Sashe 83
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Giwa ta katseta da fad’in “Ni Turai nafi k’arfin wani yayo min ture.... Nasha gaban kowa a tsafi, ni nakeda Tal’udu mai Fitilar tsafi...Ni nake turawa badai a turomun ba, kaman yanda na sace Sarautar Izzatu, da rayuwarta data cancanta na kuma guntule harshenta yanda bazatayi magana ba balle wani ya d’auki muryarta sannan na manna mata ciwon hauka daga k’arshe....Na kuma rabata da yaranta da duk wani dangi nata.... Kinga dai yanda nayi da Yarima Alfah da yaransa guda biyu da matansa guda biyu da ya taso har k’asar nan ya biyo sawun ‘yaruwarsa a lokacinda labari ya cimmasa cewa na maida Gimbiya Izzatu baiwa na maye Gurbinta da kaina...!”
Jakadiya Ta had’iyi miyau da k’yar tana jinjina ta’addanci irin na Giwa... A iyaka zatonta Izzatu Hadimarta ce aminattciya dataci amanarta ta aure Sarki AbdulJabbar bayan Giwa ta mallaka masa ita a matsayin tukuici ashe abin ba haka bane... Ashe Giwa Itace Hadimar Izzatu wacce Ta aminta da ita taci amanarta ta sace sunanta da rayuwarta harma da mijinta... Jiki na matuk’ar rawa Jakadiya ta soma jada baya tana duban Giwa cikeda tsoro...
“Rankidad’e Ki gafarceni amma ta yaya akayi haka....?!”
Giwa ta murmusa tace “Kar kiji tsoro Jakadiya nidake mun zama d’aya... Kinsan sirrikana da yawa... Yau zan sanar dake Sirrin da dagani sai Tal’udu saiko Marigayi Wambai ne muka sani... Sirrin da Wambai ya rufeta cikin K’undi...!”
Jakadiya dake rakub’e gefe har lokacin jikinta bai daina rawa ba take duban Giwa....
_WAIWAYE_
Gimbiya Turai d’iyace ga Sarki Jamaludeen na k’asar Benin, su biyu rak Allah ya baiwa Sarki Jamal... Daga ita sai k’aramin k’aninta mai suna Alfah... Sarki Jamal ya d’auki soyayyar duniya ya d’aura akan yaransa guda biyu Gimbiya Turai da kuma Yarima Alfah... Mahaifiyarsu ta rasu a lokacinda ta haifi Yarima Alfah, daga nan Sarki bai kuma haihuwa ba... Hakan sosai yayi dad’i ga Al’umman masarauta dake harin kujeran Sarki Jamal....Gimbiya Turai tanada wata Hadimarta wacce suke kusan s’anni saidai idan ma Hadimar tata zata d’ara mata bai wuce ta d’arata da Shekara d’aya zuwa biyu ba... Gimbiya Turai Allah yayita mace mai sauk’in kai da son Al’ummarta hakan yasa itada Hadimar tata mai suna Izzatu suka zamto aminai daga amintaka suka koma tamkar ‘yanuwa wanda suka fito ciki guda... Gimbiya Turai bata b’oyema Izzatu komai nata... A lokacinda d’an Sarki Mahmood Wato Sarki AbdulJabbar yaji labarin Gimbiya Turai na k’asar Benin... Al’adar k’asar ce a wancan lokacin Gimbiya bazata fita zance wajen manemin aurenta ba sabida mulki saidai Hadimarta ta fita suyi hira da mijin ita Hadimar sai ta kawo sak’on duk abinda aka fad’i a hiran ta gayawa Gimbiya... Kuma Hadimar idan ta fita itama bazata bud’e fuskarta ba har a gama hiran... A tak’aice miji bazai San fuskar matarsa ba sai randa aka kai masa ita gidansa...!”
