Sashe 134
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Gimbiya Turai ta jinjina kai tace “Tabbas Baba Sadi ne wanda kaman k’ani yake wa mahaifiyarmu, munada dangantaka dashi na tabbata shine ya d’auke Alfah gudun kar masu wawason gadon Mulki su cutar dashi..! Allahu Akbar bansan Baba Sadi yanada d’iya ba.. koda shike watak’ila nayi aure kafin ya haifeta ko kuma ya haifi mahaifiyar taki amma tana k’arama lokacin shiyasa bazan santa ba..!”
Muhibbah ta jinjina kai kana taci gaba da fad’in “Abbah ya tattaro Mu gaba d’aya ya taho damu neman abu mai mahimmanci a gareshi da kullum yake fad’i wanda Nidai ban San menene wannan abin ba mai yuwa Sabida k’arancin shekaruna a wancan lokacin amma ta yuwu Mahaifiyata ta sani..! Ashe a wannan lokacin Mahaifiyata tana d’aukeda juna biyu..! Kafin mu k’araso garin Jos mun tsaya a wani gari mai suna Tafisu a can kusan yankin Niger state..! Toh a wannan garin taita rainon Jaririn cikinta har dai labari ya iso ga mahaifina cewa abinda yake nema yana a nan garin Jos, dukda juna biyu da take dashi haka muka baro garin Tafisu muka nufo garin Jos.. A lokacin juna biyu da Mahaifiyata kedashi ya d’an soma girma...!!” Tai shiru hawaye naci gaba da gangaro mata..! Muryarta yaci gaba da rawa sanda taci gaba da basu labari tazo daidai yanda ‘Ya’yan Giwa sukaci zarafinta, da yanda Ta farka Ta tsinci kanta gaban wannan matsafin..!
Mahmood dake kallonsu daga d’akinsa hawaye ne shima yaji suna gangarowa daga fuskarsa..! Yaci gaba da matse zobban hannunsa wanda har baisan yaji masa ciwo a d’an yatsa ba sabida yanda zuciyarsa Ke tsananin tafarfasa...!
Muhibbah ta share k’wallan da suka zubo mata kana taci gaba da fad’in “Sun tarwatsa ahalin da suka rage min a wancan lokacin..! Sun cinnawa gidanmu wuta wanda hakan ya samu tserewa da rayuwarmu...! Zan iya ce maku bansan yaya akayi na had’u da Mahaifiyata ba, wane irin tashin hankula ne muka tsinci kawunanmu ciki a wancan lokacin wanda baki bazai iya fad’I ba, zuciya bazata iya kwatanta girman tashin hankalin ba... Iyakacin abinda na sani shine Mahaifiyata tace dole mu gudu mu bar wannan garin, dan a daren da abun ya faru a daji muka kwana, gashi cikinmu babu mai wani k’arfi, ita tana fama da juna biyu ni kuma ga iftila’i da tsautsayin da ya auka min wanda ko tafiya bana iya yi saidai Mahaifiyata da take fama da juna Ta Azani a bayanta..! Shin ku gaya min nayi laifi da nace zan dawo d’aukan Fansa..?!!”
Hawaye ya kasa daina gangarowa daga fuskokinsu... Lokaci guda taci gaba da fad’in “Da taimakon wani mai motan kwaso dabbobi daga arewa akwaisu Kudu shi ya taimaka mana ya fitar damu zuwa garin Yalwan Shandam, koda mukaje garin tana cikin yanayi na tashin tashin hankula, a nan wannan garin dai muka samu mafaka a sansanin ‘yan gudun Hijira wanda har na d’an sami kulawa daga likitoci masu kawo agaji ma ‘yan gudun Hijira Mahaifiyata ma ta sami kula daga wajen likitocin duba da yanayin da take ciki...! Maikatan lafiya dake kula da ‘yan gudun Hijiran sunyi mamaki da jin zafin yanda akaci zarafina gashi dududu ba wani shekaru ne dani ba..! Na shiga tashin hankali Mahaifiyata ma ta shiga tashin hankali maras misaltuwa da abinda ya sameni, na zamto bana shiga cikin yaran dake wannan sansanin domin kuwa tinda mutanen dake cikin sansanin suka soma ‘yar gulmace gulmacen abinda ya sameni kowa sai yana janye ‘ya’yensa daga gareni, babu mai barina na kusanci ‘ya’yansa balle nayi wasa taredasu.. Na koma tamkar wata mujiya abin gudu ga kowa... Rayuwa Ta mun d’aci matuk’a, na fuskanci kyara da tsangwama, kowa ya ganni sai gudu tamkar anga