← Book details Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 115 OF 162

Sashe 115

Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A tare suka saka kai k’asan rumfar yanda Mama Tabawa Ke haske Mahaukaciya Izzatu sai aman bak’ak’en zaren masu kama da saiwar itaciya take... Ga wasu dogayen bak’ak’en allurai masu kamanni da k’ayar beguwa tana amo dasu...

Baba Nomau da k’arasowarsa kenan hamdala ya soma yana furta “Allah ya amshi addu’armu gashi nan ta fitar da mugun k’ullin tun kafin kwanaki uku su cika... Alhamdulillahi Allah abin godiya..!”

Yana ida fad’in haka ya zauna daga can gefe saman tabarmarsa ta azara.. Ya dubi Ubandoma da Jafaru yace suma su zauna...!

Babu musu sukayi yanda Baba Nomau yace....

SameenaAleeyou 📚

*MUHIBBAH*

*70*

*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*

Tambayoyi Baba Nomau yake jero mata daki daki tana amsawa “Zaki iya tuna wacece ke, daga wace nahiyar kike..? Kuma yaya akayi kika k’are a halinda kika tsinci kanki ciki...?!”

Ta d’ago ta dubesu d’aya bayan d’aya kana ta jinjina kai a hankali, cikin tsananin sanyin murya Ta furta “Sunana Turai, ni d’iya ce ga Sarkin Benin Jamaluddeen...!” Ta d’anyi fasali sai kuma taci gaba da fad’in “Allah shi ya k’addari kasancewata a yanayin da na tsinci kaina ciki domin kuwa Bawa bai shige k’addararsa...!”

Baba Nomau ya murmusa a hankali yana mai jinjina kai yake furta “Wannan haka ne..!”
Gimbiya Turai taci gaba da fad’in “Amma Amintattar Hadimata wacce na aminta da ita ta zamto tamkar ‘yar uwa a gareni itace tayi sanadiyan halinda na tsinci kaina ciki..! Sabida tsananin amintaka dake tsakaninmu a wancan lokacin wasu har cewa suke muna da kamanni, kasancewar ban zab’i Hadimata ba saida na darje na zab’o mai kyau cikin Hadimaina wacce muke kusan tsara a shekare, dan tun ina yarinya ‘yar kimanin shekaru takwas na zab’o Izzatu matsayina wacce zata zamto amintattar Hadimata, harta abinci da wasanni tare mukeyi da ita koda kuwa sauran ‘yan uwanta Bayi basa k’aunar suga hakan... Saidai ni sam bai dameni ba dan tuni Allah ya jefa k’aunar junanmu cikin zukatanmu, wasu lokutan haka zan tashi daga bacci naga Izzatu rik’eda mahuci tana min fififta, sai nace mata Ta hawo gadon itama ta kwanta, tun tana tsoro har Ta daina tsoro, dai dai da ‘yar tsanata tare muke wasa da... Tayita d’aukan ‘yar tsanar tana mata kitso, wasu lokutan har tambayata take ta saka tufafi na, ni kuwa nakan ce mata duk wani abuna nata ne, kada ta damu...! Da murnanta takan saka tufafin tayita kallon kanta jikin madubi... Wata rana ne data saka tufafun ta fito dasu jikinta bayi ‘yan uwanta sukayi mata chaa har horo saida akayi mata... Tayita kuka har ta d’an ja jiki dani... Abinka da yarinta sai nace da ita ta kwantar da hankalinta itama wata ran zata zamto mai mulki idan ma tana so ni zan bata nawa mulkin mu raba...Wannan kalman da na Fad’i ashe Izzatu tana rik’edashi har zuwa girma cewa itama zata zamto mai Mulki zamu raba nawa sarautar mu biyu....Tai shiru hawaye na gangaro mata...

Baba Nomau ya nusa yace “Zaki iya tuna ko mai tayi miki...?!”

