Sashe 127
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mamaki ya cika fuskokin mutane da jin irin kalaman dake fitowa daga bakin Yazeed...! Lokaci guda Yazeed d’in ya juyo yana duban mutane kana yaci gaba da fad’in “Jama’an Masarautar nan a yau d’in nan inaso na sanar daku ko wanene Yarima Mahmood da wasunku suke masa lak’abi da Sarki mai jiran Gado...! Ina son kowa ya shaida cewa Shid’in ba kowa bane face k’ask’antaccen Bawa..! Mahaifiyarsa Baiwa ce ga matar Sarki Gimbiya Turai..! Mahaifiyarsa Hadima ce da Gimbiyar Turai tayi tukuici da ita ga mahaifina Sarki AbdulJabbar mai rasuwa..! A tarihin Masarautar nan d’an Baiwa bai tab’a mulki ba sai d’an Sarauniya..! Wannan dalilin ya tabbatar cewa Mahmood bazai tab’a gadon Karagar mulkin gidan nan ba..!!” Ya k’arashe yana mai sakin huci yana kuma duban Yarima Mahmood wanda jikinsa Ke sakewa a hankali, hannunsa dake faman dunk’ulesu yana waresu a hankali alamun ya shiga tsananin Shock da abinda yakeji na fitowa daga bakin Yazeed d’in...
Ganin haka yasa Yazeed d’in ci gaba da fad’in “K’warai..! Ina so kowa ya shaida cewa ba mahaifiyata Gimbiya Turai bace ta haifi Mahmood Hadimarta ce k’ask’antacciya da taci amanan Uwargijiyarta ta haifo Mahmood.. Wannan magana da nake sanar daku Gimbiya Turai kuma Giwar Amale da bakinta Ta sanar dani sabida zuwan irin wannan rana..! Mahaifiyata bata haifi d’an Sarki Mahmood ba... Inada k’wak’warran shaidu da zasu tabbatar da hakan..!”
Cikin tashin hankali Talba ya katsesa da fad’in “Kai Yarima, kana cikin hayyacinka kuwa kodai had’arin da kayi ya tab’a maka kaine.. Ka kuwa San abinda kake fad’i..?!”
Yazeed ya karkato yana duban Talba kana yace “K’warai kuwa Talba..! Da hankalina tsaf nasan abinda nake fad’i..! Kuma idan kuna ganin k’Arya nake zan gabatar maku da shaidun da zasu tabbatar cewa Mahaifiyata Giwa ba itace Ta haifi Yarima Mahmood ba, shid’in d’an Baiwarta ce kuma k’ask’antacciya ..!!”
Cikin sakin huci da jin zafin abinda Yarima Yazeed keyiwa d’an uwansa a bainar jama’a Talba ya bud’e murya yace “Su waye shaidun da kake magana akai Yarima Yazeed..! Su waye zasu tabbatar da k’arerayin da kake fad’i..?!”
Kafin Yazeed yakai ga bada amsa suka sinkayo wata murya mai amon gaske tana fad’in “Ni ne nan zan bada shaida..!!”
Gaba d’aya suka juya suna duban wanda yayi magana cikin tsananin Shock.. Harda Yazeed d’in wanda yake yunk’urin nuna Waziri a matsayin shaida..!
Ga tsananin mamakinsu suka zuba wa mutumin da yayi magana, sanye yake cikin shiga irinta Mulki, yayi tsayuwa irin yanda masu Mulki keyi..!
A hankali Mahmood ya furta “JAFAR..!!”Koda ace ya sanya tufafi irin na masu mulki tabbas kamanninsa bai b’ace ba..!
Mamaki da aljabi ya cika illahirin jama’an dake wajen sanda Ja’afar ya soma takowa cikin haraban Masarautar..! Mutane sai darewa suke suna basa hanya, wasu na k’ok’arin guduwa ganin Tamkar Fatalwa ne a gabansu.. Babu kaman Waziri wanda tuni fitsari ya cika mararsa..
