Sashe 88
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya katseta da fad’in “Come up with something.. Ba Yayarki tana Masarautar ba, kuma akasarin zamanki tinda yayarki tai aure ya dawo wannan Masarautar ne..Sai kisan k’aryar da zakiyi kizo idan kuma ba haka ba..?!” Yai wata murmushi ba tareda yace komai ba...
Cikeda k’osawa tace “Fine naji... Zanga mai zan iyayi...!”
Yazeed yace “Bawai zakiga mai zaki iyayi bane... Dole Ki Zo, ko dan samun zaman lafiyarki da kwanciyar hankalinki.. Mu had’u gobe a yanda muka saba had’uwa..!!”Daga haka katse kiran yai ba tareda ya kuma sauraronta ba...
Muhibbah dake mak’ale jikin staircase tsaf taji tattaunawar Yazeed da Raheema, cikin sand’a tai k’ok’arin ficewa daga sashen ta fasa shigewa...
D’aki Ta komo tana tinanin mafita, ta tina Yazeed yaceda Raheema su had’u gobe a yanda suka saba had’uwa basai ta shigo Masarautar ba dan gudun maganganun mutane... Hakan zaisa babu wanda zai gane ma tazo Masarautar koda kuwa Yayartace Gimbiya Zeenat...
Muhibbah ta k’ume a d’aki tana tinanin abinyi, wata dabarace Ta fad’o mata... Kai tsaye D’akin Zahra ta tafi yanda ta tadda Zahran na baiwa wasu bayi guda biyu umarnin su sorting wasu stuff d’inta alamun ta saduda ta soma shirya kayayyakinta dan tafiya k’asar Spain dake gabansu... Tana ganin Muhibbah ta sakar mata murmushi ta isa gareta... Muhibbah ta dubeta ta dubi Kuyangin guda biyu dake shirya kayayyakin Zahra.. Ta d’an waro idanu waje tace “Kin fara parking already..?!”
Zahra ta d’an tab’e baki tace “Kind of... Since I don’t have a choice...!”
Muhibbah Ta sakar mata murmushi wanda yafi kama da yak’e... Zahra tai alama wa Kuyangin suka fice... Lokaci guda Muhibbah Ta janyo hannunta suka zauna saman sofa....
Muhibbah tai gyaran murya kad’an tana mai tsare Zahran da idanu tace “Do you really want to leave...?!”
Zahra ta fuzar da iska kad’an tace “Only because I don’t have a choice..I’m doing this for my Paa... Idan tani ce baniso ya auri matar nan balle har mu bar k’asar nan tareda ita...!”
Muhibbah Ta jinjina kai tace “Ki kwantar da hankalinki Zahra... You’re not leaving, and your Paa is not getting married to that woman... I promise you..!”
Zahra Ta dubeta da mamaki tace “But how...?!”
Muhibbah Ta kuma gyara zama tace “I’ve a plan... matso kusa kiji..!”
Babu musu Zahra ta matso kusanta sosai... Take Ta sanar da Zahran abinda ta shirya a zuciyarta...
Cikin Rashin fahimtar abinda Muhibbar Ke nufi Zahra tace “But idan yak’i zuwa fah ...?!”
Muhibbah ta murmusa tace “Ke kad’aice wani abu zai sameki ya bar dik abinda yake ya fito.. So bazaiki’i zuwa ba...!”
Zahra ta d’anyi jim tace “Toh Wai mai zaije gani... I’m lost..!”
Muhibbah Ta kuma murmusawa tace “Abinda zai hanasa auren matar da baki so ya aura shi zai gani... All you need to do is to trust me and stick to our plan... Kin fahimta...?!”
Zahra ta jinjina kai a hankali tace “I trust you... Na yarda dake Tia...!”
Muhibbah Ta murmusa tace “Tomorrow in the evening..!”
Jinjina mata kai Zahra tai tace ta fahimta...
Da wannan shawari Muhibbah harmada Zahran suka sami bacci mai kyau...
***
Washe gari Zahra ta sami mahaifinta da batun tana so taje ta duba Uncle d’inta Fu’ad a asibiti kafin su bar k’asar...
Mahmood ya amince mata amma da sharad’in Umaima ko Jakadiya d’aya zatai mata rakiya....
Zahra Ta marairaice fuska tace “Paa fah harda gidajen k’awayena zan zaga nai masu sallama, ni banson rakiyar kowa...!”
