Sashe 120
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Innalillahi wa inna’ilaihi ilaihi raji’un..! Kalaman da zukatansu Ke iya nanatawa kenan...! Ja’afar da yaji batun a wane irin ba zata d’ago gajiyyayun idanunsa yai yana kuma duban matar da Ubandoma ya gama sanar dasu cewa itace mahaifiyarsa kuma shid’in ba Bawa bane d’ah ne ga Sarki AbdulJabbar mai rasuwa... Giwa itace ta rabasa da mahaifiyarsa ta kuma maidasa Bawa k’ask’antacce a gidan Mahaifinsa... Ya rayu a matsayin Bawa a cikin Masarautarsa..! Shin wannan zalunci da mai yayi kama...!! Sosai jikinsa yake rawa gumi na kuma karyo masa dukda iskan damuna dake hurawa, ji yake kaman numfashinsa na neman d’aukewa ya bar jikinsa.... Bai kuma fahimtar meke faruwa ba saida yaji hannun matar nan tana shafa fuskarsa cikin rawar murya take furta “Kaid’in d’ahna ne..! Tabbas kai d’in d’ah na ne... Domin kuwa jikina ya bani akwai abuna mai mahimmanci a gefen d’akinda Ubandoma ya rufe ni.. Ban fasa kankare jikin ginin ba, ban kuma amince na tafi na barka hannun azzaluman nan ba har saida na tabbatar Allah ya kub’utar damu tare...! D’anah.! Jaririna..!!!” Wane irin kuka mai k’arfi ya kufce mata tana mai janyo Ja’afar d’in cikin jikinta da tuni ya koma tamkar wanda yayi sumar tsaye..! Jijiyoyin jikinsa sai mimmik’ewa yake ba komai yake tunawa ba face irin wulak’ancin da yaran Giwa sukai masa musamman Yazeed da Jamal, Yazeed akan tsananin son Mulki da izza shi kuwa Jamal akan Umaima ne... Ya tuna akwai wani rana da Yazeed ya take gadon bayansa ya d’ale doki, ya tuna akwai wata rana da Jamal ya sakasa ya sumbaci takalminsa dan ya gansu da Umaima kawai don ya nuna masa cewa shid’in k’ask’antacce ne bai dace da basarakiya jinin sarauta kaman Umaima ba....Dan ma shid’in Allah yayisa mai taurin kai da kafiya ne tun a baya lokacin yana matsayin Bawa, yakanyi abu tamkar ba Bawa ba musamman idan ka tasamma tab’a mutuncinsa sam bazai barka ka k’ask’antashi ba a matsayinsa na d’anAdam wanda Ubangijin talikai gaba d’aya ya d’aga darajan d’an adam kan sauran halittun duniya..! Shi mutum ko yaya ka gansa ba abun wulak’antawa bane, baka San kalan Baiwar da Ubangijinsa yai masa ba, kuma bakasan koma ya fika daraja a wajen mahaliccinku ba, idan yafika tsoron Allah sai ya fika daraja..! Sam Shari’a bata bama kowa daman kaci zarafin wani wanda yake k’arashinka ba koda kuwa bawanka ne...!
Ya dinga tuna ire iren cin mutunci da wulak’anci da ya fuskanta daga wajen wannan ahali... Sai yanzu komai yake dawo masa daki daki, watak’ila Mai Martaba ya fahimci shine mahaifinsa na asali da Giwa ta fahimci hakan shine ta kashe mai Martaba shima kuma Ta nemesa zata kashesa.. Wannan mata takai mak’ura wajen zalunci... Shi ko a labarun hikayoyi da ake karanto masu da cikin Fada bai tab’a cin karo da labarin azzaluman Baiwa irin Izzatu ba...! Amma zuluncinta yazo k’arshe da izinin Allah, sai ta girbi duk abinda ta shuka daga ita har yaranta guda biyu...! Yana mamakin yanda Yarima Mahmood ya kasance daga cikin ahalin wannan azzalumar mata domin kuwa shid’in ya banbanta da muguwar ahali irin wannan.. Kodashike Allah yakan fidda rayayye daga cikin macecce sannan ya kan fidda macecce daga rayeyye... Domin kuwa babu abinda yafi k’arfin buwayarsa...! Ja’afar ya lumshe idanunsa a hankali sanda yaji hannun Gimbiya Turai tana shafe fuskarsa da ruwa dan su duk a zatonsu suma yayi...! Yaja wane irin dogon numfashi had’ida sauk’e idanunsa kan matar, yai mata K’uri bayanan kalan azabtarwa da muzgunawa had’ida mummunan cin amanan da Baiwar ta tai mata na kuma yawo a kwanyarsa...!