Kai tsaye gaban Mahmood Ja’afar ya isa ya tsaya su duka biyun suna duban juna cikin idanu... Wani irin duba Jafar keyiwa Mahmood d’in kalman Yazeed na Yawo a kwanyarsa cewa Giwa ba itace Ta haifi Mahmood ba, mahaifiyarsa Hadimarta ce..! Wato mahaifiyarsu d’aya kenan, ya shiga tuno abubuwan da mahaifiyarsa Ta sanar dashi wanda Giwa tai mata..! Kenan Yarima Mahmood shine Babban d’a ga Mai Martaba wanda Bokan Giwa yace sai an haifosa duniya..! Kenan sace Yarima Mahmood tayi Ta rabasa da mahaifiyarsa kaman yanda Ta sacesa shima..! Lokaci guda yaji hawaye na neman ciko idanunsa.. Gashi ga d’anuwansa wanda suka fito ciki guda...!
Shima Mahmood d’in wane irin duba yake ma Ja’afar d’in, sai yana ganin kaman ya tab’a ganin Ja’afar d’in da irin shigar da ya gansa ciki yau... Cikin wane irin murya mai raunin gaske ya furta “Ja’afar..!!”
Hawayen dake mak’ale cikin idanun Ja’afar suka gangaro..! Lokaci guda ya rungume Mahmood d’in hawaye naci gaba da gangaro masa..!
Mamaki ya kasa sakin d’aukacin jama’an dake wajen... Tirk’ashi..!Wannan shine ana wata ga wata..!
Waziri da ya tabbata Ja’afar yake gani raye a gabansa cikin dabara ya soma k’ok’arin silalewa yana neman hanyar da zai fice daga wajen..!
Gudu gudu ya soma jada baya yana k’ok’arin tattare babbar rigarsa, kaman daga sama yaji ya bangaji mutum har rawaninsa na zubewa k’asa. D’aga kansa da zai yaga ba kowa bane face Ubandoma..!!
SameenaAleeyou *MUHIBBAH*
*75*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Ubandoma ya sakarwa Waziri murmushi maiji da lafiya had’ida furta “Rankaidad’e..! Mai girma Wazirin Wazirai..!!”
Waziri bai iya amsawa ba saima muzurai da yake ci gaba da yi...! Lokaci guda yaci gaba da ‘yan waige waige kana ya had’e hannayensa biyu waje guda yana duban Ubandoma yake furta “Dan Allah.! Dan darajan manzo salallahu alaihi wasallama... Kayi min sutura kaman yanda Allah yayi maka, ka rufa min asiri...!!”
Ubandoma ya kuma murmusawa yana azawa Waziri rawaninsa akai yake furta “Haba Mai Girma Waziri..!!”
Waziri ya katsesa da fad’in “Banida wani girma wllhi..! K’ila ma ka fini girma a halin yanzu..!!”
Ubandoma ya girgiza kai yace “Yau nida nake duk’a maka kaine kake duk’a min Waziri..? Tabbas na yarda da hausan da ake cewa RUWA YA K’AREWA D’AN KADA..! Ruwa ya k’are maku Waziri bakuda wajen guduwa... Watan tonuwan asirinku da duk wani mummunan aiki da kuka jima kunayi cikin Masarautar nan ne ya tsaya...! Shige muje ai bazaka bar cikin Masarautar nan ba sai ka bada shaidar cewa ba Giwa bace Ta haifi Yarima Mahmooda kaman yanda Yarima Yazeed yace..!!” Ya k’arashe yana mai dank’wafo Waziri dake kuma duk’awa yana d’ago hannu yana rok’on Ubandoma ya rufa masa asiri..!
Ubandoma ya shiga janyo Waziri yana furta “Da ka tuna haka tinda wuri ka rufa ma kanka asiri kayi abinda ya dace da bai kawomu ga wannan munzani ba..! Ka sani Waziri kaida kanka ka toni asirin kanka babu wanda ya tona maka asiri..! Shige muje..!!” Ya k’arashe yana mai kuma hankad’o Waziri...
Rik’e gaskiya domin itace take fitar da tsirrai har tayi ‘ya’ya... K’arya fure take bazata Tab’a yin ‘ya’ya har a amfana da ita ba...! Ba’a tab’a cewa gaskiyarka Ta k’are saidai ace k’aryarka Ta k’are... Babu k’ask’antacce sai wanda ya k’ask’antar da kansa... Yau ga Waziri yana duk’awa gaban Bawan da a baya shi yake duk’a masa dan asirinsa ya rufu... Allah ka rabamu da jin kunya duniya da lahira Ameen..!
