Sashe 121
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A b’angare guda tun fitowar da yayi daga Bauchi sai yanzu Allah yayi isowarsa, mota ta b’aci masa a hanya sannan ya rasa mai gyara ya kuma rasa wanda zai tsaya ya taimaka masa, gashi dama ba isasshen lafiya bane dashi tinda daga asibiti ya cire ruwan drip ya fito sam babu wani k’arfi jikinsa, bashi ya samu isowa garin Jos ba sai wannan lokaci dan da kam ma ya yanke shawarin tsayawa a Toro ya kwana ne amma sai yaji inaa bazai Iya kwana baisan halinda Muhibbah ke ciki a wannan masarauta ba hakan yasa ya k’udiri niyyan komin dare sai ya shiga Jos da izinin Allah... Daidai yanda suka saba parking idan ya kawota a wajen yayi parking can tsallake da Masarautar... Yayi tsaye yana tinanin abinyi, ta yaya zai doshi Masarautar ba tareda an tambayesa wanene shi daga ina yake kuma wajen waye zai jesa, yasan by now Umaima zata iya fahimtar shid’in ya mata k’arya, Toh ta yaya zai shige Masarautar bata hanyar Umaima ba... Kodashike ita d’in tana da zuciya mai kyau watak’ila tansauraresa ta kuma basa uzuri... Take ya lalaumo wayarsa cikin mota ya soma dialing layin Umaima..! Saidai sam wayar tata bata shiga... Dafe kansa yayi a hankali had’ida jefa wayar cikin mota dan shima wayar tasa chaji gab take da k’arewa... Ya fuzar da fuci yana tunanin abinyi ya wane irin jiri dake neman kaisa k’asa dan tun bayan drip d’in babu wani abu da ya saka cikinsa..! Wata zuciya tace tsayuwa a nan bai ganka ba Ansar Muhibbah tana cikin Masarautar nan kuma tana tsananin buk’atarka ka shiga kawai ka fito da ita komai ta fanjama fanjam, komai zai faru kawai saidai ya faru but ya zama dole ka shiga ka ceto masoyiyarka...! Da wannan tunani Ansar ya nufi Masarautar yana tafe ko ganin gabansa baiyi....
A daidai lokacinda su Mahmood suka doso Masarautar suma.. Turaki ne kawai ya hango mutum yana tafe bisa kwalta tamkar mai tab’in hankali shikam Mahmood sam baiga mutum ba dukda cewa hasken wutan streetlights sun haske ko ina... Turaki fad’i yake “Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..! Watch out your Highness..!!” Inaaa sam Mahmood baima saurari abinda Turaki Ke fad’i masa ba saiji yayi ya d’auke mutum da k’arfin gaske...! Ya taka burki babu shiri Allah yasa babu wata motar ma bayanshi da shike wannan close d’in babu gidan kowa wajen ba kuma hanyar wucewa zallan Masarauta ce kawai a wajen...!
A tare suka fito suna duba mutumin da suka bige... Turaki ya d’an tab’asa yana furta “Kaman yana numfashi Your Highness.. Muyi gaggawan kaisa asibiti mafi kusa..!”
Cikin sauri Mahmood d’in ya taimakawa Turaki suka ciccib’i mutumin suka saka bayan Mota... Babu shiri Turaki ya amshi makullin motar suka nufi wani privare hospital da baida nisa sosai da Masarautar...
**
A can asibiti wajen Yazeed kuwa gaba d’aya Giwa ji take kaman an mintsileta, Ta kasa zaman asibitin Ta kuma kasa komawa Masarauta, batasan dalili ba amma zuciyarta sai yankewa yake yana bugawa yanda kasan ana sauk’e mata shirgegen guduma saman k’irjinta haka takeji... Ga wani irin muguwar k’aik’ayi da bata tab’a jin irinsa ba tsawon rayuwarta, hannunta nayi kanta nayi... Ta gaza zama ta gaza tsayuwa, gaba d’aya Giwa ba a hayyacinta take ba ta alak’anta hakan da asirinsu da Fu’ad ya tona wajen Mahmood..!