Ta d’ago ta d’an kuma dubansu kana Ta jinjina kai tace “K’warai zan iya tunawa..!” Take ta shiga jero masu bayanin yanda Giwa ta amshe mata mijinta da kuma sarautar Ta ta maida ita Baiwa a gidan aurenta...!
Ja’afar ya kasa motsawa sai duban matar yake da tsananin mamaki, ya kasa aminta abubuwan da yaji gaskiya ne Wai Giwa Baiwa ce ba Basarakiya ba, ya kasa aminta da abubuwan da yake ji na fitowa daga bakin matar nan...!

Gimbiya Turai taci gaba da basu labari

“Tin daga lokacin da Izzatu ta jefeni da muguwar asirinta na zamto banida ta cewa sai abinda tace... Bokanta ya sanar asirinta zai tasiri akaina na d’an wane lokaci, bayan wanann lokacin asirin zai karye sabida tun lokacin da aka haifeni an dafani da magunguna na bada kariya, kunsan gidajen Sarauta sun yarda da neman tsari kuma ko wanne gidan Sarauta da nasu al’adar, musamman zamanin da da ilimi bai yawaita ba, hakan yasa sam hankalin Izzatu bai kwanta ba dukda cewa banida Ta cewa a wajen kowa sai abinda ta min umarni, daidai da sunanan na asali banida iko akansa dan tuni Ta mana musayen sunaye, na kuma yi na’am da abinda tace, na soma amsa sunan Izzatu tin daga wannan lokacin, ita kuwa ta koma amsa sunan Gimbiya Turai ta k’asar Benin....”
“Kaman yanda Izzatu ta buk’ata kan cewa mijinmu bayan ya ‘yantani daga bauta ya aureni ya maidani matarsa bayan ta kyautar dani garesa matsayin tukuici, Toh sai aka barni a wancan garin yanda muka soma zama nidashi, sam Izzatu bata bari an kaini cikin Masarauta ba koda da rana guda ne...! Ina zaune a wannan gari matsayin Matar sarki kuyangarsa wacce ya ‘yanta ya kuma aura... Tunda Sarki yasa k’afa ya koma masarauta ban kuma saka shi a idanu na ba, Ina zaune a wannan garin ina zaman jiran tsammani daga ni sai Hadimata mai suna Fattu saiko mijinta mai suna Giro, suna zaune ne a wani b’angare na cikin gidan dan kula dani kaman yanda Mai Martaba yai masu umarni ya kuma ajesu a kusana..Toh muna zaune a wannan k’aramar k’auye ga laulayi da ya addabeni, dan tinda Sarki ya tafi ban kuma yin lafiya ba...! Kwatsam wata rana ina tsaka da amai saiga Izzatu tazo ta wannan gidan ba tareda rakiyar kowa ba, dan ko Hadimanta bata taho dasu ba, ta razana sosai da ganin halinda nake ciki... Tin daga nesa ta tsaya ta zuba min idanu tana duban yanda nake durk’ushe tsakar gidan shek’a amai.. Ta k’araso Ta dafa kafad’ata tace “Ke Izzatu mai zan gani, amai..! Ciki..!” Ta shiga zaro idanunta waje tana dubana.. Duk’awa tayi gefena tace “toh kina jina koda wasa kada ki tura sak’o wa mai Martaba cewa kina d’aukeda juna biyu, kinji abinda na fad’a miki...!!”

Cikin sauri na shiga jinjina kai dan idan baku mance ba na sanar daku cewa Asirin da Izzatu tamin shine duk abinda ta bani umarni na amsa mata nai mata biyayya irin yanda bawa yakema Ubangidansa, ko kusa bana mata musu...
Ta murmusa tace dani na mik’e tsaye..! Babu musu nayi yanda tace..! Ta d’aga tufafina tana duban shafeffen cikina wanda babu wani alamu, sai gani nayi tana murmushi... Wani bak’in Dutse ta manna min a saman cikin... Naji wane irin zogi ya ratsa cikin jikina tinda ta manna min wannan bak’in dutsin..!
Koda ta manna min tsugunawa nayi wajen Ina rik’e marana dake tsananin min zogi... Take naga ta juya ta bani baya wani mummunan halitta ya bayyana gefenta sanye da bak’ak’en tufafi, dariya ya kece dashi yace “Wannan juna biyu bazai fice ba sai an haifosa duniya... Kuma shine zai zamto d’ah na farko ga Sarki AbdulJabbar...!”