Hawaye suka soma gangarowa daga idanunsa wanda tuni Sun kad’a sunyi jazir.... Ji yayi yakai hannunsa dake tsananin rawa saman fuskarta yana share mata hawayen dake kuma gangaro mata. Cikin rawar murya yake furta “Ta cutar dake..! Ta miki zalunci mafi muni Ummi tah... Ta maidaki Baiwa cikin gidan Mijinki sannan Ta maida d’anki Bawa cikin gidan mahaifinsa... Daga k’arshe ta haukataki ta kuma salwantar da sauran ahalinki..! Wannan matar bata cancanci yafiya ba domin idan na yafe mata ni kaina bazan iya yafewa kaina ba sabida abubuwan da tai miki Mahaifiyata..!!” Ya k’arashe cikin wane irin cazgan kuka..! Tuni Gimbiya ma kukan ya kufce mata suka had’e goshinsu itada d’anta Ja’afar waje guda suna yin mai isarsu...!!
Tirk’ashi..! Rayuwa mai bud’e ma Bawa shafuka daban daban, ko wanne da yanda yake zuwa maka, wad’annan bayin Allah rayuwa ta kuma bud’e masu sabbin shafuka.. Bayan tsawon shekarun nan gashi Allah ya had’a fuskokinsu, tabbas tsanani yana tareda sauk’i mai hak’uri shikeda riba...!
Bayan komai ya tsagaita Baba Nomau ya nusa had’ida furta “Alhamdulillahi..! Alhamdulillah...! Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Ubangijin da babu wani bayan shi, mai mulkin Sammai da k’assai da abinda ke cikinsu da abinda ke tsakaninsu, tsira da amincinsa su sake tabbata ga Annabinsa fiyayyen halitta wanda babu yashi, Manzon tsira (S.A.W)...!”
Ya juyo kad’an ya dubi Ubandoma yace “Hak’ik’a ka tapka kurakurai a baya, wanda a ajizancinmu na ‘yan adam zai wahala wani ya yafe maka..! Ubangijinmu ne zamuyi masa laifi duk girmanta duk yawanta ya kuma gafarta mana mu maimaita mu kuma sake rok’onsa ya yafe mana matuk’a bazamu masa tarayya wajen bauta masa ba... Shirka itace mafi munin zalunci da Bawa zai aikataga Ubangijinsa a doron k’asa, Shirka itace mafi girman laifi da mutum zai mutu yanayi Ubangiji bazai gafarta masa ba.. Amma duk wani laifi bayan shirka Ubangiji mai iya gafartawa ne idan yaso domin shid’in shine Algaffar kuma Arraheem..! Ka tapka kurakurai a baya amma daga k’arshe ka gane kuskurenka kuma kayi abinda ya dace sannan ka rok’i Ubangijinka gafara, Muna fata ya gafarta mana baki d’aya... Sannan muna fata wad’anda kaima wannan aika aika su gafarta maka domin shi addu’an wanda aka zalunta babu hijabi tsakaninsa da Ubanginsa..! Sannan ko a Shari’a idan an maka laifi ka rama gwargwadon abinda aka maka bakayi laifi ba amma saidai da zaka zamto mai afuwa da yafiya sai ya fi maka alkhairi... Allah yana son masu afuwa kuma yana tareda masu hak’uri..!”
Ya maidoda dubansa ga Ja’afar da mahaifiyarsa wanda kawunasu ke k’asa suna saurarensa, Baba Nomau yaci gaba da fad’in “An zalunceku kuma an cutar daku... Wannan mushirikar matar Ta maku zalunci mafi muni amma ku sani wani shari’ar sai a lahira..! Tinda Allah yasa duk mun fahimci haka kuma ya baki lafiya a halin yanzu ya kuma had’a fuskarki dana d’anki bayan kun d’ibe tsammanin sake had’uwa da juna.. Sai mu gode masa da wannan rahama nasa sannan gobe idan Allah yasa muna cikin masu nisan kwana mu d’unguma mu koma Masarauta a ida warware komai..!”
Gimbiya Turai ta jinjina kai tace “Haka ne Baba...!”
Ja’afar ma jinjina kansa yayi saidai kafin yakaiga furta wani kalma Ubandoma ya katsesu da fad’in “Bazan iya komawa Masarautar nan ba har sai na tabbata kun yafe min... Dan Allah ku yafe min duk abubuwan da nai maku a baya...!!”
