← Book details Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 162

Sashe 87

Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Turaki ya nusa kad’an kana ya furta “Fine naji baka nemi shawarina ba... But ya zama dole na fad’a maka ko bazaka saurareni ba Your Royal Highness...!! Haka zaka tafi kana mai sab’a alk’awari..Haka zaka tafi ka bar mutuwar mahaifinka da matarka unpunished..? Haka zaka tafi ka k’yale mahaifiyarka da jin kunya bayan Ta aminta da kai..? Haka zaka tafi ka bar Al’ummanka masu k’aunarka broken..?!” Ya d’an sassauta muryarsa yana mai ci gaba da fad’in “Haka zaka tafi ka k’yaleta da k’aninka mai kwad’ayin jikinta cikin Masarautar bayan ka mata alk’awarin kareta..?! Haka zaka tafi ka hana zuciyarka kasancewa da zab’inta... You can’t leave all these behind your Highness...!!Ya k’arashe yana mai duban abokin nasa cikin wane irin yanayi....

A hankali ya karkato yana duban Turaki zuciyarsa na kuma bugawa, lokaci guda yake furta “What exactly do you mean..? Wacece kake nufi..?!”

Turaki bai basa amsa ba saima maida dubansaga b’angaren dasu Muhibbah Ke zaune da yayi... Lokaci guda yake ci gaba da furta “You can’t deny it your Highness, You love her... So much...!!” Ya k’arashe yana duban Mahmood d’in cikin idanu...

Bai iya furta komai ba sai duban Turaki da yake babu k’yafta idanu, fuskar nan tasa kaman bai tab’a dariya ba...

Turaki na ci gaba da sakin huci yake furta “Your Highness abinda kake k’ok’arin yi cin amanan Masarauta ne..! Cin amanan Al’ummanka ne...! Cin amana Ahalinka ne..!! Ba’asan Sarki da sab’a Alk’awari ba Rankaidad’e... Sunnan Sarakuna ne cika alk’awari da yin magana k’wara d’aya tak..! Kada ka zamto Sarki na farko da zai bar abin fad’i a tarihi..!!”

Da tsananin mamaki Mahmood ke dubansa, shine Turaki Ke fad’a masa magana haka....Lokaci guda yai gyaran murya Parlorn ya amsa... Take Hadiminsa ya k’araso yana mai zubewa had’ida kwasan gaisuwa...

Har lokacin idanunsa naga Turaki hannayensa hard’e ta baya, fuskar nan tasa tamau, saida ya kwashe dak’ik’ai kaman bazai magana ba Hadimin nasa na nan risine wajen sai kuma ya bud’e murya yace “Kai masa rakiya zuwa k’ofan Fada...! Kuma kar a sake barinsa ya shigo har sai na bada umarnin hakan..!!”

Turaki ya sadda idanunsa k’asa dan yasan hakan ka iya faruwa... Lokaci guda yake furta “I’m sorry Your Highness... But I know my way out..!!”
Yana ida fad’in haka ya risina yace “Na Barka Lafiya Rankaidad’e..!!” Lokaci guda yasa kai ya nufi k’ofa...

Barde ya mik’e yana an gama Rankaidad’e..! Allah shi ja zamaninka..!!” Lokaci guda yabi bayan Turaki yana furta “Fada bata Marhaban da kai...!!”

Mahmood dake nan tsaye wajen fuzar da huci mai tsananin d’umi yayi zuciyarsa na masa k’una... Yana mai tuhumar kansa da abubuwan da Turaki ya zayyano masa, ciki babu wanda ya tsaya masa a rai kaman cewa da yai son yarinyar nan yake...
Hannayensa biyu yasa ya shafi fuskarsa yana mai kuma fuzar da fuci yake taka cikin tampatsetsen parlorn nasa cikin taku d’ai d’ai irinta masu mulki...

