← Book details Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 123 OF 162

Sashe 123

Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Daidai nan Jamal ya k’araso ya finciko wacce yake gani tsaye gaban Muhibbah ta basa baya...
Ga tsananin mamakinsa Zahra ya gani...!

SameenaAleeyou📚
*MUHIBBAH*

*73*

*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*

Cikin wane irin sauti Jamal ya furta “Zahra..! Mai ya kawoki nan...? Ya ma akai kika shigo nan..?!”

Zahra dake nan tsaye tana dubansa itama shaye da mamaki tace “Uncle I followed you here...! Wait what’s going on.. Why is she tied up..? Mai Ta maka Uncle..?!”

Huci kurum Kamal keyi yana duban Zahra wacce itama idanu waje take dubansa... Lokaci guda ya kuma finciko hannun Zahra yana fad’in “You’re too young to understand Zahra.. Just come with your Uncle..!” Ya k’arashe yana mai k’ok’arin janyota....

Fincike hannunta tayi da k’arfin gaske tana fad’in “No Uncle I’m not leaving this place sai ka sanar dani mai ta maka ka d’aureta a nan..! Uncle you’re not a bad person right..!” Ta k’arashe cikin yanayin tsoro idanunta suna firfitowa waje...

Jamal da ya gama k’osawa da yarinyar, k’ok’arin finciko hannunta yake yana fad’in “I said come with me Zahra, you talk too much...!!” Ya k’arashe yana mai damk’o hannunta da k’arfin gaske ya shiga janyota...
Tarjewa take tana furta “Let go Uncle,You’re hurting me.. Let me go..!!” Inaa bai saketa ba saima kuma janyota da yake dad’a yi...

Cikin yanayin gwari gwari dan yaren ba wai ya gama nuna a bakinta bane kalmomi take tunowa Ta samu Ta harhad’o su bada ma’ana, nan ta bud’e murya taceda Zahra “Morder su mano Zahra..!” (Ki ciza hannunsa Zahra).. “Y corre directo a tu Paa” (Ki gudu zuwa wajen Paa d’inki)

Jamal bai daina janye Zahra ba yake waigowa yana duban Muhibba yana fad’in “You witch, what are you telling her..?!”

A daidai wannan lokacin Zahra tayi amfani da damar tayi abinda Muhibbah ta fad’a mata, ta sunkuya ta had’e hak’waranta ta gantsarawa Jamal cizo.... Ya saki k’aran azaba lokaci guda ya saki sandarsa da hannun Zahra ya zube k’asa..

Zahra ta soma gudu tana fad’i da Muhibbah “No te preocupes, la tía mi papá vendrá a rescatarte, te lo prometo...!” (Kar ki damu Tia, Paa d’ina zaizo ya taimakeki... Nayi Alk’awari)...

Ita dai Muhibbah idanunta naga Jamal dake k’ok’arin jan jiki yana rarrafawa ga sandarsa... Cikin tashin hankali take ceda Zahra “Ejecuta Zahra..!” (Ki gudu Zahra) “Y dale esos papeles a tu Paa..!” (Ki baiwa Paa d’inki takardun nan)

Zahra da jikinta bai daina rawa ba lokaci guda take jinjina kai tana furta “Si segura le daré..!” (Eh K’warai zan bashi)...

Cikin hawaye Muhibbah Ke furta “Te amo zahra..!” (Ina k’aunarki Zahra)

Zahra da har ta kai k’ofa juyowa tayi cikin hawaye itama ta furta “Yo tambien te amo tia..!” (Nima ina k’aunarki Tia) Daga haka ficewa tayi a guje dai dai nan Jamal ya samu ya janyo sandarsa ya mik’e... Cikin wane irin bud’e murya yake dokawa Zahra kira...

Saidai tinda Zahra ta fice take gudu hanya na had’e mata sam bata gane ta yanda suka shigo wannan wajen ba balle ta fice... Taja ta tsaya zuciyarta naci gaba da yankewa... Juyawa baya tayi ta kalli gabas ta kalli yamma kudu da arewa... Ko ta ina bata fahimci hanya ba.... Ga wasu irin jerin k’ofofi duka iri guda... Tana a haka ta soma jiyo sauti kaman na sandar Jamal alamun yana nufota...
Zuciyarta ta kuma tsinkewa, nan Ta kuma daburcewa Ta rasa wane hanya zata bi...