Jamal ya da shima hankalinsa ba’a kwance yake ba ya k’araso ga mahaifiyar tasa cikin cangwala sandarsa, ya tsaya dab da ita yana muzurai yake furta “Maami meye abinyi yanzu da Yaya yasan laifin da muka aikata shekarun baya... Maami jikina na bani Yaya bazai dakata ba until he seek justice for what happened to that girl, koda kuwa mu d’in ahalinsa ne.. Maami kin sanshi kinfi kowa saninsa tinda Ke kika haifesa...!”
Cikin tashin hankali Giwa dake faman soshe soshe Ta katse Jamal da fad’in “Bani na haifesa ba kar ka sake cewa ni na haifi wannan tsinannen yaron... D’anda na haifa bazai tab’a kiranada ‘yar ta’adda ba...!!!”
Cikin rashin gane ina kalamanta suka dosa Jamal yace “Maami ban gane ba... Ban fahimta ba...! Yaya ne fah..! Yaya Mahmood nake nufi..!!”
Cikin daka tsawa Giwa tace “Uban Yaya Mahmood ne ba Yaya Mahmood ba... Allah yasa Mahmooda Uban AbdulJabbar ne..! Kai nace maka bani na haifesa ba kar ka sake cewa d’ah na ne..!!” Ta k’arashe tana mai ci gaba da susa...!
Jamal yasha jinin jikinsa yana dubanta cikeda tsoro saikace wata sabuwar kamu..! Koda shike k’ila fushi take da Mahmood d’in shisa take ambatonsa da cewa ba ita ta haifesa ba..! Ya d’anyi shiru sai kuma yace “Maami ya kamata mu koma masarauta Kinsan akwai aikin da bamu k’arasa ba can Masarautar..!”
Nan ma katsesa Giwa tayi da fad’in “Kai nace maka bazamu bar asibtin nan ba sai Yazeed ya farka..! ko ni ko kai babu mai barin asibitin nan sai mun tabbata d’an uwanka ya farfad’o, ince da handcuffs ka d’aure yarinyar toh uban waye zai kwanceta...!!”
Jamal ya kuma jinjina kai a hankali yana kallon bak’on lamari daga mahaifiyar tasa... Bai kuma cewa komai ba sai komawa gefe da yayi...!
Can Giwa ta hango Waziri ashe Shima ya kasa tafiya yana nan yana jiran farfad’owar Yazeed... Giwa tana ganin giftawarsa tai saurin bin hanyar da yabi...
Koda Jamal dake fakaice da ita yaga tabi bayan Waziri sai shima ya saci idon Jakadiya yabi bayan mahaifiyarsa a hankali...
Tsaye yayi ya lab’e yana sauraren tattaunawar Giwa da Waziri...
Cikin k’unan rai Giwa ke ci gaba da fad’in “Saida nace kabi bayansa ka dakatar dashi, Wannan duk laifinka ne... Ka kasa dakatar dashi... Da ace ka dakatar dashi da yanzu d’anmu yana nan da lafiyarsa, da yanzu bai rasa hannayensa ba balle ‘ya’yansa... Idan Yazeed ya farka bazai tab’a yafe maka ba kuma bazai tab’a amsarka a matsayin mahaifi ba...!”
Cikin tashin hankali Waziri Ke fad’in “Ki dakata ki saurareni Turai, Yazeed ni na basa jini ni na taimaki d’anmu na basa jini akai masa aiki, da ace banyi gaggawan basa jinina ba k’ila da yanzu mun rasashi gaba d’aya.. Ki gode ma Allah ki gode min har yanzu Yazeed yana numfashi...!”
Cikin karaji Giwa Ke fad’in “Meye abin godiya a nan bayan kasa d’anmu ya zama muskini shikenan haka zai tashi yaga ya rasa hannayensa.. Duk burin sarautar da naci masa yanzu bazai samu ba..! Ka cuceni Waziri... Ka cuci D’anka Yazeed..!!”