Da wutsiyar idanu ya dubeta, dak’ik’a guda Ta gifta kana ya girgiza kai yace “Bana son gardama...!!”
Ta sadda kanta k’asa kad’an tace “Alright zan fad’iwa Jakadiya..!!”
Bai tankata ba saima kiran Hadiminsa da yai... Hadimin ya k’araso ya zube yana kwasan gaisuwa...
Mahmood dake tsaye hannayensa hard’e ta baya ya bud’e murya kad’an yace “Barde aimin ison Jakadiya..!!”
Barde ya d’ago hannu alamun jinjina “Allah shi taimakeka..! An gama Rankaidad’e..!!” Ya mik’e da sauri a durk’ushe ya fice isar da sak’on shugabansa...
Zahra ta saki baki kurum tana duban mahaifin nata wanda ga dukkan alamu mulkin ya soma ratsa jikinsa, tayi imani da a baya ne iyaka abinda take so shi za’ai amma yanzu abubuwa yake irinta masu ji da Mulki... Ta had’iyi miyau da k’yar dan idan dai da Jakadiya za’ai tafiyar shirinsu da Muhibbah zai b’aci... Yanzu mai zatai..?
Batakaiga samo amsa ba Jakadiya Ta shigo a duk’e tana gaida Sarki...
Mahmood yai gyaran murya kad’an ya ambato sunan Jakadiya
“Allah shi baka yawan rai...!!” Jakadiya ta fad’i tana mai kuma risinawa alamun amsawa...
“A tafi da ita duk yanda take so, karki rabu da ita daidai da dak’ik’a guda...!!”
Jakadiya ta kuma risinawa bayan ta dubi Zahra dake tsaye gefen Babanta kana tace “An gama Rankaidad’e.. In sha Allahu ko k’uda bazai tab’a ta ba...!!”
Zahra ta narkama Jakadiya harara dan yanda bata k’aunar Kakarta Giwa haka bata k’aunar Jakadiya....
Ya jinjina masu kai had’ida basu izinin fita....
Tana fitowa ta turawa Muhibbah sak’o cewa Paa d’inta ya k’yaleta taje asibiti duba Fu’ad amma harda rakiyar Jakadiya...
Muhibbah ta ida karance sak’on had’ida rintse idanunta dan babu Jakadiya a tsarin nasu, kasancewarta ka iya b’ata komai...
Sak’o Zahra ta kuma turo mata _What do I do..?_
Dafe kanta tai tana tinanin abinyi... Kaman ance ta kalli can gefe da yanda take tsaye Ta hango Jamal kishingid’e cikin rumfar shak’atawa ta alfarma yana juya wani guntun k’yalle a hannunsa, Ta tsare k’yallen da idanunta daga nan yanda take lab’e... Ko shakka babu ta fahimci k’yallen mayafinta ne da ya gutsire sanda ta haye saman ginin benen b’angaren Jamal d’in lokacinda take binciken Zanen ginin gidan sarauta dake wajen Jamal d’in....Wato ya d’auki k’yallen kenan yana neman mai tufafin... Tabbas idan yasan wanene mai Tufafin zai fahimci tana masa binciken k’wak’waf ne... Bazata bari ya kamata ba... Amma mai zatai... Take tinanin Jakadiya ya fad’o mata... Ta tina cikin labarin da Fu’ad ya bata Jakadiya itace ta d’auketa ta kaitama wancan tsinannen bokan wanda yaso k’ara aikata alfasha da ita akan wanda ‘ya’yan Sarkin suka mata.... Take taji wani irin tsanar Jakadiya na kuma taso mata... Tabbas Jakadiya yau zata karb’i nata itama wajen Jamal... Ba tareda d’aukan doka a hannunta ba Jamal zai zartar mata da nata hukuncin, dan yanda taga fuskar nan nasa babu alamun rahama tasan idan ya kama mai tufafin nan bazai masa da dad’i ba....
Sak’o ta turama Zahra cewa tazo sashen bak’i ta sameta kafin su fice amma kada ta sanar da Jakadiya ga yanda zataje...
Zahra tai yanda Muhibbar tace... Ta dubi Jakadiya tace ta jirata nan tana zuwa...
Jakadiya Ta jinjina kai tace an gama Rankaidad’e....
Zahra ta iso jikin k’ofar Muhibbah tai knocking a hankali...
Muhibbah Ta lek’o kana Ta janyo hannunta zuwa cikin parlorn...