**

Tinda suka fito daga Janaza basu wuce Fada direct ba yanda aka bisne ‘ya’yan Yazeed a nan cikin Masarauta mak’abartan da ake busne ahalin gidan... Su sai basu k’arasa masarauta ba suka nufi wajen mutumin da suka bigesa a daren jiya, suna addua’n Allah yasa su samu ya farka...

Turaki ne ya soma yin gaba Mahmood ya tsaya amsa kiran Likitan Yazeed dan tun daren jiya Yazeed d’in ya farka yake hauka, he couldn’t accept changes d’in da ya farka ya tarar tattaredashi...! Turaki kaw yana isa d’akin da aka kwantar da mutumin ya tadda sai sa’insa tsakanin likitan da mutunin ake... Mutumin yana fad’in “Look Dr, we have same profession.. You can’t detain me here, da hankalina nasan abinda nake...I’m leaving this place right this moment.. With or without your permission..!!” Ya k’arashe yana mai fincike drip d’in...

Dr ya girgiza kai yace “Toh idan Kai likita ne bana tsammanin kasan aikinka... Maybe you’re a quack..!”

A zuciye Ansar ya mik’e yana k’ok’arin shak’o wuyan likitan yake fad’in “What did you just call me..!”

Daidai nan Turaki yai saurin k’arasowa yana k’ok’arin raba tsakaninsu... Likitan na huci yake furta “Yauwa yayi kyau da ka k’araso... Please ka d’auke mana wannan lunatic a nan, what he needs is a psychiatrist.. Wannan mutumin tinda ya tashi hauka kawai yake... Jiya an kawosa nan ruwa ruwa babu abinci a cikinsa babu komai yau yasha drip har ya samu k’arfin da zai bud’e baki yace yasan abinda yake shi likita ne... Ance maka zama likitan cin tuwo ne..! Take him away please..!!” Ansar ya kuma harzuk’a yana sakin huci zai kuma cakumo mutumin... Turaki yai saurin rik’esa yana basa hak’uri.. Shidai likitan tattara folder d’insa yai ya fice ya barsu nan cikin d’akin...!

Turaki ya k’araso yana duban mutumin wanda goshinsa Ke mak’ale da bandage, ya mik’a masa hannu alamun musabaha yace “Yusuf Turaki..!”

Da idanu kurum Ansar ke dubansa, kaman bazai mik’a masa hannu ba sai kuma ya mik’a sukai masabaha...

Turaki yaci gaba da fad’in “Jiya mun bige ka a k’ofar masarauta sai mukai rushing d’inka to this hospital, bamu samu komai tareda kai ba, babu ID babu komai shisa bamuyi gaggawan kiran family d’inka ba... How are you feeling now...?!”

K’ok’arin sa kai Ansar yake yana furta “Get out of my way... I need to save her..!!” Ya k’arashe yana mai k’ok’arin ficewa...
Cikin sauri Turaki ya take masa baya dan ya soma yarda da batun Dr da yace wannan mutumin kwanyarsa ba’a saite yake ba, kuma sanda suka bigesa tafiya yake gaba gad’i saman kwalta ta yuwu da gaske ba mai lafiyar kwanya bane...

Haka suka nufo dogon corridor na asibitin Turaki na biye dashi yana furta “Abokina tsaya ka saurareni, d’an tsaya ka saurareni.. Sanar dani inane gidan naku sai na kaika... Ko ka kawo lambar wani naka daga gida a kira...! Kanada mata ne..?!”

A harzuk’e Ansar ya juyo yana furta “This is exactly why I’m here, to take my wife back...! Sun rabamu da k’arfi.. Muhibbah is mine..! Ita d’in tawa ce..! We were about to get married but they took her away from me...!!”
Hawaye suka ci gaba da gangaro masa sanda yake furta “Sun cutar da ita..! Sun lalata mata rayuwa, hakan duk bai ishesu ba...! And now sun kuma zagayowa sunyi auren nunafunci da ita kawai dan su gama da ita, su kasheta... Na tabbata wannan dalili yasa suka zagayo suka bada dukiya suka sayeta dan kawai su kasheta... Nayi imani sun fahimci cewa Muhibbah itace SAUDATU yarinyar da ‘ya’yan Sarki suka lalata ma rayuwa 14yrs back..!!” Muryar Ansar yaci gaba da rawa yana duban Turaki dake tsaye tamkar statue a gabansa yake ci gaba da furta “Wannan Masarautar babu komai cikinta face zalunci..! Yes zalunci..!! They all deserve to die..! Ka fahimceni..!! Ka fahimceni yanzu.!!!” Ya k’arashe yana mai jijjiga Turaki dake tsaye tamkar gunki gabansa, cikin wane irin kuka Ansar ke jijjiga Turaki Wanda da gani kasan fitar da k’uncinsa da damuwarsa yake..!

