Sashe 118
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Cikin wane irin daka tsawa taceda Jakadiya “Maza ki koma ki tabbata Alfah ya mutu wannan karon daga shi har matar tasa ku k’onesu da wuta, kada ki bari ya kufce..!! Ita kuma wannan yarinyar zan mik’ata ga boka Tal’udu domin ya sanar dani duk yarinyar da ‘ya’yana suka lalata ma rayuwa itace gudan jinin da K’addarar Masarautar nan zai rayu a wuyatan, itace zai tsafi da ita domin ya tabbatar da dawamammiyar mulki na data ‘ya’yana cikin Masarautar nan...! Wannan yarinya SAUDATU itace makullin mulki na data ‘ya’yana...!!!” Ta k’arashe tana sakin wane irin shewa, ni kuma a lokacin naji jikina na wane irin karkarwa, naga wannan yarinyar d’iyar d’anuwana kaman yanda Izzatu tace tana buk’atar taimako daga gareni dan idan na barta Izzatu zata halak’ata, koda ba d’iyar d’anuwana bace rai ne mai buk’atan taimako daga hannun wannan azzalumar Baiwa da babu Allah cikin zuciyarta... Na isaga yarinya SAUDATU na tallafota na k’urama fuskarta idanu sai na hango kamannin d’anuwana a tattareda ita, naji wasu irin hawaye suna zuwa min, jikina ya d’auki rawa... Duk wannan abinda nake Izzatu bata lura dani ba sai sakin wane irin muguwar dariya take tana furta a yau burinta zai cika za’a kulle k’ofar sarautun Masarautar nan akanta da ahalinta da jinin wannan yarinyar... Cikin rawar jiki na soma k’ok’arin gudu rungume da yarinyar saidai ashe bokan Izzatu tuni ya hangoni sai ganinsa nayi gaba gareni cikin wane irin yanayi maras kyan gani.... Kafin nayi wani aune ya nunani da sandar tsafinsa sai gani nayi kaman an finciki yarinyar daga hannuna ta fad’a hannunsa, naji mummunar muryarsa yana furta “Wannan tamu ce, ita d’in an d’aura mata aure da Sarauniya, Amaryarmu ce wacce sarauniya zata zuk’i jininta..!” Take naji kaman an kifar dani k’asa tin daga lokacin ban kuma sake sanin komai gameda Alfah da ahalinsa ba domin kaw farkawa kawai nayi na ganni a d’akina wannan mutumin ya d’aureni da sark’ok’i... Hakan yasa nasan Fuskar d’iyar Alfah... Kuma ko bayan shekaru da na sake ganinta sai na fahimci itace, kenan Allah bai ida nufin Izzatu da Bokanta akan d’iyar Alfah ba, ya kub’utar da ita da buwayarsa daga hannun wad’annan azzaluman bayi nasa... Shiyasa na k’udiri niyyan mallaka mata wannan Taswira da Wambai ya bani shekara da shekaru Ina ajiye dashi, domin kuwa jikina ya bani itace zata zamto silan tonon asirin Izzatu...!!”Tana hawaye taci gaba da basu labari har kawo zuwa yanda Muhibbah ta taimakesu itada Ja’afar da taimakon da Ubandoma yayi masu bayan duk abubuwan da yayi mata a baya wanda Muhibbah itace Ta matso masa da tsoron mahaliccinsa kusa har ya karyar masa da zuciya yayi abinda ya dace..!!
Gaba d’aya baka jin sautin komai sai ajiyan zuciya da zuban hawaye... Sosai Ja’afar yake kuka ya matso kusan Gimbiya Turai ya duk’a yace “Rankidad’e kikace budurwar data taimaka mana sunanata Muhibbah Kuma Ta ambaci sunana tace ta sanni..?!”
Gimbiya Turai ta jinjina kai tace “K’warai ta ambato sunanka J’afar, kuma ta sanka, kuma wanann budurwar itace SAUDATU d’iyar d’anuwana Alfah wanda Izzatu ta halak’asa...!!”