Kaman daga sama suka sinkayo muryar Jamal cikin wane irin yanayi yana furta “Maami did I hear it right..! Naji da kyau cewa Yazeed d’an Waziri ne..?!!”
Daga Giwa har Waziri aka rasa mai basa amsa...Jamal dake ci gaba da sakin huci ya k’araso gaban Giwa sosai yana furta “Answer me..! Ki amsa min...! Yazeed d’an Waziri ne..?!”
Giwa bata iya furta komai ba sai muzurai.. Ya kuma d’aga murya yana jefo mata tambayar... Waziri ne ya basa amsa da fad’in “K’warai abinda kaji haka ne Jamal... Yazeed d’ah na ne da mahaifiyarka....!!”
Cikin tsananin Shock yake duban Giwa zuciyarsa na kuma tsinkewa har wani irin rawa jikinsa keyi, kana iya hango hakan daga sandar crotchets d’insa yanda sandar ke rawa kaman zai dungurar da Jamal d’in k’asa..!
Cikin wane irin yanayi yake girgiza kai yana duban Giwa “You tell me what really happened..! You tell me ta yaya wannan mutumin ya zamto mahaifin d’an uwana da muka fito ciki guda muka girma a matsayin ‘yan uwa da suka had’a duka iyaye biyu..! Maami ki bud’e baki ki sanar dani..!!” Ya k’arashe hawaye na gangaro masa cikin tsananin k’unan rai...!
Giwa dake danne kukanta tace “Ya faru ne hakan..! Domin kuwa Waziri shi yake taimaka min da komai wajen ganin na kafa mulki na cikin gidan nan..!”
Jamal ya katseta da fad’in “Shiyasa kikaci amanan mahaifina kika basa kanki...! Maami how could you do this..! Ke fah mai sarauta ce mai Martaba..! Ta yaya zaki aikata k’ask’antaccen laifi irin wannan..!”
Giwa ta katsesa da fad’in “Kada ka yarda ka yanke hukunci akaina domin kuwa baka San kalan rayuwar dana fuskanta a baya ba dan na tabbatar da mulkin nan bai kufce min ba..!”
Cikin huci Jamal d’inma ke furta “Wane mulki kike magana bayan d’an naki ba Magajin mahaifinmu bane... Ince Yazeed kike maganan d’aurawa saman Karagar..? Ashe dama duk son Yaya da kike na k’Arya ne..? Toh idan ba ke kika haifesa ba wacece Ta haifesa..?!”
Giwa Ta basa amsa da fad’in “Wannan ba matsalarka bace a halin yanzu.. Kaidai tinda kasan kaid’in d’ah ne magana ya k’are..!”
Waziri ya katseta da fad’in “Ina magana ya k’are tinda shi baisan waye nasa mahaifin ba..!!”
Ya karkata ya dubi Waziri da tsananin mamaki hawaye naci gaba da gangaro masa lokaci guda ya maidoda dubansaga Giwa yace “Answer his question... Waye mahaifina Giwa...?!”
Hararan Waziri kurum Giwa take kana tace “Mahaifinka Sarki AbdulJabbar ne..!!”
Waziri ya bud’e murya yace “K’arya take maka ita kanta batasan waye mahaifinka ba domin kuwa Ta shiga rud’u a lokacin..!!”
Jamal ya fiddo idanu waje yana duban Giwa lokaci guda yake girgiza kai yana mai furta “You’re unbelievable..! Shin abinda yake fad’i gaskiya ne Giwa..?! Do I need to take a DNA test for me to know who my father is..?!! Answer me Giwa..?! Ki amsa min nace..!!”
Cikin zuban hawaye Giwa Ke jinjina kai tana furta “Gaskiya ne Jamal bansan waye mahaifinka ba...!”