dodanniya... Wannan rayuwar itace na fuskanta a Sansanin da muka tsinci kawunanmu ciki... Inada tabbacin tsananin da muka shiga tareda k’uncin abinda ya sameni shi ya sanya Mahaifiyata haihuwa yazo mata ba tareda lokacin haihuwar ya cika ba..! Mahaifiyata ta haifo d’iyarta mace kyakkyawa, saidai tinda Ta haihu batayi lafiya ba... Na buk’aci a sanyawa Yarinyar suna Muhibbah domin ta samu soyayyar mutane kaman yanda sunan nata yake..! A daidai wannan lokaci ‘yan tadda suka kawoma Sansanin Farmak’i... Suka cinna ma Sansanin wuta, aka soma gudu kan mai uwa dawabi ana tattara yaran dake Sansanin dan tseratar da rayuwarmu.. Banga Mahaifiyata ba banga jarriyarta ba.. Na dinga tsalle ina ihu ina k’ok’arin k’watan hannuna daga hannun ‘yan kwana kwanan da suka kawo mana d’auki Ina fad’in su k’yaleni Mahaifiyata da k’anwata suna cikin Tent d’inmu wanda Ke ci da wuta..! Haka suka hanani zuwa suna sanar dani saidai nayi hak’uri Mahaifiyata da ‘yaruwata sun mutu a wannan wutar sun zama toka go gawawwakinsu ba’a gani ba..!”
Ta kuma goge wasu hawayen kana taci gaba da fad’in “Ya kuke tunanin yarinya mai k’aramin shekaru kaman nawa zataji a wancan lokacin.. Ta yaya bazan girma da k’udirin tarwatsa mutanen da suka tarwatsa min ahalina ba..!” Cikin muryarta dake tsananin rawa taci gaba da furta “Na k’wace hannuna na soma gudu banma San ina nake zuwa ba.. A iyaka sanina shine bazan kuma zama a wannan Sansanin babu Mahaifiyata babu k’anwata ba...!”
“Sansanin dake Yalwan Shandam..!” Ya nanata a hankali...Take ya shiga tuna abubuwan da suka faru baya, abinda suka bisne shida abokinsa Turaki tsawon shekaru..!Shafe fuskarsa da gumi Ke tsartsafo masa ya kumayi yana jin yanda Muhibba taci gaba da bada labarin yanda ta kub’uta daga wannan sansanin har kawo zuwa yanda iyayen Ansar suka taimaka mata, suka zamto sutura da Gata a gareta, Ansar ya zamto tamkar wani fitila wanda ya haskaka mata rayuwa.. Shida mahaifiyarsa sunyi mata komai. Taji tsoron sanar dasu abinda ya faru da ita gudun kar suma su k’yamace ta kaman yanda aka gujeta a Sansanin Yalwan Shandam..! Haka taita basu labari har dawowarta Masarautar da k’udirinta da kuma yanda Ansar ya taimaka mata sukayi komai tare hardai zuwa k’alubalen da suka fuskanta daga wajen Yawale da Gudidi kan batun aurensu da yanda mahaifiyar Ansar tak’i amincewa bayan dataji abinda ya sami Muhibbar wanda bata baiwa Muhibbah ko Ansar daman yi mata bayanin abinda ya faru ba..! Hardai zuwa ranan aurenta data farka Ta tsinci kanta a wannan d’akin...!
Gimbiya Turai ta dafe hannayensu su duka biyun tace “Duk wannan iftila’i da rarrabuwan ahali da muka tsinci kawunanmu ciki tuni Allah ya k’addari faruwan hakan saidai akwai sanadi, sanadi kuma Izzatu ce..! Dole mu godewa Allah mu kuma gode masa da a k’arashe ya had’e ahalinmu waje guda..! ‘Yanuwanmu da suka rigayemu gidan gaskiya Ubangiji ya gafarta masu mu kuma idan namu tazo ya d’auki ranmu muna masu imani, mutuwa dole ce hanyace guda d’aya wanda dole kowa sai yabi..! Banaso ku saka ma ranku cewa wani ne ya jawo kuka rasa masoyanku iyayenku da ‘yanuwanku, a’a wani baya rayawa kuma baya kashewa.. Allah shi kad’ai ne mai rayawa ya kuma kashe, duk wanda ya rasu lokacinsa ne yayi saidai wani ya zamto sanadi kun fahimta..!” Suka jinjina kansu a hankali suna masu share hawayensu..! Sun d’an jima kad’an har sukaci abinci tare gwanin dad’I da sha’awa kana sukaima Muhibbah sallama kowa ya nufi nasa b’angaren, Gimbiya Turai ma da nata Hadiman ta nufi nata b’angaren da aka Ware mata na musamman... Can ta tadda Gimbiya Zeenat na zaman jiran K’arasowarta..!