Cikeda isa da gadara Yazeed ya dakatar da Ja’afar da fad’in “The drama is over kai k’ask’antacce Bawa..! Idan ma banda lalacewa Ta yaya za’a ce Basarake yana rungumar Bawa..! Wannan ya tabbatar da abinda nake fad’i cewa Mahaifiyata ba ita ta haifi Mahmooda ba, shid’in jinin Bauta ne gashi nan kuna gani Bawa d’an uwansa na rungumarsa... Watak’ila sud’in sun had’a jini.. Wannan shine kuke so ya zamto Sarkinku..! Ace Sarki yana rungume rungumen bayi..?! Wace masarauta ce kuka tab’a ganin anyi haka..! Lallai lalacewa yakai lalacewa..! Har abada jinin Bauta bazai tab’a mulkanmu ba..!” Ya k’arashe yana fidda huci...
Daidai nan Ja’afar da idanunsa suka gama kad’awa ya juyo ya Yazeed yana takowa gaba garesa cikeda izza da isa shima wanda sam baisan yanada irinta ba, nan yake furta “Tabbas kayi gaskiya mud’in ‘yan uwan juna ne wanda suka fito ciki guda..! Tabbas kayi gaskiya shid’in bai fito daga tsatson mahaifiyarka ba ..! Tabbas kayi gaskiya jinin Bauta bazai tab’a mulkin Masarautar nan ba..! Wanda hakan ya tabbar da kaid’in har abada bazaka tab’a d’ale Karagar mulkin gidan nan ba a matsayinka na D’AN BAIWA..!!” Ya k’arashe yana mai matso da fuskarsa dab na Yazeed zuciyarsa naci gaba da wane irin tafarfasa...!!
Yazeed d’inma da wasu irin idanu yake duban Ja’afar d’in yana jin inama yanada hannuwa ya shak’o wuyan wannan bawa ya saka sa a yanda ya kamacesa..!!
Cikin tsananin huci Yazeed Ke furta “Kai k’ask’antacce Bawa..! Wa ya baka daman ka gaya min maganganu haka..! Kai har ka isa ka kira Mahaifiyata da Baiwa.. K’ask’antacce kaman Kai..!!!”
Muryar Ubandoma Yazeed ya sinkaya yana fad’in “Waziri shi zai tabbatar da abinda Yarima Ja’afar yake fad’i..!!”
Gaba d’aya mutanen dake wajen suka shiga juya sunan da Ubandoma ya kirawo Jafar dashi.. Yarima Ja’afar..! Yarima Ja’afar dai..! Shin yaushe Ja’afar ya zamto Yarima..? A Iya sanin kowa JA’AFARU D’an Bawa ne wanda bai gaji komai ba sai Bauta toh a ina ya samo title d’in ‘ya’yan Saraki..!!
Da tsananin mamaki Yazeed yai k’ok’arin kaikaitowa yana duban Ubandoma dake tafe tareda Waziri wanda ko d’aga Kai baiyi..!
Shikam Mahmood badon Allah ya taimaka yanada k’arfin zuciya ba tabbas da tuni ya silale k’asa sumamme da irin abubuwan da yake gani suna faruwa gaba gareshi wanda yafi kamanceceniya da ire iren mafarkan da yake..!
Yazeed ya dubi Ubandoma ya dubi Waziri..! Ubandoma ya kuma duba yace “Kai k’ask’antacce Bawa..! Ka kuwa San abinda kake fad’i..?!!”
Ubandoma ya risina gaban Yazeed yace “K’warai Rankaidad’e abinda nake fad’i gaskiya ne..! Mai girma Waziri shi ne zai bada shaida..!!!”
Wane irin k’asaitaccen murmushi Yazeed yayi ya dubi Waziri yace “Waziri inaso ka k’aryata wad’annan mak’aryatan a bainal jama’a..! Ina so ka bud’e baki ka bada shaidar cewa Mahmood d’an Baiwa ce bai gaji sarauta ba..! Domin kuwa D’an Bawa baya sarauta..!! Ina so ka bud’e bakinka Waziri ka sanar da d’aukacin ahalin Masarauta yanda Hadimar Mahaifiyata Ta yaudari Mai Martaba ya fad’a tarkonta har Ta haifo masa d’ansa Mahmood..!!”
Shidai Waziri banda rawa babu abinda jikinsa keyi, ga wane irin gumi dake tsartsafo masa babu k’akk’autawa..! Gaba d’aya saima silalewa saman gwiwoyinsa da yayi...!
Al’ajabi ya kuma cika mutane, Yazeed ya tsaresa da idanu yana mamakin yanda ya zube k’asa yana mai farawa da neman gafara..!