Hawaye suka kasa daina zubowa daga idanun Ja’afar, lokaci guda yake furta “Saudah ta dawo, ta dawo cikin Masarautar nan...!!”
Gimbiya Turai ta jinjina masa kai tace “K’warai Jafar ta dawo kuma nasan duk yanda take cikin Masarautar nan tana buk’atar taimakonmu domin kuwa idan har Izzatu ta fahimci wacece ita toh rayuwarta ka iya kasancewa cikin had’ari mafi muni fiyema da wanda ta shiga a baya...! Amma ya akayi kasan SAUDATU..?!”
Ja’afar da idanunsa suka kad’a sukai jazir bayan hannunsa yasa ya share hawayen da suka zubo masa lokaci guda ya soma furta “SAUDATU wata yarinya ce da muke had’uwa da ita a k’aramar Kasuwar dake gabashin Masarautarmu, nakan shiga kasuwa duk ranan asabar domin nayi cinikin harawan dawakan Sarki na musamman, kaman yanda kuka sani ni d’in dah ne d’aya tol ga Sarkin Bargan Dawakan Sarki mai rasuwa mai suna Almu, mahaifiyata kuwa mai suna Kumbo tun lokacin data haifeni Allah yayi mata cikawa kaman yanda mahaifina ya bani labari, tun tasowata bansan komai ba face kulada dawakan Sarki kaman yanda mahaifina ya d’aurani akai, hakan yasa har bayan rasuwar mahaifina Mai Martaba bai yarda da kowa yaci gaba da kula masa da dawakansa ba sai ni dukda kuwa k’arancin shekaruna a wancan lokacin, tun ina k’arami na iya zuwa kasuwa nayi cinikayyan abincin Dawakan Sarki da kaina sabida nid’in nasan kan kalolin ciyayi abinci Dawakai wanda yafi kyau ma Dawakai... Wannan dalili na d’aya daga cikin abinda ya kuma jefa shak’uwa da Sabo tsakanina da Sarki AbdulJabbar... Toh Kasuwar da nake zuwa nakan had’u da yarinya Saudatu wasu lokutan da ‘yar jakanta Ta kayan data saye a kasuwa... Na lura yarinyar kaman tanada tsoron mutane dan ko kallo idan ka faye mata zakaga ta soma jada baya kaman zata gudu, da shike kasuwa ne k’arami hakan yasa yawancin mutanen da suke halartan kasuwan akai akai sukan iya sanin juna... Wata rana ta gama sayyayan kayan lambu dangin su tumatur ni kuma na d’auko harawata ta Dawakai na yunk’ura zan mik’e d’aukeda harawa a gadon bayana kwatsam mik’ewar da zanyi naji nayi fatali da abu ashe kayan miyanta na watsar mata... Ta durk’usa a wajen tana duban kayan miyan tana kuka...!
Akaita bata hak’uri tak’i tayi shiru, nima da naji haushi nayi zuciya nace kar Allah Sa kiyi hak’uri Ke wannan yarinyar dama haka kike ko yaushe kina yawan zuwa kasuwa amma kaman akwai abinda kike b’oyewa, wasu irin iyaye ne gareki ma da bazasu Zo kasuwa da kansu ba sai su turo k’aramar yarinya kaman ke...!! Haka nayita mata masifa a wajen har ta tsagaita da kukan da take ta tsaya tana dubana... Ashe itama taji haushi matuk’a ai kuwa tuni naga ta daka tsalle ta finciko harawana ya tsinke gaba d’aya k’ullun dakai masa ya watse a wajen... Sai faman sakin huci take tana hararata... K’arshe jama’an dake wajen suka shiga bamu hak’uri da ni ita, aka tattara mata kayan miyanta nima aka tattara min nawa harawan..! Sosai rashin tsoronta ya bani mamaki... Ni kuwa nace wannan yarinyar batada tsoro kuma ban santa a fad’in yankin ba, bansan su waye iyayenta ba, amma wannan rashin tsoro nata yayi min kamada d’iyar manyan mutane ko masu mulki, nace sai nabi yarinyar naga inane gidansu... Tana tafe ina biye da ita har ta fahimci Ina biye da ita... Taja ta tsaya ta rik’e kunkumi tanaci gaba da sakin huci, lokaci guda kuma naga Ta auna a guje tana k’ok’arin canza hanya.. Nayi saurin shan gabanta nace “Ki tafi a hankali kada ki kuma zubar da kayan miyanki, ni babu abinda zan miki...!”