Ga mamakin Zahra wani mayafi Muhibbah Ta mik’a mata...
Zahra ta juya mayafin tace “Mai zanyi da wannan...?!”
Muhibbah tace “A tsarinmu Babu Jakadiya ciki... Wannan mayafin shi zai hana Jakadiya daga ficewa cikin Masarautar nan... Ki bata kice ta yafashi ke bazaki fice da ita tagajan magajan ba ana kallonku haka.... Idan ta yafa kubi ta k’ofar Shataletale (Yanda Jamal Ke zaune)..”
Zahra dai bata fahimci komai ba amma Ta sami kanta da yin yanda Muhibbar Ta umarta... Sai juya mayafin take hannunta har ta iso yanda ta bar Jakadiya na jiranta...
Tana k’arasowa Jakadiya tai mata jinjina da gaisuwa....
Zahra Ta sakar mata murmushi kana Ta mik’a mata mayafin dake hannunta tace ta yafa shi...
Jakadiya Ta shiga juya mayafin tana mai furta “Allah shi taimakeki wannan ai naku ne masu mulki, Ina na isa yafa wannan Ina talakarku...!”
Zahra ta murmusa tace “Karki damu Jakadiya, dukkanmu da kike gani d’aya muke a wajen Allah, idan ma kinfini tsoron Allah sai ki fini matsayi wajensa... Dukkanninmu bayin Allah ne.. Ke ‘yaradam ce kaman ni... So ki karb’a kawai ki yafa babu wani abu...!”
Jakadiya tai mata K’uri tana dubanta cikin tsananin sanyin jiki, tinda take a Masarautar ba’a tab’a karramata irinta yau ba... Bata tab’a jin tanada daraja a matsayinta Ta ‘yaradam kaman yau ba... Allah sarki sai ta tuna jik’onda Giwa tasa taita d’irkawa matar Yarima Mahmood Aliya wanda ya lalata mahaifarta kuma sukeda tabbacin bazata tab’a haihuwa ba... Sunada tabbacin Zahra ba d’iyar Aliya bace dan Tal’udu ya tabbatarwa Giwa Aliyar bazata tab’a haihuwa ba duk asibitin duniya da zasuje shisa koda suka dawo da Zahra k’asar a matsayin d’iyarsu sukeda shakku da alamun tambaya akan yarinyar.. Amma dai abinda yarinyar nan tai mata yau tayi imani d’iyar halak ce koda kuwa ta wata hanyar aka sameta... Zahra ce ta katse mata tinanin da fad’in subi ta k’ofar Shataletale... Suna tafe tana jan Jakadiya da hira....
Jakadiya sai Washe baki take tana jin kanta tamkar ‘yantacciya musamman data rufa mayafi irinta masu Mulki...
Daga can yanda take kishingid’e a Rumfar hutawarsu Ta ‘ya’yan sarakuna yana mai ci gaba da juya k’yallen ya hango Jakadiya da Zahra na tahowa...
Ya k’urama Jakadiya idanu da mayafin dake kanta, ya kuma juya k’yallen dake hannunsa... Lokaci guda ya shiga jinjina kai... Wato Jakadiya ce mai masa bincike a d’akinsa... Alk’awari ya d’auka idan ya kama mai masa binciken k’wak’waf d’in nan sai ya hukuntasa hukunci mai tsauri dan shi a nasa tsarin babu yafiya, duk wanda ya shiga gonarsa sai ya hukunta sa, hakan yasa ya hukunta Ja’afar sannan Majidad’i ma bai mance dashi ba h’d definitely get what’s coming for him... Yanzu ma dole ya hukunta Jakadiya... Ya k’arashe yana sakin huci...
Bawa guda dake tsaye gefensa yai masa alama yazo.... Take ya basa umarnin yai masa kiran Jakadiya...
Bawan ya tafi yayi yanda Jamal yace.. A tare Zahra da Jakadiya suka k’araso... Jakadiya ta zube tana kwasan gaisuwa...
Zahra ma Ta gaida Uncle d’in nata da sakin fuska....
Jamal ya tambayeta Ina suka nufa..? Yana tambayar yana k’arema mayafin Jakadiya kallo dan tabbatarda zarginsa har dai idanunsa suka sauk’a kan yanda gutsirin k’yallen ya fice... Ta tabbata Jakadiya ce mai masa binciken sirri watak’ila ma bakinsu d’aya da Ubandoma ita ta had’a baki da Ubandoma suka kub’utar da Ja’afar....