Giwa Ta numfasa kana taci gaba da fad’in “Tun daga wannan lokacin da nayi shiga irinta masu mulki na rufa kaina na fita wajen Sarki AbdulJabbar a matsayin wacce ta fito ganawa da mijin da zata aura sai na d’and’ani zak’in mulki naji duniyar nan babu abinda ya kaita dad’i ashe... Ina can ina bauta... Uwa uba da na k’yallara idanu kan kyakkyawan Sarkin maiji da k’uruciya da Mulki naji duniyar nan bazan iya rayuwa ba taredashi ba... A lokacin mahaifin AbdulJabbar ya rasu za’a nad’asa sarauta akace sai yayi aure ai masa nad’i gaba d’aya... Hakan yasa yayi tattaki har Benin dan lokacin Sarki Jamal yayi sanarwa k’asashe daban daban cewa d’iyarsa zata zab’i miji, aka saka wa masu Mulki rana kowa yazo ya nuna bajintarsa... Toh koda yaran sarakuna da masu mulki suka Zo wannan gasa na zab’en gwani da Gimbiya Turai zatai Sarki AbdulJabbar bai sami halarta ba baida lafiya... D’anuwansa Wambai shi ya halarta a matsayin wakilin k’aninsa... Anyi gasar gwani Wambai yaci gasa yace ma Sarkin k’asarsu yaci wannan gasa kuma d’an uwansa... Wambai shi kad’ai yasan fuskar Gimbiya Turai ya dawo gida da labari mai dad’iga d’anuwansa Sarki AbdulJabbar... “
“Koda aka d’aura auren Sarki AbdulJabbar da Gimbiya Turai bata buk’aci a kawota wannan Masarautar da tarin Hadimai ba, a cewarta ni kad’ai na isheta.... Al’ada ce a wancan lokacin Matar Sarki bazata iso masarauta ba sai ta yada zango a wata k’aramar gari kafin Ta iso masarauta.. Hakan Ta faru damu... Nida Uwargijiyata Gimbiya Turai matar AbdulJabbar, Wambai wanda shine tsaye akan komai na auren d’an uwan nasa tin a lokacin na hango hassada da k’yashin d’aukaka da Allah ya baiwa d’an uwan nasa sama dashi, nayi amfani da wannan damar na rinjaye Wambai tinda shi yaje gasa shikadai yasan fuskar Gimbiya Turai Sarki AbdulJabbar bai sani ba... Muka had’e kai dashi cewa ni ce zan zamto matar AbdulJabbar da sharad’in zan taimaka masa mu kawar da AbdulJabbar ya d’ale Karagan mulkin mahaifinsu wanda shi ya kamata ya gada amma aka baiwa AbdulJabbar, naita gurb’ata masa zuciyarsa da tunani marassa kyau har na samu nasaran shawo kansa....A wannan garin na fantsama wata daji neman maganin da zan rufe bakin Gimbiya Turai, a nan na had’u da Tal’udu ya sanar dani banida matsala... Tal’udu ya zamto gatana, ya tura bak’in Aljani ya kashe Sarki Jamal na k’asar Benin Wato mahaifin Gimbiya Turai... Daga nan Gimbiya ta zamto batada kowa sai k’aramin k’aninta Alfah wanda shi a lokacin k’aramin yaro ne baida ko masaniyar Sarkin wata k’asa ce ya auri ‘yaruwarsa sabida k’ank’ancin shekaru nasa, yadai an gasa akai wani Sarki ta k’asashen gabas yaci gasar amma bai San wace k’asa bace....Tuni masu wawoson mulki sukai ma k’aragar mulkin caaa, aka mance da Alfah da ‘yaruwarsa Turai...
Saidai tin kafin na tareda Sarki AbdulJabbar Gimbiya Turai ta riga ta basa ni a matsayin kyauta, Wanda dama al’ada ne kyauta tsakanin sabbin ma’aurata, ka d’aga abu mai daraja ka baiwa partner d’inka... Toh ita sai ta basa baiwarta Izzatu a matsayin tukwici, labari ya isa masa daga wajen Wambai... Randa za’a kawoni masarauta ranan muka gana dashi dan tuni Tal’udu ya rufe bakin Gimbiya Turai duk abinda na bata umarni shi takeyi, haka nan mace da ita daga wancan lokacin itace Izzatu Hadimata ni kuma nice Uwargijiyarta Gimbiya Turai... Sadai ta sami kanta da amsa min da min biyayya dan bazata iya ce min a’a ba... Kallon farko ashe Sarki ya auka wa soyayyar Baiwa Izzatu....Sarki AbdulJabbar yabada umarnin a k’arasa dani Masarauta ita kuma Baiwar a bar masa ita a nan wannan garin zasu k’araso tare... Haushi da takaici ya cikani ta yaya gani nan sabuwar amaryarsa ya zab’i ya taho tareda Kuyanga... Na dad’a k’ullatan Turai wacce itace Izzatu a halin yanzu, na tsaneta da duka zuciyata dukda na sace identity nata da komai amma da alama Sarki yana son k’ulla alak’a da ita... Naji takaicin basa kyautar baiwa da tayi... Ashe bayan tafiyar mu Fada Sarki ya umarci Wambai a d’aura masu aure shida Baiwa Izzatu ya kuma riga tarewa da ita yayinda ni kuma muka taho Fada na ije Tal’udu nan cikin Masarauta tareda taimakon Waziri wanda tuni mun k’ulla alak’a dashi ba tareda sanin Mai Martaba ba musamman da mai Martaban ya sanar dani cewa ya tare da Baiwa Izzatu kuma ya aureta Ta zama matarsa kaman ni..
