← Book details Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 125 OF 162

Sashe 125

Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bud’e idanun da zatai Ta hangi Giwa, Jamal harma da Jakadiya tsaye daga k’ofar d’akin suna dubanta..!

Giwa ta kece da wani irin dariya yau d’in sanye take da bak’ar lkyabbarta na tsafi ga wani bak’in tulu gabanta harda wani jan fitila maici da jan wuta...

SameenaAleeyou 📚*MUHIBBAH*

*74*

*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*

Cikin zuban hawaye take dubansu d’aya bayan d’aya zuciyarta na kuma karaya da tinanin watak’ila itakuma tata K’ADDARAR kenan ta mutu cikin wannan d’akin hannun wad’annan azzaluman... Ta lumshe idanunta hawaye suka kuma gangaro mata.. Cikin zuciyarta take furta “Ya Allah kada ka k’addara mutuwata hannun wad’annan azzaluman bayi naka..! Ya Allah ka kub’utar dani da buwayarka kar ka basu nasaran cutar dani..!” Bata ida ba taji Giwa tasa k’afa ta shureta...

Tayi tsaye gaban Muhibbar had’ida k’ura mata idanu, lokaci guda ta shiga jinjina kai tana furta “Tabbas ke ce..! SAUDATU..!” Ta kuma sakin murmushi kana taci gaba da fad’in “Na tabbata kin gane d’akin nan..! D’akin da ya shekara goma sha hud’u a bud’e yana zaman jiranki, yau gashi kin dawo cikinsa kuma zaki dawwama cikinsa domin kuwa wannan d’aki Naki ne wanda aka ambacesa da sunanki Saudatu aka kuma rubuta saman Farin k’yalle, Ked’in kyauta ce ga Sarauniya, a yau Zata cika k’udirin ta ta kuma cika min Mulki na da gudan jininki..!!” Ta kuma kecewa da dariya..!

Muhibbah da hawaye Ke gangaro mata take Ta soma furta “Allah bai baku nasara shekarun baya ba, Maiyasa kike tunanin zai baku nasara yanzu..? Maiyasa kike tunanin zaki tabbata kina zalunci..! Barin tuna miki idan kin mance.. Ni ce nan wacce na shigo rayuwarku na tarwastaku ba tareda kun ankare ba..! Kuma ni ce nan zan zamto silan tonuwar asirinki dake da muk’arabbanki... Zaki gani da sannu Ubangijina zai kawo min d’auki ya kawo wanda zai fiddani daga sharrinku..!!” Batakai aya ba Giwa ta d’auketa da muguwar mari.. Lokaci guda take furta “Babu wanda zai fitar dake daga wajen nan Saudatu, duk duniyar nan babu wanda yakeda mabud’in wannan gini... Mutum guda yake da mabud’in wannan gini kuma ya mutu.. Mabud’in wannan gini guda d’aya ne tak kuma an bisneta cikin K’undi da jimawa... Saudatu bazaki tab’a ficewa daga wajen nan ba... Nima kaina banida wannan mabud’in wanda ya adana wannan mabud’in har ya bar duniya bai mallaka min ba... An busnesa tareda k’undin cikin turb’aya....Tal’udu shi ya bani karatun tsafi da zanke biyawa ginin ya tsage min na shige.. Sannan ko Jakadiya da a kullum take min rakiya bata iya wannan karatun tsafin ba.. Gata nan ga Jamal ki tambayesu ya akai suka shigo wajen nan... Bud’e idanu kawai suma sukai suka gansu cikin wajen nan kaman yanda Kema bud’e idanu kurum kikayi kika ganki ciki..! Har abada babu wanda zai iya fitar dake Saudatu..!!” Ta kuma kecewa da wani irin dariya..