Dakatar da ita yayi ta hanyar d’aga mata hannu yana mai sakin huci yake furta “No..! My father is dead..! My father was King AbdulJabbar... Shine mahaifina... Bazan tab’a zama product na cin amanar da kika masa ba..! You’re a worthless mother..! Mujiyar uwace Ke mai kashe ‘ya’yanta..! Ko baki d’auki wuk’a kin dab’a mana ba kin kashe mu da abinda kika mana... Gaba d’aya rayuwana nayisa ne wajen miki biyayya..! Ashe duka rayuwan nawa k’Arya ne... Babu komai cikinta face k’arya...! Duk fad’i tashin da Kike wajen ganin kin kafa mulkin babu komai a cikin labarin face k’arya..! Kina neman ki d’aura ‘ya’yanki saman Karagar da basuda gado..! Maami kin cuceni kin zalunceni..! Nayi nadaman miki biyayya da nayi a baya dukda ire iren muggan abubuwan da kika sa na dingayi.. Allah ya isa tsakanina dake Giwa.. Kuma yanzu basai anjima ba zanje na kwance yarinyar nan bazan sake miki biyayya ba daidai da dak’ik’a guda..!”
A daidai lokacinda su Mahmood suka doso Masarautar suma.. Turaki ne kawai ya hango mutum yana tafe bisa kwalta tamkar mai tab’in hankali shikam Mahmood sam baiga mutum ba dukda cewa hasken wutan streetlights sun haske ko ina... Turaki fad’i yake “Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..! Watch out your Highness..!!” Inaaa sam Mahmood baima saurari abinda Turaki Ke fad’i masa ba saiji yayi ya d’auke mutum da k’arfin gaske...! Ya taka burki babu shiri Allah yasa babu wata motar ma bayanshi da shike wannan close d’in babu gidan kowa wajen ba kuma hanyar wucewa zallan Masarauta ce kawai a wajen...!
A tare suka fito suna duba mutumin da suka bige... Turaki ya d’an tab’asa yana furta “Kaman yana numfashi Your Highness.. Muyi gaggawan kaisa asibiti mafi kusa..!”
Cikin sauri Mahmood d’in ya taimakawa Turaki suka ciccib’i mutumin suka saka bayan Mota... Babu shiri Turaki ya amshi makullin motar suka nufi wani privare hospital da baida nisa sosai da Masarautar...
**
A can asibiti wajen Yazeed kuwa gaba d’aya Giwa ji take kaman an mintsileta, Ta kasa zaman asibitin Ta kuma kasa komawa Masarauta, batasan dalili ba amma zuciyarta sai yankewa yake yana bugawa yanda kasan ana sauk’e mata shirgegen guduma saman k’irjinta haka takeji... Ga wani irin muguwar k’aik’ayi da bata tab’a jin irinsa ba tsawon rayuwarta, hannunta nayi kanta nayi... Ta gaza zama ta gaza tsayuwa, gaba d’aya Giwa ba a hayyacinta take ba ta alak’anta hakan da asirinsu da Fu’ad ya tona wajen Mahmood..!
Jamal ya da shima hankalinsa ba’a kwance yake ba ya k’araso ga mahaifiyar tasa cikin cangwala sandarsa, ya tsaya dab da ita yana muzurai yake furta “Maami meye abinyi yanzu da Yaya yasan laifin da muka aikata shekarun baya... Maami jikina na bani Yaya bazai dakata ba until he seek justice for what happened to that girl, koda kuwa mu d’in ahalinsa ne.. Maami kin sanshi kinfi kowa saninsa tinda Ke kika haifesa...!”
Cikin tashin hankali Giwa dake faman soshe soshe Ta katse Jamal da fad’in “Bani na haifesa ba kar ka sake cewa ni na haifi wannan tsinannen yaron... D’anda na haifa bazai tab’a kiranada ‘yar ta’adda ba...!!!”
Cikin rashin gane ina kalamanta suka dosa Jamal yace “Maami ban gane ba... Ban fahimta ba...! Yaya ne fah..! Yaya Mahmood nake nufi..!!”