Nace atafau Baiwa bazata tab’a zamtowa kaman ni ba, dan haka dole ya barta a wancan garin Ta zauna a can idan yana neman zaman lafiya... Ban hanasa ya auro ko wata mace ya kawota cikin Fada ba amma banda baiwata Izzatu, nafi k’arfin nayi kishi da ita... Sarki ya amince da sharad’ina musamman da ya lura da irin halarcin da nai masa na basa kyautar Baiwa wacce ya aukawa soyayyarta har takaisu ga aure...!”
K’aik’ayi ya hana Giwa ci gaba da magana... Zumbur ta mik’e taceda Jakadiya su tafi wajen Tal’udu...
Jakadiya ta zaro idanu waje tace “Allah shi taimakeki yau kuma wajen Tal’udu rana tsage tsage....?!”
Tsawa Giwa ta dirara mata tana ci gaba da susa... Babu shiri Jakadiya Ta mik’e zumbur tana furta “Tuba nake Allah shi taimakeki..!!!”
SameenaAleeyou 📚*MUHIBBAH*
*53*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Dariya Tal’udu yake amma wani irin hayak’i ne Ke fitowa daga cikin bakin nasa... Yai alamawa Giwa data masto kusa sosai.... Babu shiri Giwa ta matsa kusansa tana lek’a cikin k’aton tulun tsafi da yake aza mata akanta duk randa za’ai mata wani aiki... Sannan duk randa tulun yaci wuta tabbas babu nasara a aikin da za’ayi....
Giwa ta shiga girgiza kai tana furta “Tal’udu kayi wani abin amma babu ta yanda za’ayi na yarda a kuma azamin wannan tukunyar azabar.. Kaga dik yanda sassan jikina Ke k’onewa, ga azaban k’ai....!”
Batakai aya ba ya katseta da fad’in “Ke Izzatu ba’a mana gardama a nan..!!!”
A zabure ta d’ago tana dubansa jin ya kirata da sunanta na yanka... Ta had’iyi miyau da k’yar tace “Maiyasa yau ka kirani da sunana na yanka...? Tsawon shekarun da mukai tare baka tab’a yin hakan ba..?!” Ta k’arashe tashin hankali bayyane saman fuskarta...
Wata dariyar mai wani irin sauti maras dad’in sauraro ya kumayi kana ya d’auko wata fitila mai launin ja ya haska cikin tulun dashi yace “Lek’a nan..!”
Babu musu Giwa ta lek’a cikin tulun da tuni jan fitilar ya haske ciki da wane irin jan haske maras kyaun gani...
Ga mamakinta Gimbiya Turai na k’asar Benin ta gani cikin shiga irinta mulki da sarauta babu yanayin hauka a tattereda ita... Gefe da ita zaratan mazaje ne guda biyu duk sunyi shiga irinta masu mulki saidai bata tantance fuskokin mazajen ba sabida hasken fitilar dake kawowa yana d’aukewa kaman walk’iya....
Zuciyar Giwa yaci gaba da bugawa, jikinta ya d’auki karkarwa... Ta d’ago a zabure tana duban Tal’udu dake rik’eda fitilar...
Baki na rawa Giwa Ke furta “Mai nake gani haka badai Izzatu ta sami lafiya ba..? Kuma a ina take...?!!”
Ya kuma darawa a karo na biyu yace “Ai saida naja miki kunne, saida na miki kashedi kan cewar kar Ki bari Ta kufce miki...!”