Gabatar da kanta Gimbiya Zeenat tayi had’ida neman yafiya kan biyewa Giwa da tayi Ta kasa tona mata asiri na kisan matar Mahmood Aliya da tayi dan kawai ‘yaruwarta ta auri Mahmood d’in.. Gimbiya Turai tace ai Babu komai itama ta fad’a tarkon Izzatu ne, tana fata abubuwanda suka faru cikin Masarautar ya zamto wa’azi garesu gaba d’aya Dama wad’anda sukaso kwakwayon wannan muggan d’abi’u..!
**
Zama yayi bisa couch yana duban duk wani motsinta tinanin labarinta bai daina Yawo akansa ba... Lokaci guda ya hangota ya fito daga closet, wannan karon doguwar rigar bacci ce mai laushin gaske Wanda ya kwanta luf jikinta..! Ya lumshe idanunsa a hankali yana tunanin idan yana son sanin cewa Muhibbah da Zarah ‘yan uwan junane Toh ya kamata ya d’auko sample d’in Muhibbar cikin daren nan Washe gari ya bada a running masa DNA test tsakanin samples d’in nasu guda biyu..! Toh amma ta ya zai sami sample d’in Muhibbah cikin daren..?!
Ya kuma lumshe idanunsa yana tunanin abinyi, wata zuciya tace kaje ka samo da kanka..!
Yana ganin sanda ta ida sallan shafa’i da wutiri Ta linke abin sallahn ta mik’e ta haye gado had’ida kashe wuta..!
Mik’ewa shima yayi ya zira jallabiyarsa fara k’al sai k’amshi ke tashi ya nufi nata b’angaren..!
Harga Allah bataji shigowar mutum ba dan bacci yayi gaba da ita... Ya jima sosai yana k’are mata kallo da d’an hasken dake hasko cikin d’akin daga waje... Ya zauna a gefenta a hankali yana mai ci gaba da k’arema halittar jikinta kallo...
Ya lumshe idanunsa a hankali yana mai jin yarrr gaba d’aya stikar jikinsa na tashi... Wata zuciyar tace kayi abinda ya kawo ka ka fice kafin Ta farka ta ganka...!
Da wannan tunanin ya soma zame hular bacci dake kanta a hankali kaman mai tsoron kada ya tada ita ga wani irin bugu da zuciyarsa keyi..!
Muhibbah ta jinjina kai kana taci gaba da fad’in “Abbah ya tattaro Mu gaba d’aya ya taho damu neman abu mai mahimmanci a gareshi da kullum yake fad’i wanda Nidai ban San menene wannan abin ba mai yuwa Sabida k’arancin shekaruna a wancan lokacin amma ta yuwu Mahaifiyata ta sani..! Ashe a wannan lokacin Mahaifiyata tana d’aukeda juna biyu..! Kafin mu k’araso garin Jos mun tsaya a wani gari mai suna Tafisu a can kusan yankin Niger state..! Toh a wannan garin taita rainon Jaririn cikinta har dai labari ya iso ga mahaifina cewa abinda yake nema yana a nan garin Jos, dukda juna biyu da take dashi haka muka baro garin Tafisu muka nufo garin Jos.. A lokacin juna biyu da Mahaifiyata kedashi ya d’an soma girma...!!” Tai shiru hawaye naci gaba da gangaro mata..! Muryarta yaci gaba da rawa sanda taci gaba da basu labari tazo daidai yanda ‘Ya’yan Giwa sukaci zarafinta, da yanda Ta farka Ta tsinci kanta gaban wannan matsafin..!
Mahmood dake kallonsu daga d’akinsa hawaye ne shima yaji suna gangarowa daga fuskarsa..! Yaci gaba da matse zobban hannunsa wanda har baisan yaji masa ciwo a d’an yatsa ba sabida yanda zuciyarsa Ke tsananin tafarfasa...!