Sai naga taja Ta tsaya amma dai tsoro bai rabu da ita ba... Na aje harawana gefe nace “Ke kuwa yarinya menene sunanki kuma daga ina kike dan ni ban tab’a ganinki a yankin nan ba sai tsakanin kwanakin nan..!”
Ta kauda kanta gefe kaman bazata min magana ba sai kuma tace “Abbah na ya hanani magana da kowa a garin nan..!”
Mamaki ya kamani nace “Ya hanaki magana da kowa kuma shine yake turoki Kasuwa kiyi sayayya..?!”
Ta jinjina kai tace “Eh ya hanani magana da kowa yace akwai dalilin da ya kawo mu garin nan da zaran mun sami dalilin zamu tafi mu bar garin nan, Abbah na baya fitowa daga gida sai dare sabida yace akwai wasu mugaye a garin nan da zasu iya cutar dashi shiyasa baya iya zuwa kasuwa saidai ya turani...!”
“Sosai mamaki ya kamani jin irin kalaman da take fad’i, na jinjina kai nace “Toh Ummanki fah.. Maiyasa bazata miki rakiya zuwa Kasuwar ba..?!”
Gaba d’aya baka jin sautin komai sai ajiyan zuciya da zuban hawaye... Sosai Ja’afar yake kuka ya matso kusan Gimbiya Turai ya duk’a yace “Rankidad’e kikace budurwar data taimaka mana sunanata Muhibbah Kuma Ta ambaci sunana tace ta sanni..?!”
Gimbiya Turai ta jinjina kai tace “K’warai ta ambato sunanka J’afar, kuma ta sanka, kuma wanann budurwar itace SAUDATU d’iyar d’anuwana Alfah wanda Izzatu ta halak’asa...!!”
Hawaye suka kasa daina zubowa daga idanun Ja’afar, lokaci guda yake furta “Saudah ta dawo, ta dawo cikin Masarautar nan...!!”
Gimbiya Turai ta jinjina masa kai tace “K’warai Jafar ta dawo kuma nasan duk yanda take cikin Masarautar nan tana buk’atar taimakonmu domin kuwa idan har Izzatu ta fahimci wacece ita toh rayuwarta ka iya kasancewa cikin had’ari mafi muni fiyema da wanda ta shiga a baya...! Amma ya akayi kasan SAUDATU..?!”