Murmusawa Gimbiya Turai tai tace “Na yafeka tuntuni tun lokacin da ka zab’i kayi abinda ya dace bayan kanada damar da zaka kuma mik’ani hannun wannan azzalumar Baiwar, amma ka zab’i kayi abinda ya dace kayi sanadiyar kub’utarmu nida d’ah na ka kuma kawo mu yanda maganinmu yake cikin hukuncin Ubangiji da ikonsa..! Kaima abin mu maka godiya ne Ubandoma... Allah Ubangiji ya saka maka da mafificin alkhair bisa abinda kayi...!”
Ubandoma ya duk’a yana hawaye yake furta “Na gode na gode Rankidad’e..! Ubangiji ya k’ara girma..!”
Ya kaikaito kad’an yana duban Ja’afar... Kafin yayi magana Ja’afar yayi saurin d’agosa ya rungumesa, lokaci guda yake furta “Tun zamanin da nake na matsayin Bawa cikin Masarauta baka tab’a muzguna mun ba hasalima kai d’in kana d’aya daga cikin masu kwatanta alkhairi a gareni.. Sannan daga k’arshe kamin abinda bazan iya saka maka ba koda kuwa daga farko ka zamto silan shiga rayuwar da na girma na tsinci kaina ciki..! Na gode maka Baba..!”
Ubandoma na hawaye yake furta “Rankaidad’e nifa Bawanka ne ka daina furta min kalman godiya.. Ka barni na duk’a gabanka..!”
Ja’afar na murmushi yake furta “Ni dakai duk d’aya muke wajen Allah mu duka bayinsa ne kuma har kullum kai d’in tamkar Uba ne a gareni dan bazan mance yanda ka kula dani ba bayan babu iyayen da na girma na sansu matsayin iyayena.. Babu k’ask’antacce sai wanda ya k’ask’antar da kanshi kaji koh..!”
Cikin sauri Ubandoma ya shiga jinjina kai cikeda jin dad’i yana kuma godiya... Fuskoki suka cika da annuri da Farin ciki... Ja’afar da mahaifiyarsa suka kasa sakin juna sabida Farin ciki.. Gani take kaman wani abu zai kuma giftawa ya raba tsakaninta da d’anta...!
Baba Nomau ya kuma basu wasu add’u’o’i yace suyita nanatawa suna ambaton Allah domin kuwa duk yanda wad’anda suka cutar dasu suke suna cikin tashin hankali...
**
Tinda suka baro asibitin wajen Yazeed yake shek’a gudu saman kwalta daga gani zaka fahimci neman hanyar fitar da b’acin ransa kurum yake, ya kasa yarda ‘yan uwansa da mahaifiyarsa zasu aikata irin mugun abinda yaji sun aikata, Allah ya gani ko k’aunar ganin fuskokinsu baya yi shiyasa ma koda suka iso asibitin yake alla alla ya fice daga cikin asibtin... Babu yanda Turaki bai ba ya basa motar ya tuk’a amma yak’i sai zuba gudu dasu yake saman kwalta... Bai cewa uffan sai shek’a gudu yake jijiyoyin jikinsa suna kuma fitowa duk sanda kalman fyad’e da k’annensa suka aikata ma k’aramar yarinyar nan zaizo zuciyarsa.. Idanunsa suna kuma kad’awa...! Turaki kansa ya rasa gane kan abokin nasa, tashin hankalin da yake hangowa tattareda Mahmood d’in yafi k’arfin ace dan sabida iftila’in da ya aukawa Yazeed da ahalinsa yake ciki tinda yasan abokin masa musulmi ne kuma yayi imani da K’addara mai kyau ko akasinta... Amma ya rasa gane ina tauhidin abokin nasa ya tafi yake neman yin wasa da rayuwarsu saman kwalta... Shi kansa Turaki bai iya cewa komai sai ambaton Allah kurum da yake cikin zuciyarsa....