Ba Turaki da yayi mutuwar tsaye yana duban yanda Mutumin Ke kuka dirshan a k’Asa ba, harta Mahmood da tin isowarsa yake tsaye yana dubansu ji yayi jiri na neman kifar dashi k’asa..! Kalaman Fu’ad dana wannan mutumin suna buga k’wak’walwarsa dake barazanar tarwatsewa..! Da zaka d’aura hannunka kuwa a k’irjinsa zaka iya jin yanda zuciyarsa ke bugawa kaman zata b’alle ta fito daga cikin k’irjin nasa... A haka ya dinga jefa k’afafunsa har ya iso gaban Ansar, ya saka hannayensa biyu ya d’agosa, hawayen da baisan daga ina bane suna gangaro masa... Cikin wane irin rawar murya mai rarrabewa yake furta “What did you say..?! Tell me what you know about Muhibbah..! Tell me what you know about my wife..!!!” Ya k’arashe yana mai kuma dage k’arfinsa yana matse rigar Ansar wanda har ya soma b’arkewa sabida tsananin damk’a da Mahmood yai masa...

Tashin hankali sosai ya bayyana a fuskan Turaki... Ansar ya gane Mahmood, ya gane shine Babban d’an Sarki AbdulJabbar wanda daga farko Muhibbah tai masa mummunan zato... Ashe shine kenan ya zago ya aure Muhibbah..! Shine Bak’on Buzu da yayita b’adda kama a cikin Masarautar, lokaci guda cikin tsananin huci Ansar ke furta “Yes your Highness..! You heard me loud and clear.. Your three Bastard Brothers raped Muhibbah when she was a Kid...! Ta girma da k’udirin dawowa wannan Masarautar to take her revenge.. Ko ince tayi zaton mahaifinta was somehow hidden cikin Masarautar... She thought harda Kai a cikin ‘yanuwanka da sukaci zarafinta suka d’aid’aita mata ahali... Suka tarwatsa rayuwarta, shiyasa taci alwashin kai wannan Masarautar k’asa by all means... She promised to take each and everyone of you down koda hakan zai zamto abinda zatayi na k’arshe a rayuwarta..! Taso tayi amfani da d’iyarka to ruin you sai ta fahimci kaid’in baka daga cikin wad’anda sukaci zarafinta suka d’aid’aita mata rayuwa...! Bayan ta had’aka fad’a da d’iyarka Ta zab’i Ta kuma dawowa Masarautar domin ta gyara abinda ta b’ata sabida kaid’in baka d’aya daga cikinsu... Dukda sanin had’arin dake tattareda ita na dawowa cikin Masarautar but still Ta zab’i Ta dawo tayi abinda ya dace, Ta zab’i ta dawo only for you and your daughter... To fix your relationship with your daughter...! That’s how much she loves your daughter..! Amma yanzu daka satota ka kawota cikin Masarautar ranan da ya kamata ya kasance ranan aurenmu nayi imani mugayen ahalinka bazasu k’yaleta ba har sai sunga bayan rayuwarta..!!!”

Mahmood da jikinsa Ke tsananin rawa bai iya k’arasa sauraren Ansar ba yayi jifa dashi gefe guda ya fice a guje cikin wane irin tashin hankali...

Turaki da shima har lokacin bai koma daidai ba ya kasa aminta da abubuwan da yaji, jin abin yayi tamkar wani a film... A guje yabi bayan abokinsa yana furta “Your Highness..!!! Mahmood..!!!” Inaaa tuni Mahmood ya fice...
Ansar ma ya mik’e da k’yar ya biyo bayan Turaki...!
Chapter 123 · 0% Book details