Muhibbah ta share k’wallan da suka zubo mata kana taci gaba da fad’in “Sun tarwatsa ahalin da suka rage min a wancan lokacin..! Sun cinnawa gidanmu wuta wanda hakan ya samu tserewa da rayuwarmu...! Zan iya ce maku bansan yaya akayi na had’u da Mahaifiyata ba, wane irin tashin hankula ne muka tsinci kawunanmu ciki a wancan lokacin wanda baki bazai iya fad’I ba, zuciya bazata iya kwatanta girman tashin hankalin ba... Iyakacin abinda na sani shine Mahaifiyata tace dole mu gudu mu bar wannan garin, dan a daren da abun ya faru a daji muka kwana, gashi cikinmu babu mai wani k’arfi, ita tana fama da juna biyu ni kuma ga iftila’i da tsautsayin da ya auka min wanda ko tafiya bana iya yi saidai Mahaifiyata da take fama da juna Ta Azani a bayanta..! Shin ku gaya min nayi laifi da nace zan dawo d’aukan Fansa..?!!”
Hawaye ya kasa daina gangarowa daga fuskokinsu... Lokaci guda taci gaba da fad’in “Da taimakon wani mai motan kwaso dabbobi daga arewa akwaisu Kudu shi ya taimaka mana ya fitar damu zuwa garin Yalwan Shandam, koda mukaje garin tana cikin yanayi na tashin tashin hankula, a nan wannan garin dai muka samu mafaka a sansanin ‘yan gudun Hijira wanda har na d’an sami kulawa daga likitoci masu kawo agaji ma ‘yan gudun Hijira Mahaifiyata ma ta sami kula daga wajen likitocin duba da yanayin da take ciki...! Maikatan lafiya dake kula da ‘yan gudun Hijiran sunyi mamaki da jin zafin yanda akaci zarafina gashi dududu ba wani shekaru ne dani ba..! Na shiga tashin hankali Mahaifiyata ma ta shiga tashin hankali maras misaltuwa da abinda ya sameni, na zamto bana shiga cikin yaran dake wannan sansanin domin kuwa tinda mutanen dake cikin sansanin suka soma ‘yar gulmace gulmacen abinda ya sameni kowa sai yana janye ‘ya’yensa daga gareni, babu mai barina na kusanci ‘ya’yansa balle nayi wasa taredasu.. Na koma tamkar wata mujiya abin gudu ga kowa... Rayuwa Ta mun d’aci matuk’a, na fuskanci kyara da tsangwama, kowa ya ganni sai gudu tamkar anga dodanniya... Wannan rayuwar itace na fuskanta a Sansanin da muka tsinci kawunanmu ciki... Inada tabbacin tsananin da muka shiga tareda k’uncin abinda ya sameni shi ya sanya Mahaifiyata haihuwa yazo mata ba tareda lokacin haihuwar ya cika ba..! Mahaifiyata ta haifo d’iyarta mace kyakkyawa, saidai tinda Ta haihu batayi lafiya ba... Na buk’aci a sanyawa Yarinyar suna Muhibbah domin ta samu soyayyar mutane kaman yanda sunan nata yake..! A daidai wannan lokaci ‘yan tadda suka kawoma Sansanin Farmak’i... Suka cinna ma Sansanin wuta, aka soma gudu kan mai uwa dawabi ana tattara yaran dake Sansanin dan tseratar da rayuwarmu.. Banga Mahaifiyata ba banga jarriyarta ba.. Na dinga tsalle ina ihu ina k’ok’arin k’watan hannuna daga hannun ‘yan kwana kwanan da suka kawo mana d’auki Ina fad’in su k’yaleni Mahaifiyata da k’anwata suna cikin Tent d’inmu wanda Ke ci da wuta..! Haka suka hanani zuwa suna sanar dani saidai nayi hak’uri Mahaifiyata da ‘yaruwata sun mutu a wannan wutar sun zama toka go gawawwakinsu ba’a gani ba..!”
Ta kuma goge wasu hawayen kana taci gaba da fad’in “Ya kuke tunanin yarinya mai k’aramin shekaru kaman nawa zataji a wancan lokacin.. Ta yaya bazan girma da k’udirin tarwatsa mutanen da suka tarwatsa min ahalina ba..!” Cikin muryarta dake tsananin rawa taci gaba da furta “Na k’wace hannuna na soma gudu banma San ina nake zuwa ba.. A iyaka sanina shine bazan kuma zama a wannan Sansanin babu Mahaifiyata babu k’anwata ba...!”