SameenaAleeyou📚*MUHIBBAH*

*55*

*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*

Yau kusan sati kenan babu su Ubandoma babu labarinsu, fad’in tashin hankalin da Giwa Ta tsinci kanta ciki b’ata baki ne... Ga duk wanda yai mata Farin sani kallo guda zai mata ya fahimci bata a hayyacinta, tabbas duniya tai mata atishawan tsaki, abubuwa sunci gaba da tafiya ba yanda taso ba... A halin yanzu nad’in sarautar Mahmood da auren Jamal da Umaima ne kawai take tinanin Sune sa’arta na k’arshe, amma kam b’acewar Izzatu da Jafar harmada Ubandoma ba k’aramin d’aga hankalinta hakan yayi ba... Daga ita har Waziri an rasa mai dannan wani... Shima a nasa tinanin lokaci ya kusa da zai juya mata baya dan a nasa tsarin da zaran sun kauda Mahmood Karagar tasa ce ko kusa bazai bari Yazeed ya d’ale Karagar ba... Wannan k’udiri nasa ya jima cikin zuciyarsa tun ba yanzu ba...

**

A b’angaren Yarima Mahmood kaw tinanin abubuwan da Turaki ya fad’i masa sun kasa b’acewa daga kwanyarsa... Kullum cikin tunani yake, kalaman Turaki na k’arshe su suka tsaya masa a zuciya _”Abinda kake k’ok’arin yi cin amanan masarauta ce, cin amanan Ahalinka ne.. Cin amana Al’ummanka ne..! Cin amana Zuciyarka ne..”_

Ya kuma lumshe idanunsa a hankali yana mai aje pencil d’in da yake sketching dashi... Ya mik’e yana zaga farfajiyan benen nasa lokaci guda yana tunanin abinyi... Wata zuciya tace ka sami d’iyarka da batun kar rana tsaka taga zaku koma Spain Ta kuma zarginka da wani abin...! Ya kuma sauk’e ajiyan zuciya a hankali kana yayi kiran Hadiminsa yace a kirawo masa d’iyarsa Zahra...

Babu jimawa Zahra ta shigo kanta a k’asa ta duk’a ta gaida mahaifin nata... Ya amsa mata da sakin fuska kana ya nuna mata gefensa yace tazo Ta zauna...
Ta d’an d’ago idanu ta dubesa daga nan k’asa yanda take zaune kana tace “Paa kaifa Maimartaba ne yanzu...!”

Ya murmusa kad’an yace “Kema Maimartaba ce, Zo ki zauna...!”

Ta mik’e cikeda jin nauyi ta isa ta zauna a d’arare ba kaman yanda ta saba a baya ba domin kaw tabbas mulki ba k’arya bane akwaita da gizo... Mahmood ya karkato kad’an yana dubanta kana yai gyaran murya ya soma fad’in “Zahra Ina son Ki sani duk abinda nakeyi sabida Ke nakeyi, bazanyi abinda zan cutar dake ba... Kuma bazan yanke shawarinda bazai miki amfani ba..!”

Yanda yake maganan gaba d’aya sai yasa jikinta yin sanyi, Ta d’an d’ago idanunta masu rauni tace “Paa you’re starting to scare me now, just tell me ko menene nasan bazaka cutar dani ba.. Aunty Muhibbah tace a koda yaushe na kasance mai kyautata zato wa mutane and especially to you Paa, coz you’re my Father and you love me unconditionally...But with the way you’re talking Paa, sai ina jin tsoron abinda zai fito daga bakinka.. You become totally irrational tinda muka dawo k’asar nan... Paa what exactly are you afraid of telling me..?!” Ta k’arashe cikin raunin murya..

Sirhitaccen murmushi saman fuskarsa yake dubanta, cikin zuciyarsa yana kuma nanata sunan Muhibbah... Lokaci guda ya jinjina kai yace “Your Tia was right... Ina k’aunarki sosai kuma bazanyi abinda zai cutar dake ba..! Zahra, Decidí que volveremos a España tan pronto como me case con Raheema..” (Zahra na yanke shawarin zamu koma Spain da zaran na auri Raheema)
“We’d have a new life there the three of us..!”

Da tsananin mamaki Zahra ke dubansa... Ta d’an girgiza kai tace “Is that really necessary Paa..?, Wai zamu sake komawa Spain, kuma da matar nan...But Paa...”

Katseta yai da fad’in “It’s for the best Zahra.. I promise..!”

Kaman zatai magana sai kuma tai shiru cikin tsananin sanyin jiki take furta “Alright..!Shikenan ..! Si tú lo dices Paa” (Idan kace haka Paa)

Lokaci guda ta mik’e ta d’an sadda kanta tace “Na Barka lafiya Papa..!”