Muhibbah na murmushi take furta “Wanda ya fitar dani daga farko inada tabbacin shi zai kuma fitar dani..! Dashi nayi imani dashi na dogara, kuma na tabbata shine zai taimakeni..! Da sannu zai tona miki asiri, sannan ya k’asak’antar dake, zaki koma bakida wani daraja ko matsayi ta yanda k’ask’antaccen bawa sai ya fiki daraja cikin Masarautar nan..!” Bata kai aya ba Giwa ta kuma kwashe ta da wata mari.. Tana huci take nunata tana fad’in “Ke k’aramar maras kunya..! Na gama da iyayenki na gama da kaf zuri’arki balle ke..Tin daga Kan Kakanki Sarki Jamaluddeen na k’asar Benin wanda shine ya haifi mahaifinki Yarima Alfah d’an uwa ga Gimbiya Turai matar Sarki AbdulJabbar wacce na maidata Kuyanga a gidan Mijinta, mahaifiya ga ‘ya’yan Sarki guda biyu Yarima Mahmood wanda na maidashi nawa tin yana jariri domin na cika k’udirina akansa, da kuma Ja’afar wanda na maidashi d’an Bawa ya girma cikin k’ask’anci da bauta a gidan mahaifinsa a Masarautar Sa.. Dan haka ki sani gamawa dake abu ne mai matuk’ar sauk’i a gareni k’aramar Alhaki..!!” Ta k’arashe tana mai d’ago fuskar Muhibbah wacce ta shige rud’u sosai.. Bata fahimci mai wannan matar take fad’i ba gaba d’aya ta zama lost and confused..! Cikin wane irin yanayi take duban Giwa da idanunta da suka firfito waje tana jin kanta na juya mata...

Giwa ta kuma kecewa da dariya tace “Nasan duk bakisan wad’annan labarun ba, bakida masaniya amma bazan bari ki tafi ba tareda kin sani ba... Zan baki labarin duk abubuwan da nayi ma zuri’arki tin daga tushe... Idan kika tafi a haka ba tareda kin sani ba kinci banza..! Gwara ki San komai, kisan duk abubuwan dana aikata kafin k’ofar d’akin nan ya rufe dake rufuwa ta har abada..!!” Ta kuma kecewa da muguwar dariya...

Take Giwa Ta shiga labartawa Muhibbah duk abubuwan da suka faru tin daga farko, Dik wani k’ulli da makirci da tayi da lokutan da abubuwan suka faru da komai da komai..!

**

A can asibiti wajen Yazeed kuwa bore da hauka yake ci gaba da yi, an masa alluran baccin ma kaman a banza don yana somawa allurar zata sakesa ya farka yaci gaba da ihu yana fad’in a dawo masa da hannayensa da yaransa... Ya dubi Waziri dake zaune gefensa dan tinda ya farka bai bar gefen Yazeed d’in ba...! Cikin wane irin huci yake ceda Waziri “Kai Old Geezer, Take me to the palace..! I want to see Mahmood, I want to rub it to his face... Ina so naga fuskarsa idan yaji cewa shid’in ba kowa bane d’an Baiwa ce k’ask’antacciya mai k’wacen mijin Uwargijiyarta..! Ka d’aukeni ka kaini Masarauta na sanar da Mahmood haka, ya daina jin kansa shid’in wani ne ko shi d’in yafi wani... Baifi kowa ba shid’in k’asaitacce ne d’an Baiwa... Baiwarma Ta wani Masarautar wacce aka sadakar da ita...! Ka d’aukeni Ka kaini nace... I can’t be the only loser..! Mahmood ma dole ya d’and’ani irin k’uncin dana d’and’ana... Na tabbata yana can yana murnan abubuwan da suka sameni..! Amma idan yaji asalinsa da tushensa zai fahimci cewa shid’in k’ask’antacce ne... Bawa bai dace da sarautar Masarautar mu ba... Gwara nakasasshe ya zamto Sarki akanka D’an Baiwa ya gaji sarauta..! Ashe abin a jini yake shiyasa ya k’are ya auri d’iyar bayi...! Toh yau d’in nan wllhi zaiji asalinsa koda zai had’iyi zuciya ya mutu ne..!!” Ya k’arashe yana mai ci gaba da fidda huci..!

Waziri dake faman muzurai zuciyarsa na tsinkewa ya soma fad’in “A’a Yazeed kai hak’uri dai har ka k’ara samun lafiya...!”

Baikai aya ba Yazeed ya katsesa da fad’in “Kai Dattijo kayi abinda na umarceka idan kana son kanka da lafiya.. Har gobe nid’in sama dakai nake domin ni d’an Sarki AbdulJabbar ne... Ko a mafarki kada ka tab’a zaton zan kalleka matsayin mahaifi..! Tashi ka kaini masarauta idan baka so na k’arasa kashe kaina yanzu a asibitin nan..!!”

