saudatu, nakan mata rakiya har zuwa gida, a haka bukin sallah ya k’arato na kula tana son zuwa taga hawan Dawakai amma baza’a barta ba a gida tinda ba’a barinta taje ko ina... Nayita bata labarin yanda hawan bukin sallah yake kasancewa, sosai yake sakata nishad’i yanda kasan ta had’a jini da sarauta... Kullum bata da labari da ya wuce na Dawakai da gidan sarauta... Tace min tana son ta shigo Masarautar nan wata ran taga yanda ginin gidan sarauta yake.. sabida idan tanama Abbanta labarin sarauta da abinda ya shafi gidan sarauta sai yayita mata fad’a yace koda wasa babu abinda ya had’ata da sarauta, babu komai cikin gidan sarauta sai zalunci... Dukda kuwa tsananin son kasancewa gidan sarauta da Saudatu keyi... Wata Rana Nace ta biyoni na shiga da ita taga yanda gidan sarauta yake ko sau d’aya ne a rayuwarta...haka kuwa akayi wani rana ta biyoni a tsorace na nuna mata cikin Masarauta, tayita mamakin girman gidan sarauta da yanda ake gudanar da al’amaran cikin Masarauta.. Naga yanda take matuk’ar son gidan sarauta da abinda ya shafi sarauta... Nace tinda ga k’aramar Sallah ta gabato ta fita taga yanda ake wasan Dawakai masu mulki suna hawa dawaki kuma suyi wasan saman dawaki su nuna bajintarsu.. Tace dani Aiko duk yanda za’ayi zata nemi hanya ta fito dukda ba sanin gari tayi ba, amma tana matuk’ar son ganin wasan doki... Nace zanso nayi mata rakiya tinda batasan kan gari ba amma saidai nid’in Bawa ne banida iko sai abinda Iyayen gidana sukace.. Na bata hak’uri nace bazan samu mata rakiya ba domin kuwa ni ne nake jan linzamin dokin D’an Sarki k’arami Wato Yarima Fu’ad sabida bai iya rik’e linzami..! A haka dai tace toh shikenan amma tabbas zata fita taga yanda wasan Doki yake kasancewa...!”
J’afar ya sauk’e nannauyan ajiyan zuciya hawaye naci gaba da gangaro masa yake furta “A ranan bukin wannan sallan tabbas wani al’amari ya faru... A hanyarmu ta komawa dani da yaran Sarki gaba d’aya wanda mune mukai dare sabida wasan doki da yaran sarki suka tsaya yi... A hanyarmu muka tsinci Saudatu ta b’ata sabida batasan kan gari ba... Yarima Mahmood wanda duk cikin yaran Sarki yafisu jin k’an mutane shi yayi umarni mu d’auketa mu maidota gida dan na sanar dashi na santa kuma har gidansu na sani.. Hakan yasa muka d’aukota muka nufo Masarauta... Na tafi na barta tareda yaran Sarki..!!” Muryarsa ya carke hawaye naci gaba da zubo masa...! Lokaci guda ya kuma d’agowa yana duban Gimbiya Turai wacce itama hawayen take... Cikin rawar murya yake furta “Kenan sun lalata rayuwar Saudatu..! Sunci zarfinta.. Sun tarwatsa ahalinta..!!! Tabbas daga baya na daina ganinta a kasuwa na kuma tadda gidansu su Saudatu ya k’one babu kowa cikinsa ya zama kango... Kuma babu wanda ya sansu balle naji labarun ina suka koma.! Ashe abinda Giwa da ‘ya’yanta suka aikata ma Saudatu kenan..!!” Ya k’arashe cikin wane irin huci lokaci guda ya mik’e yana furta “Wllhi sai na d’au fansa akan abinda suka mata..! Sai nayi ajalinsu d’aya bayan d’aya koda nima za’a d’auki nawa a matsayina na k’ask’antaccen Bawa..!!” Ya k’arashe cikin wane irin karaji...
Muryar Ubandoma suka sinkaya cikin zuban hawaye yana furta “Kai ba k’ask’antacce bane Ranakaidad’e..! Kai d’in Mai Martaba ne jinin mai Martaba..! Kai d’in D’ah ne ga Sarki AbdulJabbar mai rasuwa kuma mahaifiyarka tana nan a wajen nan tareda Kai...!!!”
K’irajai suka shiga bugawa..!! Gaba d’aya idanu suka koma kan Ubandoma....
SameenaAleeyou 📚
*MUHIBBAH*
*72*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Ubandoma ya d’an tsagaita da kukan da yake ya d’ago ya dubi Gimbiya Turai ya kuma duban Ja’afar wanda su duka biyun hawaye ne Ke gangarowa daga idanunsu ya kuma saita dubansaga Gimbiya Turai ya duk’a gabanta had’ida risinar da kansa “Rankidad’e Jaririn da Giwa ko ince Izzatu ta canza da naki shine jaririn Malam Almu Sarkin Barga... Izzatu itace Ta kashe matar Malam Almu ta kuma kashe jaririn, tazo da da wani jariri rayayye ta canza da jaririn matar Almu, ni....!” Muryarsa ta soma rawa sosai sanda Ja’afar da tuni jikinsa ya soma rawa sosai ya duk’a gaban Ubandoma yana mai furta “Da wani jariri ka canza..! Kayi magana, ka sanar damu wanene jaririn..!!?”
Ubandoma yaci gaba da hawaye yana mai furta “Gaba d’aya cikin laifukan da nayi a baya bisaga umarnin Izzatu babu wanda ya tsaya min a rai irin wannan sabida ya k’unshi jariri wanda baida hakkin kowa... Bansan daga yanda ta samo rayayyen jariri a wancan lokacin ba Ta bani nayi musayen jaririn da na matar Malam Almu wanda tuni tayi tsafi ta kashesu daga shi har uwarsa...!” Ya kuma d’agowa yana duban Ja’afar da Gimbiya Turai kana yaci gaba da fad’in “Rankidad’e wannan jaririn da aka kai miki matsayin naki tabbas ba naki bane kaman yanda Fattu Ta gani kuma ta fad’i maki... Jaririnki yana nan da raye..! Rankidad’e jaririnki ba kowa bane face JA’AFARU..!!!” Ya k’arashe cikin wani irin kuka yana mai zama dirshan a dandamalin k’asa...!