Lokaci guda Waziri yaci gaba da furta “Nidai amin aikin gafara..! Wllhi sharrin shaid’an ne da kuma sharrin zuciya had’ida rud’in duniya..!!”
A wane irin zuciye Yazeed ya katsesa da fad’in “Kai Old man ba wannan aka tambayeka ba..! Babu wanda yace kayi ma kanka tonan asiri..! Ba asirinka nace ka tona ba..! Asirin Mahmood nace ka tona..! Ka tona asirin Mahmood kowa yasan shid’in d’an Baiwa ce k’ask’antacciya..!!!” Ya k’arashe yana mai shure Waziri da k’afafunsa..!
Ganin haka yasa Yazeed d’in ci gaba da fad’in “K’warai..! Ina so kowa ya shaida cewa ba mahaifiyata Gimbiya Turai bace ta haifi Mahmood Hadimarta ce k’ask’antacciya da taci amanan Uwargijiyarta ta haifo Mahmood.. Wannan magana da nake sanar daku Gimbiya Turai kuma Giwar Amale da bakinta Ta sanar dani sabida zuwan irin wannan rana..! Mahaifiyata bata haifi d’an Sarki Mahmood ba... Inada k’wak’warran shaidu da zasu tabbatar da hakan..!”
Cikin tashin hankali Talba ya katsesa da fad’in “Kai Yarima, kana cikin hayyacinka kuwa kodai had’arin da kayi ya tab’a maka kaine.. Ka kuwa San abinda kake fad’i..?!”
Yazeed ya karkato yana duban Talba kana yace “K’warai kuwa Talba..! Da hankalina tsaf nasan abinda nake fad’i..! Kuma idan kuna ganin k’Arya nake zan gabatar maku da shaidun da zasu tabbatar cewa Mahaifiyata Giwa ba itace Ta haifi Yarima Mahmood ba, shid’in d’an Baiwarta ce kuma k’ask’antacciya ..!!”
Cikin sakin huci da jin zafin abinda Yarima Yazeed keyiwa d’an uwansa a bainar jama’a Talba ya bud’e murya yace “Su waye shaidun da kake magana akai Yarima Yazeed..! Su waye zasu tabbatar da k’arerayin da kake fad’i..?!”
Kafin Yazeed yakai ga bada amsa suka sinkayo wata murya mai amon gaske tana fad’in “Ni ne nan zan bada shaida..!!”
Gaba d’aya suka juya suna duban wanda yayi magana cikin tsananin Shock.. Harda Yazeed d’in wanda yake yunk’urin nuna Waziri a matsayin shaida..!
Ga tsananin mamakinsu suka zuba wa mutumin da yayi magana, sanye yake cikin shiga irinta Mulki, yayi tsayuwa irin yanda masu Mulki keyi..!
A hankali Mahmood ya furta “JAFAR..!!”Koda ace ya sanya tufafi irin na masu mulki tabbas kamanninsa bai b’ace ba..!
Mamaki da aljabi ya cika illahirin jama’an dake wajen sanda Ja’afar ya soma takowa cikin haraban Masarautar..! Mutane sai darewa suke suna basa hanya, wasu na k’ok’arin guduwa ganin Tamkar Fatalwa ne a gabansu.. Babu kaman Waziri wanda tuni fitsari ya cika mararsa..
Kai tsaye gaban Mahmood Ja’afar ya isa ya tsaya su duka biyun suna duban juna cikin idanu... Wani irin duba Jafar keyiwa Mahmood d’in kalman Yazeed na Yawo a kwanyarsa cewa Giwa ba itace Ta haifi Mahmood ba, mahaifiyarsa Hadimarta ce..! Wato mahaifiyarsu d’aya kenan, ya shiga tuno abubuwan da mahaifiyarsa Ta sanar dashi wanda Giwa tai mata..! Kenan Yarima Mahmood shine Babban d’a ga Mai Martaba wanda Bokan Giwa yace sai an haifosa duniya..! Kenan sace Yarima Mahmood tayi Ta rabasa da mahaifiyarsa kaman yanda Ta sacesa shima..! Lokaci guda yaji hawaye na neman ciko idanunsa.. Gashi ga d’anuwansa wanda suka fito ciki guda...!
Shima Mahmood d’in wane irin duba yake ma Ja’afar d’in, sai yana ganin kaman ya tab’a ganin Ja’afar d’in da irin shigar da ya gansa ciki yau... Cikin wane irin murya mai raunin gaske ya furta “Ja’afar..!!”