Ya dubi Zahra yace “Princess, gashi kuwa inaso Jakadiya tai min wani aiki... Ko na had’aki da wata Hadimace Ta rakaki...?!”
Cikeda k’osawa tace “Fine naji... Zanga mai zan iyayi...!”
Yazeed yace “Bawai zakiga mai zaki iyayi bane... Dole Ki Zo, ko dan samun zaman lafiyarki da kwanciyar hankalinki.. Mu had’u gobe a yanda muka saba had’uwa..!!”Daga haka katse kiran yai ba tareda ya kuma sauraronta ba...
Muhibbah dake mak’ale jikin staircase tsaf taji tattaunawar Yazeed da Raheema, cikin sand’a tai k’ok’arin ficewa daga sashen ta fasa shigewa...
D’aki Ta komo tana tinanin mafita, ta tina Yazeed yaceda Raheema su had’u gobe a yanda suka saba had’uwa basai ta shigo Masarautar ba dan gudun maganganun mutane... Hakan zaisa babu wanda zai gane ma tazo Masarautar koda kuwa Yayartace Gimbiya Zeenat...
Muhibbah ta k’ume a d’aki tana tinanin abinyi, wata dabarace Ta fad’o mata... Kai tsaye D’akin Zahra ta tafi yanda ta tadda Zahran na baiwa wasu bayi guda biyu umarnin su sorting wasu stuff d’inta alamun ta saduda ta soma shirya kayayyakinta dan tafiya k’asar Spain dake gabansu... Tana ganin Muhibbah ta sakar mata murmushi ta isa gareta... Muhibbah ta dubeta ta dubi Kuyangin guda biyu dake shirya kayayyakin Zahra.. Ta d’an waro idanu waje tace “Kin fara parking already..?!”
Zahra ta d’an tab’e baki tace “Kind of... Since I don’t have a choice...!”
Muhibbah Ta sakar mata murmushi wanda yafi kama da yak’e... Zahra tai alama wa Kuyangin suka fice... Lokaci guda Muhibbah Ta janyo hannunta suka zauna saman sofa....
Muhibbah tai gyaran murya kad’an tana mai tsare Zahran da idanu tace “Do you really want to leave...?!”
Zahra ta fuzar da iska kad’an tace “Only because I don’t have a choice..I’m doing this for my Paa... Idan tani ce baniso ya auri matar nan balle har mu bar k’asar nan tareda ita...!”
Muhibbah Ta jinjina kai tace “Ki kwantar da hankalinki Zahra... You’re not leaving, and your Paa is not getting married to that woman... I promise you..!”
Zahra Ta dubeta da mamaki tace “But how...?!”
Muhibbah Ta kuma gyara zama tace “I’ve a plan... matso kusa kiji..!”
Babu musu Zahra ta matso kusanta sosai... Take Ta sanar da Zahran abinda ta shirya a zuciyarta...
Cikin Rashin fahimtar abinda Muhibbar Ke nufi Zahra tace “But idan yak’i zuwa fah ...?!”
Muhibbah ta murmusa tace “Ke kad’aice wani abu zai sameki ya bar dik abinda yake ya fito.. So bazaiki’i zuwa ba...!”
Zahra ta d’anyi jim tace “Toh Wai mai zaije gani... I’m lost..!”
Muhibbah Ta kuma murmusawa tace “Abinda zai hanasa auren matar da baki so ya aura shi zai gani... All you need to do is to trust me and stick to our plan... Kin fahimta...?!”
Zahra ta jinjina kai a hankali tace “I trust you... Na yarda dake Tia...!”
Muhibbah Ta murmusa tace “Tomorrow in the evening..!”
Jinjina mata kai Zahra tai tace ta fahimta...
Da wannan shawari Muhibbah harmada Zahran suka sami bacci mai kyau...
***
Washe gari Zahra ta sami mahaifinta da batun tana so taje ta duba Uncle d’inta Fu’ad a asibiti kafin su bar k’asar...
Mahmood ya amince mata amma da sharad’in Umaima ko Jakadiya d’aya zatai mata rakiya....
Zahra Ta marairaice fuska tace “Paa fah harda gidajen k’awayena zan zaga nai masu sallama, ni banson rakiyar kowa...!”
Da wutsiyar idanu ya dubeta, dak’ik’a guda Ta gifta kana ya girgiza kai yace “Bana son gardama...!!”
Ta sadda kanta k’asa kad’an tace “Alright zan fad’iwa Jakadiya..!!”