**
Ya dinga tuna ire iren cin mutunci da wulak’anci da ya fuskanta daga wajen wannan ahali... Sai yanzu komai yake dawo masa daki daki, watak’ila Mai Martaba ya fahimci shine mahaifinsa na asali da Giwa ta fahimci hakan shine ta kashe mai Martaba shima kuma Ta nemesa zata kashesa.. Wannan mata takai mak’ura wajen zalunci... Shi ko a labarun hikayoyi da ake karanto masu da cikin Fada bai tab’a cin karo da labarin azzaluman Baiwa irin Izzatu ba...! Amma zuluncinta yazo k’arshe da izinin Allah, sai ta girbi duk abinda ta shuka daga ita har yaranta guda biyu...! Yana mamakin yanda Yarima Mahmood ya kasance daga cikin ahalin wannan azzalumar mata domin kuwa shid’in ya banbanta da muguwar ahali irin wannan.. Kodashike Allah yakan fidda rayayye daga cikin macecce sannan ya kan fidda macecce daga rayeyye... Domin kuwa babu abinda yafi k’arfin buwayarsa...! Ja’afar ya lumshe idanunsa a hankali sanda yaji hannun Gimbiya Turai tana shafe fuskarsa da ruwa dan su duk a zatonsu suma yayi...! Yaja wane irin dogon numfashi had’ida sauk’e idanunsa kan matar, yai mata K’uri bayanan kalan azabtarwa da muzgunawa had’ida mummunan cin amanan da Baiwar ta tai mata na kuma yawo a kwanyarsa...!
Hawaye suka soma gangarowa daga idanunsa wanda tuni Sun kad’a sunyi jazir.... Ji yayi yakai hannunsa dake tsananin rawa saman fuskarta yana share mata hawayen dake kuma gangaro mata. Cikin rawar murya yake furta “Ta cutar dake..! Ta miki zalunci mafi muni Ummi tah... Ta maidaki Baiwa cikin gidan Mijinki sannan Ta maida d’anki Bawa cikin gidan mahaifinsa... Daga k’arshe ta haukataki ta kuma salwantar da sauran ahalinki..! Wannan matar bata cancanci yafiya ba domin idan na yafe mata ni kaina bazan iya yafewa kaina ba sabida abubuwan da tai miki Mahaifiyata..!!” Ya k’arashe cikin wane irin cazgan kuka..! Tuni Gimbiya ma kukan ya kufce mata suka had’e goshinsu itada d’anta Ja’afar waje guda suna yin mai isarsu...!!
Tirk’ashi..! Rayuwa mai bud’e ma Bawa shafuka daban daban, ko wanne da yanda yake zuwa maka, wad’annan bayin Allah rayuwa ta kuma bud’e masu sabbin shafuka.. Bayan tsawon shekarun nan gashi Allah ya had’a fuskokinsu, tabbas tsanani yana tareda sauk’i mai hak’uri shikeda riba...!
Bayan komai ya tsagaita Baba Nomau ya nusa had’ida furta “Alhamdulillahi..! Alhamdulillah...! Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Ubangijin da babu wani bayan shi, mai mulkin Sammai da k’assai da abinda ke cikinsu da abinda ke tsakaninsu, tsira da amincinsa su sake tabbata ga Annabinsa fiyayyen halitta wanda babu yashi, Manzon tsira (S.A.W)...!”
Ya juyo kad’an ya dubi Ubandoma yace “Hak’ik’a ka tapka kurakurai a baya, wanda a ajizancinmu na ‘yan adam zai wahala wani ya yafe maka..! Ubangijinmu ne zamuyi masa laifi duk girmanta duk yawanta ya kuma gafarta mana mu maimaita mu kuma sake rok’onsa ya yafe mana matuk’a bazamu masa tarayya wajen bauta masa ba... Shirka itace mafi munin zalunci da Bawa zai aikataga Ubangijinsa a doron k’asa, Shirka itace mafi girman laifi da mutum zai mutu yanayi Ubangiji bazai gafarta masa ba.. Amma duk wani laifi bayan shirka Ubangiji mai iya gafartawa ne idan yaso domin shid’in shine Algaffar kuma Arraheem..! Ka tapka kurakurai a baya amma daga k’arshe ka gane kuskurenka kuma kayi abinda ya dace sannan ka rok’i Ubangijinka gafara, Muna fata ya gafarta mana baki d’aya... Sannan muna fata wad’anda kaima wannan aika aika su gafarta maka domin shi addu’an wanda aka zalunta babu hijabi tsakaninsa da Ubanginsa..! Sannan ko a Shari’a idan an maka laifi ka rama gwargwadon abinda aka maka bakayi laifi ba amma saidai da zaka zamto mai afuwa da yafiya sai ya fi maka alkhairi... Allah yana son masu afuwa kuma yana tareda masu hak’uri..!”
Ya maidoda dubansa ga Ja’afar da mahaifiyarsa wanda kawunasu ke k’asa suna saurarensa, Baba Nomau yaci gaba da fad’in “An zalunceku kuma an cutar daku... Wannan mushirikar matar Ta maku zalunci mafi muni amma ku sani wani shari’ar sai a lahira..! Tinda Allah yasa duk mun fahimci haka kuma ya baki lafiya a halin yanzu ya kuma had’a fuskarki dana d’anki bayan kun d’ibe tsammanin sake had’uwa da juna.. Sai mu gode masa da wannan rahama nasa sannan gobe idan Allah yasa muna cikin masu nisan kwana mu d’unguma mu koma Masarauta a ida warware komai..!”