A fusace Giwa Ta katsesa da fad’in “Wannan kuma laifinka ne tinda aikinka kenan ka cika min duk wasu burika na wannan dalilin yasa na d’auko ka na aje cikin Masarautar nan... Idan dukuwa bazaka cika min burikana ba zamanka cikin Masarautar nan baida amfani... Tsohon kawai..!!”
Jakadiya Ta had’iyi miyau da k’yar tana jinjina ta’addanci irin na Giwa... A iyaka zatonta Izzatu Hadimarta ce aminattciya dataci amanarta ta aure Sarki AbdulJabbar bayan Giwa ta mallaka masa ita a matsayin tukuici ashe abin ba haka bane... Ashe Giwa Itace Hadimar Izzatu wacce Ta aminta da ita taci amanarta ta sace sunanta da rayuwarta harma da mijinta... Jiki na matuk’ar rawa Jakadiya ta soma jada baya tana duban Giwa cikeda tsoro...
“Rankidad’e Ki gafarceni amma ta yaya akayi haka....?!”
Giwa ta murmusa tace “Kar kiji tsoro Jakadiya nidake mun zama d’aya... Kinsan sirrikana da yawa... Yau zan sanar dake Sirrin da dagani sai Tal’udu saiko Marigayi Wambai ne muka sani... Sirrin da Wambai ya rufeta cikin K’undi...!”
Jakadiya dake rakub’e gefe har lokacin jikinta bai daina rawa ba take duban Giwa....
_WAIWAYE_
Gimbiya Turai d’iyace ga Sarki Jamaludeen na k’asar Benin, su biyu rak Allah ya baiwa Sarki Jamal... Daga ita sai k’aramin k’aninta mai suna Alfah... Sarki Jamal ya d’auki soyayyar duniya ya d’aura akan yaransa guda biyu Gimbiya Turai da kuma Yarima Alfah... Mahaifiyarsu ta rasu a lokacinda ta haifi Yarima Alfah, daga nan Sarki bai kuma haihuwa ba... Hakan sosai yayi dad’i ga Al’umman masarauta dake harin kujeran Sarki Jamal....Gimbiya Turai tanada wata Hadimarta wacce suke kusan s’anni saidai idan ma Hadimar tata zata d’ara mata bai wuce ta d’arata da Shekara d’aya zuwa biyu ba... Gimbiya Turai Allah yayita mace mai sauk’in kai da son Al’ummarta hakan yasa itada Hadimar tata mai suna Izzatu suka zamto aminai daga amintaka suka koma tamkar ‘yanuwa wanda suka fito ciki guda... Gimbiya Turai bata b’oyema Izzatu komai nata... A lokacinda d’an Sarki Mahmood Wato Sarki AbdulJabbar yaji labarin Gimbiya Turai na k’asar Benin... Al’adar k’asar ce a wancan lokacin Gimbiya bazata fita zance wajen manemin aurenta ba sabida mulki saidai Hadimarta ta fita suyi hira da mijin ita Hadimar sai ta kawo sak’on duk abinda aka fad’i a hiran ta gayawa Gimbiya... Kuma Hadimar idan ta fita itama bazata bud’e fuskarta ba har a gama hiran... A tak’aice miji bazai San fuskar matarsa ba sai randa aka kai masa ita gidansa...!”