Cikin daka tsawa Giwa tace “Uban Yaya Mahmood ne ba Yaya Mahmood ba... Allah yasa Mahmooda Uban AbdulJabbar ne..! Kai nace maka bani na haifesa ba kar ka sake cewa d’ah na ne..!!” Ta k’arashe tana mai ci gaba da susa...!
Jamal yasha jinin jikinsa yana dubanta cikeda tsoro saikace wata sabuwar kamu..! Koda shike k’ila fushi take da Mahmood d’in shisa take ambatonsa da cewa ba ita ta haifesa ba..! Ya d’anyi shiru sai kuma yace “Maami ya kamata mu koma masarauta Kinsan akwai aikin da bamu k’arasa ba can Masarautar..!”
Nan ma katsesa Giwa tayi da fad’in “Kai nace maka bazamu bar asibtin nan ba sai Yazeed ya farka..! ko ni ko kai babu mai barin asibitin nan sai mun tabbata d’an uwanka ya farfad’o, ince da handcuffs ka d’aure yarinyar toh uban waye zai kwanceta...!!”
Jamal ya kuma jinjina kai a hankali yana kallon bak’on lamari daga mahaifiyar tasa... Bai kuma cewa komai ba sai komawa gefe da yayi...!
Can Giwa ta hango Waziri ashe Shima ya kasa tafiya yana nan yana jiran farfad’owar Yazeed... Giwa tana ganin giftawarsa tai saurin bin hanyar da yabi...
Koda Jamal dake fakaice da ita yaga tabi bayan Waziri sai shima ya saci idon Jakadiya yabi bayan mahaifiyarsa a hankali...
Tsaye yayi ya lab’e yana sauraren tattaunawar Giwa da Waziri...
Cikin k’unan rai Giwa ke ci gaba da fad’in “Saida nace kabi bayansa ka dakatar dashi, Wannan duk laifinka ne... Ka kasa dakatar dashi... Da ace ka dakatar dashi da yanzu d’anmu yana nan da lafiyarsa, da yanzu bai rasa hannayensa ba balle ‘ya’yansa... Idan Yazeed ya farka bazai tab’a yafe maka ba kuma bazai tab’a amsarka a matsayin mahaifi ba...!”
Cikin tashin hankali Waziri Ke fad’in “Ki dakata ki saurareni Turai, Yazeed ni na basa jini ni na taimaki d’anmu na basa jini akai masa aiki, da ace banyi gaggawan basa jinina ba k’ila da yanzu mun rasashi gaba d’aya.. Ki gode ma Allah ki gode min har yanzu Yazeed yana numfashi...!”
Cikin karaji Giwa Ke fad’in “Meye abin godiya a nan bayan kasa d’anmu ya zama muskini shikenan haka zai tashi yaga ya rasa hannayensa.. Duk burin sarautar da naci masa yanzu bazai samu ba..! Ka cuceni Waziri... Ka cuci D’anka Yazeed..!!”
Kaman daga sama suka sinkayo muryar Jamal cikin wane irin yanayi yana furta “Maami did I hear it right..! Naji da kyau cewa Yazeed d’an Waziri ne..?!!”
Daga Giwa har Waziri aka rasa mai basa amsa...Jamal dake ci gaba da sakin huci ya k’araso gaban Giwa sosai yana furta “Answer me..! Ki amsa min...! Yazeed d’an Waziri ne..?!”
Giwa bata iya furta komai ba sai muzurai.. Ya kuma d’aga murya yana jefo mata tambayar... Waziri ne ya basa amsa da fad’in “K’warai abinda kaji haka ne Jamal... Yazeed d’ah na ne da mahaifiyarka....!!”
Cikin tsananin Shock yake duban Giwa zuciyarsa na kuma tsinkewa har wani irin rawa jikinsa keyi, kana iya hango hakan daga sandar crotchets d’insa yanda sandar ke rawa kaman zai dungurar da Jamal d’in k’asa..!