Waziri ya had’iyi miyau da k’yar yana sab’a babbar riga cikeda daburcewa yake fad’in “Toh..Toh.. Toh ai Wato ai gani nayi ciwonka d’anye ne dukda cewa na rufe cikin bandeji..!”

Yazeed ya katsesa da fad’in “Zakayi abinda na umarceka ne kokuwa...!!”

Waziri ya kuma mik’ewa zunbur yana furta “A’a ba za’ayi haka ba Rankaidad’e..!!” Lokaci guda ya mik’e ya nufi k’ofa yana fad’in bari ya kirawo malaman asibiti su kwance ruwan da aka d’aura masa...! Bai kuma tsayawa sauraren Yazeed ba ya fice...!

Yazeed ya shiga k’walla masa kira, inaa Waziri ko juyowa baiba dan ko kusa bazai biyema Yazeed su tapka wannan rashin hankalin ba... Domin kuwa ba asirin Mahmood zai tona ba asirin mahaifiyarsa zai tona...!

Yazeed yaji zuciyarsa kaman zata buga Dan babu abinda zai iyayiwa kansa... Ya shiga shure shure da k’arfin gaske har dai ya samu ya finciki drip d’in dukda tsananin azaban hannayensa da yakeji... Amma dole ya daure koda jini zai b’alle a jikinsa ne sai yaje ya tunk’ari Mahmood ya tarwatsa zuciyarsa kaman yanda nasa rayuwar Ta tarwatse... Haka ya lallab’a ya sauk’o daga saman gado babu hannaye... Taimakonsa d’aya Waziri ya mance k’ofa a bud’e nan yabi ta k’ofar yana tafe yana ciza labb’a sabida tsananin azaban da hannayensa ke masa, zafin zuciya irin nasa da tsanar Mahmood bazai bari ya zauna a asibiti Mahmood yana can yana jubilating nakasan da yayi ba...
A haka ya fito yana bin garu yana satan idon mutane har ya samu ya fito haraban waje... Nan ya iske Waziri na k’ok’arin shigewa Mota... Cikin sauri Yazeed ya nufi Waziri yana furta “Kai Oldtimer..! Kai Dattijo..!!”

Waziri na k’ok’arin kutsa kai Mota dan baiyi zaton zaiga Yazeed ba, Yazeed ya k’araso yana hakin azaba lokaci guda yake furta “Kana jina wllhi ko ka d’aukeni ka kaini masarauta ko kaima na tona maka asiri kaci amanan amininka ka nemi matarsa har kun haihu... Kasan ni a halin yanzu I’ve got nothing to lose..! My whole life is already ruined... Abokin tafiya nake nema shiyasa zan fuskanci Mahmood na sanar dashi asalinsa..! Idan kana son kanka da lafiya, idan baka so ka tafi k’asa taredani da Mahmood, Toh ka d’aukeni ka kaini Masarautar nan,.. Kuma Kai banda abinka, idan naje Masarauta na tona asalin wanene Mahmood ai Kasuwarka ce Waziri, kaga watak’ila sarauta ta fice daga ahalin AbdulJabbar ta har abada Kaga shikenan ka samu tsuntsu a sama gasasshe... All thanks to your Bastard Son, at least ko ban maka noma ba na baka abinda yafi Gonakin ka da ‘ya’yanka suka jima suna noma maka..! Na baka sarautar k’asar baki d’aya...! Ko ya kace Old geezer.. Kaga watak’ila nayi recognizing d’inka as Uba..!!” Ya k’arashe muguwar murmushin nan nasa saman fuskarsa...

Waziri ya shiga Washe baki yana furta “Allah koh Yarima..! Kuma fah kaima ka kawo wani shawari... Idan na zama Sarki shikenan batu yayi dad’i, duk Sadaukarwa da mahaifiyarka tayi bai tafi a banza ba..! Shige muje..!” Ya k’arashe yana mai bud’e ma Yazeed d’in marfin Mota....

**
Chapter 125 · 0% Book details