Giwa ta shiga girgiza kai tana fad’in “Bazai yuwu ba..! Wanann k’ask’antacciyar baiwar bazata rigani baiwa mijina Magaji ba domin kuwa ni ce nan zan kafa Mulki na a wannan Masarautar, kowa sai ya zamto yana k’ark’ashin iko na...Menene abinyi..?!”

Daga nan ban kuma jin tattaunawarsu da matsafin mutumin data shigo tareda shi ba nidai na kwanta nan wajen ina rik’e marata dake tsananin murd’a min Ina neman agaji... Can da jimawa Fattu tazo ta taddani, cikin rawar jiki take fad’in “Rankidad’e..! Lafiya kike..?! Rankidad’e ko na kira Giro ne ya nemo amalanke mu fitar dake gari mu kaiki asibiti...?!”
Girgiza mata kai nayi nace “Fattu ba sai kun fitar dani ba ki bani ruwa nasha k’ishin ruwa nakeji..!”
Cikin sauri Fattu ta kawo min ruwa nasha..! Na lumshe idanuna ta taimaka min na kwanta bisa tabarmar sak’a dake gefe..
Fattu tayi jigum tana dubana cikeda tausayawa, lokaci guda ta kuma fad’in “Rankidad’e kodai Giro yayi tattaki ya tafi Masarauta ne ya sanar da Amale halinda kike ciki..?!”

Cikin sauri na d’ago sabida tsananin tsoron abinda ka iya zuwa yazo tinda Izzatu ta haneni nace da Fattu koda wasa, ko ita ko mijinta kar sukai wannan batu wa Amale..! Fattu dai ba dan taso ba sai dan babu yanda ta iya ta amince da batu na..!
Muna nan a haka wasu lokutan haka zanyita ganin abubuwa na ban tsoro suna kawo min ziyara, a haka cikina yaketa girma har zuwa ranan da zan haihu... Wani ikon Allah ranan haihuwata Fattu bata gidan, ko ita ko Giro Babu kowa amma saiga Izzatu tafe da zungureren ciki tareda wannan mutumi matsafin, Izzatu ita ta amshi hauhuwata dukda zungureren cikin dake jikinta... Inajin kukan jariri sanda ya fito daga jikina.. Amma daga haka ban kuma sanin mai ya faru ba ban kuma farkawa ba sai a gadon asibiti a nan cikin k’auyen dan dajin da gidan yake yana da d’an nisa da gari... Na tashi ina tambayar Ina jariri na Malam asibiti sukace haka aka kawo masu ni rai hannun Allah, Allah ne ma yayi taimako an iso dani asibiti da wuri da tuni jinin jikina ya k’are.. Fattu ta tusani gaba cikeda tausayawa tana tambayar Rankidad’e ina jaririn ya akayi hakan ta kasance mai ya faru..?!”

Kuka kurum nake ban Iya ceda Fattu komai ba dan na tuna duk abinda ya faru, na tuna cewa Izzatu Itace ta amshi haihuwata...! Fattu tace Giro zai tafi Masarauta yaje ya sanar da mai Martaba..! Kuka sosai na dingayi Ina rok’on Fattu idan tana ma Allah ko Giro kada ta sanar dashi wannan al’amari..! Na tambayi Fattu ya akayi Ta kawoni asibiti..? Fattu ta sanar dani tana can gona itada Giro ta dawo gida kai masa abinci nan Ta taddani a halinda nake ciki, tayi gaggawan fitowa gari ta sami masu amalanke suka taimaka suka kawoni asibiti...!”
Gimbiya Turai ta lumshe idanunta wasu hawayen suka kuma zubo mata...
Daidai da Jafar da Ubandoma suma hawayen ne suka zubo masu, harta Mama Tabawa itama hawayen take da jin irin wannan al’amari....
Chapter 115 · 0% Book details