Giwa Ta numfasa kana taci gaba da fad’in “Tun daga wannan lokacin da nayi shiga irinta masu mulki na rufa kaina na fita wajen Sarki AbdulJabbar a matsayin wacce ta fito ganawa da mijin da zata aura sai na d’and’ani zak’in mulki naji duniyar nan babu abinda ya kaita dad’i ashe... Ina can ina bauta... Uwa uba da na k’yallara idanu kan kyakkyawan Sarkin maiji da k’uruciya da Mulki naji duniyar nan bazan iya rayuwa ba taredashi ba... A lokacin mahaifin AbdulJabbar ya rasu za’a nad’asa sarauta akace sai yayi aure ai masa nad’i gaba d’aya... Hakan yasa yayi tattaki har Benin dan lokacin Sarki Jamal yayi sanarwa k’asashe daban daban cewa d’iyarsa zata zab’i miji, aka saka wa masu Mulki rana kowa yazo ya nuna bajintarsa... Toh koda yaran sarakuna da masu mulki suka Zo wannan gasa na zab’en gwani da Gimbiya Turai zatai Sarki AbdulJabbar bai sami halarta ba baida lafiya... D’anuwansa Wambai shi ya halarta a matsayin wakilin k’aninsa... Anyi gasar gwani Wambai yaci gasa yace ma Sarkin k’asarsu yaci wannan gasa kuma d’an uwansa... Wambai shi kad’ai yasan fuskar Gimbiya Turai ya dawo gida da labari mai dad’iga d’anuwansa Sarki AbdulJabbar... “
“Koda aka d’aura auren Sarki AbdulJabbar da Gimbiya Turai bata buk’aci a kawota wannan Masarautar da tarin Hadimai ba, a cewarta ni kad’ai na isheta.... Al’ada ce a wancan lokacin Matar Sarki bazata iso masarauta ba sai ta yada zango a wata k’aramar gari kafin Ta iso masarauta.. Hakan Ta faru damu... Nida Uwargijiyata Gimbiya Turai matar AbdulJabbar, Wambai wanda shine tsaye akan komai na auren d’an uwan nasa tin a lokacin na hango hassada da k’yashin d’aukaka da Allah ya baiwa d’an uwan nasa sama dashi, nayi amfani da wannan damar na rinjaye Wambai tinda shi yaje gasa shikadai yasan fuskar Gimbiya Turai Sarki AbdulJabbar bai sani ba... Muka had’e kai dashi cewa ni ce zan zamto matar AbdulJabbar da sharad’in zan taimaka masa mu kawar da AbdulJabbar ya d’ale Karagan mulkin mahaifinsu wanda shi ya kamata ya gada amma aka baiwa AbdulJabbar, naita gurb’ata masa zuciyarsa da tunani marassa kyau har na samu nasaran shawo kansa....A wannan garin na fantsama wata daji neman maganin da zan rufe bakin Gimbiya Turai, a nan na had’u da Tal’udu ya sanar dani banida matsala... Tal’udu ya zamto gatana, ya tura bak’in Aljani ya kashe Sarki Jamal na k’asar Benin Wato mahaifin Gimbiya Turai... Daga nan Gimbiya ta zamto batada kowa sai k’aramin k’aninta Alfah wanda shi a lokacin k’aramin yaro ne baida ko masaniyar Sarkin wata k’asa ce ya auri ‘yaruwarsa sabida k’ank’ancin shekaru nasa, yadai an gasa akai wani Sarki ta k’asashen gabas yaci gasar amma bai San wace k’asa bace....Tuni masu wawoson mulki sukai ma k’aragar mulkin caaa, aka mance da Alfah da ‘yaruwarsa Turai...
Saidai tin kafin na tareda Sarki AbdulJabbar Gimbiya Turai ta riga ta basa ni a matsayin kyauta, Wanda dama al’ada ne kyauta tsakanin sabbin ma’aurata, ka d’aga abu mai daraja ka baiwa partner d’inka... Toh ita sai ta basa baiwarta Izzatu a matsayin tukwici, labari ya isa masa daga wajen Wambai... Randa za’a kawoni masarauta ranan muka gana dashi dan tuni Tal’udu ya rufe bakin Gimbiya Turai duk abinda na bata umarni shi takeyi, haka nan mace da ita daga wancan lokacin itace Izzatu Hadimata ni kuma nice Uwargijiyarta Gimbiya Turai... Sadai ta sami kanta da amsa min da min biyayya dan bazata iya ce min a’a ba... Kallon farko ashe Sarki ya auka wa soyayyar Baiwa Izzatu....Sarki AbdulJabbar yabada umarnin a k’arasa dani Masarauta ita kuma Baiwar a bar masa ita a nan wannan garin zasu k’araso tare... Haushi da takaici ya cikani ta yaya gani nan sabuwar amaryarsa ya zab’i ya taho tareda Kuyanga... Na dad’a k’ullatan Turai wacce itace Izzatu a halin yanzu, na tsaneta da duka zuciyata dukda na sace identity nata da komai amma da alama Sarki yana son k’ulla alak’a da ita... Naji takaicin basa kyautar baiwa da tayi... Ashe bayan tafiyar mu Fada Sarki ya umarci Wambai a d’aura masu aure shida Baiwa Izzatu ya kuma riga tarewa da ita yayinda ni kuma muka taho Fada na ije Tal’udu nan cikin Masarauta tareda taimakon Waziri wanda tuni mun k’ulla alak’a dashi ba tareda sanin Mai Martaba ba musamman da mai Martaban ya sanar dani cewa ya tare da Baiwa Izzatu kuma ya aureta Ta zama matarsa kaman ni..