Ja’afar da idanunsa suka kad’a sukai jazir bayan hannunsa yasa ya share hawayen da suka zubo masa lokaci guda ya soma furta “SAUDATU wata yarinya ce da muke had’uwa da ita a k’aramar Kasuwar dake gabashin Masarautarmu, nakan shiga kasuwa duk ranan asabar domin nayi cinikin harawan dawakan Sarki na musamman, kaman yanda kuka sani ni d’in dah ne d’aya tol ga Sarkin Bargan Dawakan Sarki mai rasuwa mai suna Almu, mahaifiyata kuwa mai suna Kumbo tun lokacin data haifeni Allah yayi mata cikawa kaman yanda mahaifina ya bani labari, tun tasowata bansan komai ba face kulada dawakan Sarki kaman yanda mahaifina ya d’aurani akai, hakan yasa har bayan rasuwar mahaifina Mai Martaba bai yarda da kowa yaci gaba da kula masa da dawakansa ba sai ni dukda kuwa k’arancin shekaruna a wancan lokacin, tun ina k’arami na iya zuwa kasuwa nayi cinikayyan abincin Dawakan Sarki da kaina sabida nid’in nasan kan kalolin ciyayi abinci Dawakai wanda yafi kyau ma Dawakai... Wannan dalili na d’aya daga cikin abinda ya kuma jefa shak’uwa da Sabo tsakanina da Sarki AbdulJabbar... Toh Kasuwar da nake zuwa nakan had’u da yarinya Saudatu wasu lokutan da ‘yar jakanta Ta kayan data saye a kasuwa... Na lura yarinyar kaman tanada tsoron mutane dan ko kallo idan ka faye mata zakaga ta soma jada baya kaman zata gudu, da shike kasuwa ne k’arami hakan yasa yawancin mutanen da suke halartan kasuwan akai akai sukan iya sanin juna... Wata rana ta gama sayyayan kayan lambu dangin su tumatur ni kuma na d’auko harawata ta Dawakai na yunk’ura zan mik’e d’aukeda harawa a gadon bayana kwatsam mik’ewar da zanyi naji nayi fatali da abu ashe kayan miyanta na watsar mata... Ta durk’usa a wajen tana duban kayan miyan tana kuka...!
Akaita bata hak’uri tak’i tayi shiru, nima da naji haushi nayi zuciya nace kar Allah Sa kiyi hak’uri Ke wannan yarinyar dama haka kike ko yaushe kina yawan zuwa kasuwa amma kaman akwai abinda kike b’oyewa, wasu irin iyaye ne gareki ma da bazasu Zo kasuwa da kansu ba sai su turo k’aramar yarinya kaman ke...!! Haka nayita mata masifa a wajen har ta tsagaita da kukan da take ta tsaya tana dubana... Ashe itama taji haushi matuk’a ai kuwa tuni naga ta daka tsalle ta finciko harawana ya tsinke gaba d’aya k’ullun dakai masa ya watse a wajen... Sai faman sakin huci take tana hararata... K’arshe jama’an dake wajen suka shiga bamu hak’uri da ni ita, aka tattara mata kayan miyanta nima aka tattara min nawa harawan..! Sosai rashin tsoronta ya bani mamaki... Ni kuwa nace wannan yarinyar batada tsoro kuma ban santa a fad’in yankin ba, bansan su waye iyayenta ba, amma wannan rashin tsoro nata yayi min kamada d’iyar manyan mutane ko masu mulki, nace sai nabi yarinyar naga inane gidansu... Tana tafe ina biye da ita har ta fahimci Ina biye da ita... Taja ta tsaya ta rik’e kunkumi tanaci gaba da sakin huci, lokaci guda kuma naga Ta auna a guje tana k’ok’arin canza hanya.. Nayi saurin shan gabanta nace “Ki tafi a hankali kada ki kuma zubar da kayan miyanki, ni babu abinda zan miki...!”
Sai naga taja Ta tsaya amma dai tsoro bai rabu da ita ba... Na aje harawana gefe nace “Ke kuwa yarinya menene sunanki kuma daga ina kike dan ni ban tab’a ganinki a yankin nan ba sai tsakanin kwanakin nan..!”
Ta kauda kanta gefe kaman bazata min magana ba sai kuma tace “Abbah na ya hanani magana da kowa a garin nan..!”
Mamaki ya kamani nace “Ya hanaki magana da kowa kuma shine yake turoki Kasuwa kiyi sayayya..?!”
Ta jinjina kai tace “Eh ya hanani magana da kowa yace akwai dalilin da ya kawo mu garin nan da zaran mun sami dalilin zamu tafi mu bar garin nan, Abbah na baya fitowa daga gida sai dare sabida yace akwai wasu mugaye a garin nan da zasu iya cutar dashi shiyasa baya iya zuwa kasuwa saidai ya turani...!”
“Sosai mamaki ya kamani jin irin kalaman da take fad’i, na jinjina kai nace “Toh Ummanki fah.. Maiyasa bazata miki rakiya zuwa Kasuwar ba..?!”