Hawayen dake mak’ale cikin idanun Ja’afar suka gangaro..! Lokaci guda ya rungume Mahmood d’in hawaye naci gaba da gangaro masa..!
Mamaki ya kasa sakin d’aukacin jama’an dake wajen... Tirk’ashi..!Wannan shine ana wata ga wata..!
Waziri da ya tabbata Ja’afar yake gani raye a gabansa cikin dabara ya soma k’ok’arin silalewa yana neman hanyar da zai fice daga wajen..!
Gudu gudu ya soma jada baya yana k’ok’arin tattare babbar rigarsa, kaman daga sama yaji ya bangaji mutum har rawaninsa na zubewa k’asa. D’aga kansa da zai yaga ba kowa bane face Ubandoma..!!
SameenaAleeyou *MUHIBBAH*
*75*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Ubandoma ya sakarwa Waziri murmushi maiji da lafiya had’ida furta “Rankaidad’e..! Mai girma Wazirin Wazirai..!!”
Waziri bai iya amsawa ba saima muzurai da yake ci gaba da yi...! Lokaci guda yaci gaba da ‘yan waige waige kana ya had’e hannayensa biyu waje guda yana duban Ubandoma yake furta “Dan Allah.! Dan darajan manzo salallahu alaihi wasallama... Kayi min sutura kaman yanda Allah yayi maka, ka rufa min asiri...!!”
Ubandoma ya kuma murmusawa yana azawa Waziri rawaninsa akai yake furta “Haba Mai Girma Waziri..!!”
Waziri ya katsesa da fad’in “Banida wani girma wllhi..! K’ila ma ka fini girma a halin yanzu..!!”
Ubandoma ya girgiza kai yace “Yau nida nake duk’a maka kaine kake duk’a min Waziri..? Tabbas na yarda da hausan da ake cewa RUWA YA K’AREWA D’AN KADA..! Ruwa ya k’are maku Waziri bakuda wajen guduwa... Watan tonuwan asirinku da duk wani mummunan aiki da kuka jima kunayi cikin Masarautar nan ne ya tsaya...! Shige muje ai bazaka bar cikin Masarautar nan ba sai ka bada shaidar cewa ba Giwa bace Ta haifi Yarima Mahmooda kaman yanda Yarima Yazeed yace..!!” Ya k’arashe yana mai dank’wafo Waziri dake kuma duk’awa yana d’ago hannu yana rok’on Ubandoma ya rufa masa asiri..!
Ubandoma ya shiga janyo Waziri yana furta “Da ka tuna haka tinda wuri ka rufa ma kanka asiri kayi abinda ya dace da bai kawomu ga wannan munzani ba..! Ka sani Waziri kaida kanka ka toni asirin kanka babu wanda ya tona maka asiri..! Shige muje..!!” Ya k’arashe yana mai kuma hankad’o Waziri...
Rik’e gaskiya domin itace take fitar da tsirrai har tayi ‘ya’ya... K’arya fure take bazata Tab’a yin ‘ya’ya har a amfana da ita ba...! Ba’a tab’a cewa gaskiyarka Ta k’are saidai ace k’aryarka Ta k’are... Babu k’ask’antacce sai wanda ya k’ask’antar da kansa... Yau ga Waziri yana duk’awa gaban Bawan da a baya shi yake duk’a masa dan asirinsa ya rufu... Allah ka rabamu da jin kunya duniya da lahira Ameen..!
Cikeda isa da gadara Yazeed ya dakatar da Ja’afar da fad’in “The drama is over kai k’ask’antacce Bawa..! Idan ma banda lalacewa Ta yaya za’a ce Basarake yana rungumar Bawa..! Wannan ya tabbatar da abinda nake fad’i cewa Mahaifiyata ba ita ta haifi Mahmooda ba, shid’in jinin Bauta ne gashi nan kuna gani Bawa d’an uwansa na rungumarsa... Watak’ila sud’in sun had’a jini.. Wannan shine kuke so ya zamto Sarkinku..! Ace Sarki yana rungume rungumen bayi..?! Wace masarauta ce kuka tab’a ganin anyi haka..! Lallai lalacewa yakai lalacewa..! Har abada jinin Bauta bazai tab’a mulkanmu ba..!” Ya k’arashe yana fidda huci...