Nace atafau Baiwa bazata tab’a zamtowa kaman ni ba, dan haka dole ya barta a wancan garin Ta zauna a can idan yana neman zaman lafiya... Ban hanasa ya auro ko wata mace ya kawota cikin Fada ba amma banda baiwata Izzatu, nafi k’arfin nayi kishi da ita... Sarki ya amince da sharad’ina musamman da ya lura da irin halarcin da nai masa na basa kyautar Baiwa wacce ya aukawa soyayyarta har takaisu ga aure...!”
K’aik’ayi ya hana Giwa ci gaba da magana... Zumbur ta mik’e taceda Jakadiya su tafi wajen Tal’udu...
Jakadiya ta zaro idanu waje tace “Allah shi taimakeki yau kuma wajen Tal’udu rana tsage tsage....?!”
Tsawa Giwa ta dirara mata tana ci gaba da susa... Babu shiri Jakadiya Ta mik’e zumbur tana furta “Tuba nake Allah shi taimakeki..!!!”
SameenaAleeyou 📚*MUHIBBAH*
*53*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Dariya Tal’udu yake amma wani irin hayak’i ne Ke fitowa daga cikin bakin nasa... Yai alamawa Giwa data masto kusa sosai.... Babu shiri Giwa ta matsa kusansa tana lek’a cikin k’aton tulun tsafi da yake aza mata akanta duk randa za’ai mata wani aiki... Sannan duk randa tulun yaci wuta tabbas babu nasara a aikin da za’ayi....
Giwa ta shiga girgiza kai tana furta “Tal’udu kayi wani abin amma babu ta yanda za’ayi na yarda a kuma azamin wannan tukunyar azabar.. Kaga dik yanda sassan jikina Ke k’onewa, ga azaban k’ai....!”
Batakai aya ba ya katseta da fad’in “Ke Izzatu ba’a mana gardama a nan..!!!”
A zabure ta d’ago tana dubansa jin ya kirata da sunanta na yanka... Ta had’iyi miyau da k’yar tace “Maiyasa yau ka kirani da sunana na yanka...? Tsawon shekarun da mukai tare baka tab’a yin hakan ba..?!” Ta k’arashe tashin hankali bayyane saman fuskarta...
Wata dariyar mai wani irin sauti maras dad’in sauraro ya kumayi kana ya d’auko wata fitila mai launin ja ya haska cikin tulun dashi yace “Lek’a nan..!”
Babu musu Giwa ta lek’a cikin tulun da tuni jan fitilar ya haske ciki da wane irin jan haske maras kyaun gani...
Ga mamakinta Gimbiya Turai na k’asar Benin ta gani cikin shiga irinta mulki da sarauta babu yanayin hauka a tattereda ita... Gefe da ita zaratan mazaje ne guda biyu duk sunyi shiga irinta masu mulki saidai bata tantance fuskokin mazajen ba sabida hasken fitilar dake kawowa yana d’aukewa kaman walk’iya....
Zuciyar Giwa yaci gaba da bugawa, jikinta ya d’auki karkarwa... Ta d’ago a zabure tana duban Tal’udu dake rik’eda fitilar...
Baki na rawa Giwa Ke furta “Mai nake gani haka badai Izzatu ta sami lafiya ba..? Kuma a ina take...?!!”
Ya kuma darawa a karo na biyu yace “Ai saida naja miki kunne, saida na miki kashedi kan cewar kar Ki bari Ta kufce miki...!”
A fusace Giwa Ta katsesa da fad’in “Wannan kuma laifinka ne tinda aikinka kenan ka cika min duk wasu burika na wannan dalilin yasa na d’auko ka na aje cikin Masarautar nan... Idan dukuwa bazaka cika min burikana ba zamanka cikin Masarautar nan baida amfani... Tsohon kawai..!!”