Cikin wane irin yanayi yake girgiza kai yana duban Giwa “You tell me what really happened..! You tell me ta yaya wannan mutumin ya zamto mahaifin d’an uwana da muka fito ciki guda muka girma a matsayin ‘yan uwa da suka had’a duka iyaye biyu..! Maami ki bud’e baki ki sanar dani..!!” Ya k’arashe hawaye na gangaro masa cikin tsananin k’unan rai...!
Giwa dake danne kukanta tace “Ya faru ne hakan..! Domin kuwa Waziri shi yake taimaka min da komai wajen ganin na kafa mulki na cikin gidan nan..!”
Jamal ya katseta da fad’in “Shiyasa kikaci amanan mahaifina kika basa kanki...! Maami how could you do this..! Ke fah mai sarauta ce mai Martaba..! Ta yaya zaki aikata k’ask’antaccen laifi irin wannan..!”
Giwa ta katsesa da fad’in “Kada ka yarda ka yanke hukunci akaina domin kuwa baka San kalan rayuwar dana fuskanta a baya ba dan na tabbatar da mulkin nan bai kufce min ba..!”
Cikin huci Jamal d’inma ke furta “Wane mulki kike magana bayan d’an naki ba Magajin mahaifinmu bane... Ince Yazeed kike maganan d’aurawa saman Karagar..? Ashe dama duk son Yaya da kike na k’Arya ne..? Toh idan ba ke kika haifesa ba wacece Ta haifesa..?!”
Giwa Ta basa amsa da fad’in “Wannan ba matsalarka bace a halin yanzu.. Kaidai tinda kasan kaid’in d’ah ne magana ya k’are..!”
Waziri ya katseta da fad’in “Ina magana ya k’are tinda shi baisan waye nasa mahaifin ba..!!”
Ya karkata ya dubi Waziri da tsananin mamaki hawaye naci gaba da gangaro masa lokaci guda ya maidoda dubansaga Giwa yace “Answer his question... Waye mahaifina Giwa...?!”
Hararan Waziri kurum Giwa take kana tace “Mahaifinka Sarki AbdulJabbar ne..!!”
Waziri ya bud’e murya yace “K’arya take maka ita kanta batasan waye mahaifinka ba domin kuwa Ta shiga rud’u a lokacin..!!”
Jamal ya fiddo idanu waje yana duban Giwa lokaci guda yake girgiza kai yana mai furta “You’re unbelievable..! Shin abinda yake fad’i gaskiya ne Giwa..?! Do I need to take a DNA test for me to know who my father is..?!! Answer me Giwa..?! Ki amsa min nace..!!”
Cikin zuban hawaye Giwa Ke jinjina kai tana furta “Gaskiya ne Jamal bansan waye mahaifinka ba...!”
Dakatar da ita yayi ta hanyar d’aga mata hannu yana mai sakin huci yake furta “No..! My father is dead..! My father was King AbdulJabbar... Shine mahaifina... Bazan tab’a zama product na cin amanar da kika masa ba..! You’re a worthless mother..! Mujiyar uwace Ke mai kashe ‘ya’yanta..! Ko baki d’auki wuk’a kin dab’a mana ba kin kashe mu da abinda kika mana... Gaba d’aya rayuwana nayisa ne wajen miki biyayya..! Ashe duka rayuwan nawa k’Arya ne... Babu komai cikinta face k’arya...! Duk fad’i tashin da Kike wajen ganin kin kafa mulkin babu komai a cikin labarin face k’arya..! Kina neman ki d’aura ‘ya’yanki saman Karagar da basuda gado..! Maami kin cuceni kin zalunceni..! Nayi nadaman miki biyayya da nayi a baya dukda ire iren muggan abubuwan da kika sa na dingayi.. Allah ya isa tsakanina dake Giwa.. Kuma yanzu basai anjima ba zanje na kwance yarinyar nan bazan sake miki biyayya ba daidai da dak’ik’a guda..!”