Daidai nan Ja’afar da idanunsa suka gama kad’awa ya juyo ya Yazeed yana takowa gaba garesa cikeda izza da isa shima wanda sam baisan yanada irinta ba, nan yake furta “Tabbas kayi gaskiya mud’in ‘yan uwan juna ne wanda suka fito ciki guda..! Tabbas kayi gaskiya shid’in bai fito daga tsatson mahaifiyarka ba ..! Tabbas kayi gaskiya jinin Bauta bazai tab’a mulkin Masarautar nan ba..! Wanda hakan ya tabbar da kaid’in har abada bazaka tab’a d’ale Karagar mulkin gidan nan ba a matsayinka na D’AN BAIWA..!!” Ya k’arashe yana mai matso da fuskarsa dab na Yazeed zuciyarsa naci gaba da wane irin tafarfasa...!!
Yazeed d’inma da wasu irin idanu yake duban Ja’afar d’in yana jin inama yanada hannuwa ya shak’o wuyan wannan bawa ya saka sa a yanda ya kamacesa..!!
Cikin tsananin huci Yazeed Ke furta “Kai k’ask’antacce Bawa..! Wa ya baka daman ka gaya min maganganu haka..! Kai har ka isa ka kira Mahaifiyata da Baiwa.. K’ask’antacce kaman Kai..!!!”
Muryar Ubandoma Yazeed ya sinkaya yana fad’in “Waziri shi zai tabbatar da abinda Yarima Ja’afar yake fad’i..!!”
Gaba d’aya mutanen dake wajen suka shiga juya sunan da Ubandoma ya kirawo Jafar dashi.. Yarima Ja’afar..! Yarima Ja’afar dai..! Shin yaushe Ja’afar ya zamto Yarima..? A Iya sanin kowa JA’AFARU D’an Bawa ne wanda bai gaji komai ba sai Bauta toh a ina ya samo title d’in ‘ya’yan Saraki..!!
Da tsananin mamaki Yazeed yai k’ok’arin kaikaitowa yana duban Ubandoma dake tafe tareda Waziri wanda ko d’aga Kai baiyi..!
Shikam Mahmood badon Allah ya taimaka yanada k’arfin zuciya ba tabbas da tuni ya silale k’asa sumamme da irin abubuwan da yake gani suna faruwa gaba gareshi wanda yafi kamanceceniya da ire iren mafarkan da yake..!
Yazeed ya dubi Ubandoma ya dubi Waziri..! Ubandoma ya kuma duba yace “Kai k’ask’antacce Bawa..! Ka kuwa San abinda kake fad’i..?!!”
Ubandoma ya risina gaban Yazeed yace “K’warai Rankaidad’e abinda nake fad’i gaskiya ne..! Mai girma Waziri shi ne zai bada shaida..!!!”
Wane irin k’asaitaccen murmushi Yazeed yayi ya dubi Waziri yace “Waziri inaso ka k’aryata wad’annan mak’aryatan a bainal jama’a..! Ina so ka bud’e baki ka bada shaidar cewa Mahmood d’an Baiwa ce bai gaji sarauta ba..! Domin kuwa D’an Bawa baya sarauta..!! Ina so ka bud’e bakinka Waziri ka sanar da d’aukacin ahalin Masarauta yanda Hadimar Mahaifiyata Ta yaudari Mai Martaba ya fad’a tarkonta har Ta haifo masa d’ansa Mahmood..!!”
Shidai Waziri banda rawa babu abinda jikinsa keyi, ga wane irin gumi dake tsartsafo masa babu k’akk’autawa..! Gaba d’aya saima silalewa saman gwiwoyinsa da yayi...!
Al’ajabi ya kuma cika mutane, Yazeed ya tsaresa da idanu yana mamakin yanda ya zube k’asa yana mai farawa da neman gafara..!
Lokaci guda Waziri yaci gaba da furta “Nidai amin aikin gafara..! Wllhi sharrin shaid’an ne da kuma sharrin zuciya had’ida rud’in duniya..!!”
A wane irin zuciye Yazeed ya katsesa da fad’in “Kai Old man ba wannan aka tambayeka ba..! Babu wanda yace kayi ma kanka tonan asiri..! Ba asirinka nace ka tona ba..! Asirin Mahmood nace ka tona..! Ka tona asirin Mahmood kowa yasan shid’in d’an Baiwa ce k’ask’antacciya..!!!” Ya k’arashe yana mai shure Waziri da k’afafunsa..!