Ya jinjina mata kai a hankali yana mai binta da kallo har ta b’acema ganinsa...

A hanya Muhibbah Ta hangeta tana tafe tana matsan hawaye, babu shiri tabi bayanta tana tinanin mai ya faru da ita kuma...

Can k’asar wata bishiya Zahra Ta k’arasa Ta zauna tana ci gaba da kuka a hankali... Muhibbah ta k’araso ta d’an dafata kad’an “Are you alright..?!” Ta tambaya tana duban Zahran...
Mik’awa Zahra tai Ta rungumeta sosai tana mai ci gaba da kuka...
Muhibbah dake tsaye tamkar statue tana sauraron kukan da yarinyar keyi har cikin zuciyarta, a hankali Ta soma lallashinta tana tambayarta meke faruwa..?

Zahra tasa hannu ta goge hawayen da suka jik’a mata fuska “My Paa have decided we’re leaving back to Spain bayan ya auri wannan witch d’in...!!” Ta k’arashe tana sakin huci wasu hawayen na kuma gangaro mata...

Kaman sauk’an aradu haka Muhibbah taji batun “Zaku koma Spain... Wait he can’t do that... I mean your life is right here...!”

Zahra Ta jinjina kai tace “I don’t want to leave with that woman.. I don’t want her in our lives... Dik iyaka k’ok’arina naga na sota ko kad’an ne wllhi banjin sonta, kullum k’ara tsanarta nake... And and what’s worse is that.. I don’t want us to be separated.. Idan muka koma Spain shikenan bazan sake ganinki ba Tia..!” Ta k’arashe cikin tsananin rawar murya irinta mai kuka...

Janyota Muhibbah tai ta rungumeta kad’an tana lallashinta “Everything will be alright in sha Allah... kinji Ki kwantar da hankalinki....!”

Zahra tai shiru cikin k’irjinta tana ci gaba da ajiyan zuciya Muhibban na shafa kanta a hankali, su duka biyun zukatansu na bugawa...

So wannan shine dalilin da yasa Rankaidad’e ya dage da batun auren matar nan lokaci guda... Turai zasu tafi tare, ashe kenan bazai tsaya a nad’asa Sarauta ba... Hakan na nufin idan ya tafi wani zai maye gurbin Sa ya zamto Sarki... Toh waye zai maye gurbin nasa..? “YAZEED” sunan da zuciyarta ya raya mata kenan... Take Ta shiga girgiza kai tana ayyanawa cikin zuciyarta bazata tab’a bari hakan ya kasance ba... Yazeed bazai zama Sarki ba koda na rana guda ne... She needs to come up with something as soon as possible...! Ta k’arshe tana tunanin Menene abinyi...

**
A can Masarautar su Raheema kuwa Amarya gyara ake da shirin biki babuji babu gani dikda cewa Yazeed ya tak’ura mata da waya akan sai ta dawo masarauta sunyi final goodbye da juna... Yau d’inma wayace mak’ale kunnenta anai mata gyaran jiki tai excusing kanta tana mai ci gaba da amsa kiran nasa “Wai mai kake nema a wajena ne prince... Na zaci munyi sallama ai..!”

Yazeed ya murmusa kad’an yana shafan hab’arsa yace “Rankidad’e Amarya hak’uri zakiyi ki dawo masarauta muyi proper goodbye, I’m not even sure idan zan iya barinki wa Mahmood gaba d’aya..!”

Fuzar da huci tai tana mai rausayar da idanu tace “Kaga Yazeed I’m not in the mood to play such game with you, it’s over between us.. Dan Allah ka k’yaleni najida..!”

Katseta yayi da fad’in “And who’s playing games with you...!! It’s not over, until I say so..! Ki dawo Masarauta muyi sallaman k’arshe idan har kinaso Mahmood ya zama naki..!”

Ta fuzar da fuci kad’an tana mai dafe kanta tace “But mai zance... Ta yaya za’ayi na d’auki k’afafu na tafi Masarautar su mijina tun ba’a d’aura aure an kawoni ba... Kasan yanda abubuwan sarauta suke yanzu yin hakan sai ya zama wani babban scandal..!”
Chapter 87 · 0% Book details