Bai tankata ba saima kiran Hadiminsa da yai... Hadimin ya k’araso ya zube yana kwasan gaisuwa...
Mahmood dake tsaye hannayensa hard’e ta baya ya bud’e murya kad’an yace “Barde aimin ison Jakadiya..!!”
Barde ya d’ago hannu alamun jinjina “Allah shi taimakeka..! An gama Rankaidad’e..!!” Ya mik’e da sauri a durk’ushe ya fice isar da sak’on shugabansa...
Zahra ta saki baki kurum tana duban mahaifin nata wanda ga dukkan alamu mulkin ya soma ratsa jikinsa, tayi imani da a baya ne iyaka abinda take so shi za’ai amma yanzu abubuwa yake irinta masu ji da Mulki... Ta had’iyi miyau da k’yar dan idan dai da Jakadiya za’ai tafiyar shirinsu da Muhibbah zai b’aci... Yanzu mai zatai..?
Batakaiga samo amsa ba Jakadiya Ta shigo a duk’e tana gaida Sarki...
Mahmood yai gyaran murya kad’an ya ambato sunan Jakadiya
“Allah shi baka yawan rai...!!” Jakadiya ta fad’i tana mai kuma risinawa alamun amsawa...
“A tafi da ita duk yanda take so, karki rabu da ita daidai da dak’ik’a guda...!!”
Jakadiya ta kuma risinawa bayan ta dubi Zahra dake tsaye gefen Babanta kana tace “An gama Rankaidad’e.. In sha Allahu ko k’uda bazai tab’a ta ba...!!”
Zahra ta narkama Jakadiya harara dan yanda bata k’aunar Kakarta Giwa haka bata k’aunar Jakadiya....
Ya jinjina masu kai had’ida basu izinin fita....
Tana fitowa ta turawa Muhibbah sak’o cewa Paa d’inta ya k’yaleta taje asibiti duba Fu’ad amma harda rakiyar Jakadiya...
Muhibbah ta ida karance sak’on had’ida rintse idanunta dan babu Jakadiya a tsarin nasu, kasancewarta ka iya b’ata komai...
Sak’o Zahra ta kuma turo mata _What do I do..?_
Dafe kanta tai tana tinanin abinyi... Kaman ance ta kalli can gefe da yanda take tsaye Ta hango Jamal kishingid’e cikin rumfar shak’atawa ta alfarma yana juya wani guntun k’yalle a hannunsa, Ta tsare k’yallen da idanunta daga nan yanda take lab’e... Ko shakka babu ta fahimci k’yallen mayafinta ne da ya gutsire sanda ta haye saman ginin benen b’angaren Jamal d’in lokacinda take binciken Zanen ginin gidan sarauta dake wajen Jamal d’in....Wato ya d’auki k’yallen kenan yana neman mai tufafin... Tabbas idan yasan wanene mai Tufafin zai fahimci tana masa binciken k’wak’waf ne... Bazata bari ya kamata ba... Amma mai zatai... Take tinanin Jakadiya ya fad’o mata... Ta tina cikin labarin da Fu’ad ya bata Jakadiya itace ta d’auketa ta kaitama wancan tsinannen bokan wanda yaso k’ara aikata alfasha da ita akan wanda ‘ya’yan Sarkin suka mata.... Take taji wani irin tsanar Jakadiya na kuma taso mata... Tabbas Jakadiya yau zata karb’i nata itama wajen Jamal... Ba tareda d’aukan doka a hannunta ba Jamal zai zartar mata da nata hukuncin, dan yanda taga fuskar nan nasa babu alamun rahama tasan idan ya kama mai tufafin nan bazai masa da dad’i ba....
Sak’o ta turama Zahra cewa tazo sashen bak’i ta sameta kafin su fice amma kada ta sanar da Jakadiya ga yanda zataje...
Zahra tai yanda Muhibbar tace... Ta dubi Jakadiya tace ta jirata nan tana zuwa...
Jakadiya Ta jinjina kai tace an gama Rankaidad’e....
Zahra ta iso jikin k’ofar Muhibbah tai knocking a hankali...
Muhibbah Ta lek’o kana Ta janyo hannunta zuwa cikin parlorn...
Ga mamakin Zahra wani mayafi Muhibbah Ta mik’a mata...
Zahra ta juya mayafin tace “Mai zanyi da wannan...?!”