“Sansanin dake Yalwan Shandam..!” Ya nanata a hankali...Take ya shiga tuna abubuwan da suka faru baya, abinda suka bisne shida abokinsa Turaki tsawon shekaru..!Shafe fuskarsa da gumi Ke tsartsafo masa ya kumayi yana jin yanda Muhibba taci gaba da bada labarin yanda ta kub’uta daga wannan sansanin har kawo zuwa yanda iyayen Ansar suka taimaka mata, suka zamto sutura da Gata a gareta, Ansar ya zamto tamkar wani fitila wanda ya haskaka mata rayuwa.. Shida mahaifiyarsa sunyi mata komai. Taji tsoron sanar dasu abinda ya faru da ita gudun kar suma su k’yamace ta kaman yanda aka gujeta a Sansanin Yalwan Shandam..! Haka taita basu labari har dawowarta Masarautar da k’udirinta da kuma yanda Ansar ya taimaka mata sukayi komai tare hardai zuwa k’alubalen da suka fuskanta daga wajen Yawale da Gudidi kan batun aurensu da yanda mahaifiyar Ansar tak’i amincewa bayan dataji abinda ya sami Muhibbar wanda bata baiwa Muhibbah ko Ansar daman yi mata bayanin abinda ya faru ba..! Hardai zuwa ranan aurenta data farka Ta tsinci kanta a wannan d’akin...!
Gimbiya Turai ta dafe hannayensu su duka biyun tace “Duk wannan iftila’i da rarrabuwan ahali da muka tsinci kawunanmu ciki tuni Allah ya k’addari faruwan hakan saidai akwai sanadi, sanadi kuma Izzatu ce..! Dole mu godewa Allah mu kuma gode masa da a k’arashe ya had’e ahalinmu waje guda..! ‘Yanuwanmu da suka rigayemu gidan gaskiya Ubangiji ya gafarta masu mu kuma idan namu tazo ya d’auki ranmu muna masu imani, mutuwa dole ce hanyace guda d’aya wanda dole kowa sai yabi..! Banaso ku saka ma ranku cewa wani ne ya jawo kuka rasa masoyanku iyayenku da ‘yanuwanku, a’a wani baya rayawa kuma baya kashewa.. Allah shi kad’ai ne mai rayawa ya kuma kashe, duk wanda ya rasu lokacinsa ne yayi saidai wani ya zamto sanadi kun fahimta..!” Suka jinjina kansu a hankali suna masu share hawayensu..! Sun d’an jima kad’an har sukaci abinci tare gwanin dad’I da sha’awa kana sukaima Muhibbah sallama kowa ya nufi nasa b’angaren, Gimbiya Turai ma da nata Hadiman ta nufi nata b’angaren da aka Ware mata na musamman... Can ta tadda Gimbiya Zeenat na zaman jiran K’arasowarta..!
Gabatar da kanta Gimbiya Zeenat tayi had’ida neman yafiya kan biyewa Giwa da tayi Ta kasa tona mata asiri na kisan matar Mahmood Aliya da tayi dan kawai ‘yaruwarta ta auri Mahmood d’in.. Gimbiya Turai tace ai Babu komai itama ta fad’a tarkon Izzatu ne, tana fata abubuwanda suka faru cikin Masarautar ya zamto wa’azi garesu gaba d’aya Dama wad’anda sukaso kwakwayon wannan muggan d’abi’u..!
**
Zama yayi bisa couch yana duban duk wani motsinta tinanin labarinta bai daina Yawo akansa ba... Lokaci guda ya hangota ya fito daga closet, wannan karon doguwar rigar bacci ce mai laushin gaske Wanda ya kwanta luf jikinta..! Ya lumshe idanunsa a hankali yana tunanin idan yana son sanin cewa Muhibbah da Zarah ‘yan uwan junane Toh ya kamata ya d’auko sample d’in Muhibbar cikin daren nan Washe gari ya bada a running masa DNA test tsakanin samples d’in nasu guda biyu..! Toh amma ta ya zai sami sample d’in Muhibbah cikin daren..?!
Ya kuma lumshe idanunsa yana tunanin abinyi, wata zuciya tace kaje ka samo da kanka..!
Yana ganin sanda ta ida sallan shafa’i da wutiri Ta linke abin sallahn ta mik’e ta haye gado had’ida kashe wuta..!
Mik’ewa shima yayi ya zira jallabiyarsa fara k’al sai k’amshi ke tashi ya nufi nata b’angaren..!
Harga Allah bataji shigowar mutum ba dan bacci yayi gaba da ita... Ya jima sosai yana k’are mata kallo da d’an hasken dake hasko cikin d’akin daga waje... Ya zauna a gefenta a hankali yana mai ci gaba da k’arema halittar jikinta kallo...
Ya lumshe idanunsa a hankali yana mai jin yarrr gaba d’aya stikar jikinsa na tashi... Wata zuciyar tace kayi abinda ya kawo ka ka fice kafin Ta farka ta ganka...!
Da wannan tunanin ya soma zame hular bacci dake kanta a hankali kaman mai tsoron kada ya tada ita ga wani irin bugu da zuciyarsa keyi..!