Gimbiya Turai ta jinjina kai tace “Haka ne Baba...!”
Ja’afar ma jinjina kansa yayi saidai kafin yakaiga furta wani kalma Ubandoma ya katsesu da fad’in “Bazan iya komawa Masarautar nan ba har sai na tabbata kun yafe min... Dan Allah ku yafe min duk abubuwan da nai maku a baya...!!”
Murmusawa Gimbiya Turai tai tace “Na yafeka tuntuni tun lokacin da ka zab’i kayi abinda ya dace bayan kanada damar da zaka kuma mik’ani hannun wannan azzalumar Baiwar, amma ka zab’i kayi abinda ya dace kayi sanadiyar kub’utarmu nida d’ah na ka kuma kawo mu yanda maganinmu yake cikin hukuncin Ubangiji da ikonsa..! Kaima abin mu maka godiya ne Ubandoma... Allah Ubangiji ya saka maka da mafificin alkhair bisa abinda kayi...!”
Ubandoma ya duk’a yana hawaye yake furta “Na gode na gode Rankidad’e..! Ubangiji ya k’ara girma..!”
Ya kaikaito kad’an yana duban Ja’afar... Kafin yayi magana Ja’afar yayi saurin d’agosa ya rungumesa, lokaci guda yake furta “Tun zamanin da nake na matsayin Bawa cikin Masarauta baka tab’a muzguna mun ba hasalima kai d’in kana d’aya daga cikin masu kwatanta alkhairi a gareni.. Sannan daga k’arshe kamin abinda bazan iya saka maka ba koda kuwa daga farko ka zamto silan shiga rayuwar da na girma na tsinci kaina ciki..! Na gode maka Baba..!”
Ubandoma na hawaye yake furta “Rankaidad’e nifa Bawanka ne ka daina furta min kalman godiya.. Ka barni na duk’a gabanka..!”
Ja’afar na murmushi yake furta “Ni dakai duk d’aya muke wajen Allah mu duka bayinsa ne kuma har kullum kai d’in tamkar Uba ne a gareni dan bazan mance yanda ka kula dani ba bayan babu iyayen da na girma na sansu matsayin iyayena.. Babu k’ask’antacce sai wanda ya k’ask’antar da kanshi kaji koh..!”
Cikin sauri Ubandoma ya shiga jinjina kai cikeda jin dad’i yana kuma godiya... Fuskoki suka cika da annuri da Farin ciki... Ja’afar da mahaifiyarsa suka kasa sakin juna sabida Farin ciki.. Gani take kaman wani abu zai kuma giftawa ya raba tsakaninta da d’anta...!
Baba Nomau ya kuma basu wasu add’u’o’i yace suyita nanatawa suna ambaton Allah domin kuwa duk yanda wad’anda suka cutar dasu suke suna cikin tashin hankali...
**
Tinda suka baro asibitin wajen Yazeed yake shek’a gudu saman kwalta daga gani zaka fahimci neman hanyar fitar da b’acin ransa kurum yake, ya kasa yarda ‘yan uwansa da mahaifiyarsa zasu aikata irin mugun abinda yaji sun aikata, Allah ya gani ko k’aunar ganin fuskokinsu baya yi shiyasa ma koda suka iso asibitin yake alla alla ya fice daga cikin asibtin... Babu yanda Turaki bai ba ya basa motar ya tuk’a amma yak’i sai zuba gudu dasu yake saman kwalta... Bai cewa uffan sai shek’a gudu yake jijiyoyin jikinsa suna kuma fitowa duk sanda kalman fyad’e da k’annensa suka aikata ma k’aramar yarinyar nan zaizo zuciyarsa.. Idanunsa suna kuma kad’awa...! Turaki kansa ya rasa gane kan abokin nasa, tashin hankalin da yake hangowa tattareda Mahmood d’in yafi k’arfin ace dan sabida iftila’in da ya aukawa Yazeed da ahalinsa yake ciki tinda yasan abokin masa musulmi ne kuma yayi imani da K’addara mai kyau ko akasinta... Amma ya rasa gane ina tauhidin abokin nasa ya tafi yake neman yin wasa da rayuwarsu saman kwalta... Shi kansa Turaki bai iya cewa komai sai ambaton Allah kurum da yake cikin zuciyarsa....
**