Muhibbah tace “A tsarinmu Babu Jakadiya ciki... Wannan mayafin shi zai hana Jakadiya daga ficewa cikin Masarautar nan... Ki bata kice ta yafashi ke bazaki fice da ita tagajan magajan ba ana kallonku haka.... Idan ta yafa kubi ta k’ofar Shataletale (Yanda Jamal Ke zaune)..”
Zahra dai bata fahimci komai ba amma Ta sami kanta da yin yanda Muhibbar Ta umarta... Sai juya mayafin take hannunta har ta iso yanda ta bar Jakadiya na jiranta...
Tana k’arasowa Jakadiya tai mata jinjina da gaisuwa....
Zahra Ta sakar mata murmushi kana Ta mik’a mata mayafin dake hannunta tace ta yafa shi...
Jakadiya Ta shiga juya mayafin tana mai furta “Allah shi taimakeki wannan ai naku ne masu mulki, Ina na isa yafa wannan Ina talakarku...!”
Zahra ta murmusa tace “Karki damu Jakadiya, dukkanmu da kike gani d’aya muke a wajen Allah, idan ma kinfini tsoron Allah sai ki fini matsayi wajensa... Dukkanninmu bayin Allah ne.. Ke ‘yaradam ce kaman ni... So ki karb’a kawai ki yafa babu wani abu...!”
Jakadiya tai mata K’uri tana dubanta cikin tsananin sanyin jiki, tinda take a Masarautar ba’a tab’a karramata irinta yau ba... Bata tab’a jin tanada daraja a matsayinta Ta ‘yaradam kaman yau ba... Allah sarki sai ta tuna jik’onda Giwa tasa taita d’irkawa matar Yarima Mahmood Aliya wanda ya lalata mahaifarta kuma sukeda tabbacin bazata tab’a haihuwa ba... Sunada tabbacin Zahra ba d’iyar Aliya bace dan Tal’udu ya tabbatarwa Giwa Aliyar bazata tab’a haihuwa ba duk asibitin duniya da zasuje shisa koda suka dawo da Zahra k’asar a matsayin d’iyarsu sukeda shakku da alamun tambaya akan yarinyar.. Amma dai abinda yarinyar nan tai mata yau tayi imani d’iyar halak ce koda kuwa ta wata hanyar aka sameta... Zahra ce ta katse mata tinanin da fad’in subi ta k’ofar Shataletale... Suna tafe tana jan Jakadiya da hira....
Jakadiya sai Washe baki take tana jin kanta tamkar ‘yantacciya musamman data rufa mayafi irinta masu Mulki...
Daga can yanda take kishingid’e a Rumfar hutawarsu Ta ‘ya’yan sarakuna yana mai ci gaba da juya k’yallen ya hango Jakadiya da Zahra na tahowa...
Ya k’urama Jakadiya idanu da mayafin dake kanta, ya kuma juya k’yallen dake hannunsa... Lokaci guda ya shiga jinjina kai... Wato Jakadiya ce mai masa bincike a d’akinsa... Alk’awari ya d’auka idan ya kama mai masa binciken k’wak’waf d’in nan sai ya hukuntasa hukunci mai tsauri dan shi a nasa tsarin babu yafiya, duk wanda ya shiga gonarsa sai ya hukunta sa, hakan yasa ya hukunta Ja’afar sannan Majidad’i ma bai mance dashi ba h’d definitely get what’s coming for him... Yanzu ma dole ya hukunta Jakadiya... Ya k’arashe yana sakin huci...
Bawa guda dake tsaye gefensa yai masa alama yazo.... Take ya basa umarnin yai masa kiran Jakadiya...
Bawan ya tafi yayi yanda Jamal yace.. A tare Zahra da Jakadiya suka k’araso... Jakadiya ta zube tana kwasan gaisuwa...
Zahra ma Ta gaida Uncle d’in nata da sakin fuska....
Jamal ya tambayeta Ina suka nufa..? Yana tambayar yana k’arema mayafin Jakadiya kallo dan tabbatarda zarginsa har dai idanunsa suka sauk’a kan yanda gutsirin k’yallen ya fice... Ta tabbata Jakadiya ce mai masa binciken sirri watak’ila ma bakinsu d’aya da Ubandoma ita ta had’a baki da Ubandoma suka kub’utar da Ja’afar....
Ya dubi Zahra yace “Princess, gashi kuwa inaso Jakadiya tai min wani aiki... Ko na had’aki da wata Hadimace Ta rakaki...?!”