Sashe 133
Muhibba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gimbiya Turai ta kamo hannunta guda tace “Nasan kinada tambayoyi da Dama k’unshe cikin zuciyarki Saudah, wanda da zaki so a amsa miki su cikin gaggawa, amma inaso ki k’ara hak’uri har abubuwa su kuma daidaita cikin Masarautar zakiji komai daki daki kinji koh..! Yanzu ki shiga cikin d’akinki ki samu kiyi wanka ki sauya wannan tufafi domin wad’annan tufafi basu kamaceki ba ked’in Gimbiya ce kuma Sarauniya..!” Ta k’arashe kyakkyawan murmushi saman fuskarta..
K’ok’aro murmushin Muhibbah ma tayi ba tareda Ta fahimci abinda take nufi da tace itad’in Gimbiya ce kuma Sarauniya, ta alak’anta maganar nata da kasancewarta d’iyaga d’anuwanta D’an Sarki jinin Sarauta..!
A haka suka k’arasa cikin sashen, yanda suka tadda Kuyangin fin na da, saidai wannan karon wasu ne ba wad’ancan Kuyangin data tadda sanda ta farka ta tsinci kanta cikin d’akin ba.. Gaba d’aya suka zube masu suna kwasan gaisuwa.. Hadimar guda tace da Gimbiya Muhibbah an shirya mata ruwan wanka da komai da komai.. Sannan ko akwai wani abu da Gimbiya Ke buk’ata..?
Umaima ce ta jinjina kai tace “Kuna iya tafiya, Gimbiya hutu take buk’ata..!!”
Hadimar ta kuma duk’awa tayi godiya kana suka sa kai suka fice..!
Muhibbah Ta d’an dubi Umaima ta rausayar da idanu tana mai furta “Nifah wllhi duk ban saba da wad’annan abubuwan ba, sai inajin gaba d’aya kaman wata duniya ta daban nake, nafi sabawa da yin komai ma kaina..!”
Murmushi Umaima tai tace “Da sannu zaki saba da d’abi’u da al’adun Gidan nan..! Muje na zab’a miki tufafin da zaki saka..!”
Ta janyo hannunta suka nufi closet tare..!
Gimbiya Turai ta raka su da kallo murmushi saman fuskarta, mik’ewa tayi itama ta nufi closet d’in tana tayasu zab’an tufafin... Dashike almuru ya riga ya sako kai, dare ya riga ya soma shigowa hakan ya sanyasu zab’a mata tufafi mai sauk’i sanyawa irinta masu mulki da sarauta..!
**
A can b’angaren su Mahmood kuwa ko takan Giwa da ayarinta bai kuma biba tinda ya tabbata an fice dasu daga cikin Masarautar an tafi dasu asibiti domin nema masu taimako Ta gaggawa, iyaka taimakon da zai iya masu kenan dama a fice dasu daga Masarautar a nema masu agajin halin da suke ciki dukda cewa sune silan jefa mawunansu cikin wannan yanayi da suka tsinci kawunansu ciki...!
A parlor ya tadda Ja’afar da Turaki suna jiran sauk’owarsa bayan komai ya d’an lafa, Turaki ya mik’e yana fad’ida Ja’afar “Kaga ga Rankaidad’e d’in ya fito... Ni zanje na baiwa Ansar masauk’i dan yace min idan yaji k’arfin jikinsa gobe yake komawa Bauchi..!”
Ja’afar yace “Bazai bari ya kwana biyu ba.. Kuma ai akwai masauk’i cikin Masarautar nan, inaga basai ya fice..!”
Muryar Mahmood suka sinkaya yana fad’in “Mutumin nan baida masauk’i cikin Masarautar nan..!!”
Ja’afar ya had’iyi sauran kalamansa, Turaki ya jinjina kai yace “Dama can gidana zamu tafi your Highness..! Allah ya huci zuciyar Sarki mai jiran nad’i, Baban Zahra’u, kuma Angon Gimbiya Saudah Muhibbah..!!” Ya k’arashe yana mai d’ago masa hannu alamun jinjina..
Yasan ‘yan tsiyar Turaki ne suka motsa hakan yasa sam baibi takan Turaki ba saima zama da yayi saman kujera ya d’aura k’afarsa d’aya bisa d’aya yana murza zobban hannunsa a hankali..!
Turaki ya risina yace “Rankaidad’e ni zan wuce, Masarauta is all settle now..!”
Ya d’ago idanu guda yana duban Turaki ya dubi Ja’afar dake gefe... D’an gyaran murya yayi ya ambato sunan Ja’afar..!
J’afar ya amsa cikeda risinawa irin yanda k’aramin k’ani keyiwa babban wa..
Tambayarsa yayi Mahaifiyarsu..
Ja’afar yace “Tana can tareda..!” Yayi shiru ya kasa k’arasa sunan Muhibbah..!
Mahmood ya tsaresa da idanu.. K’ok’arin saita kansa Ja’afar yayi yace “Tana can tareda Gimbiya Muhibbah, Tana sashenta..!”
Ya jinina kai a hankali sai kuma ya mik’e yana mai furta “Ka jirani a nan ina dawowa..!” Ja’afar ya jinjina kai a hankali yana mai amsa masa, duban Turaki Mahmood d’in yayi lokaci guda ya soma takawa, Turaki na biye dashi yasan hakan na nufin rakiya zai masa..!
Suna tafe yana furta “Kasan irin kalaman da zaka Ke furtawa gaban k’anina..!!”
Turaki ya had’iyi dariyarsa yace “Tuba nake Rankaidad’e... Yanzu shi Ansar d’in Dawakai nawa za’a basa kyautarsu..!” Had’iye maganar nasa yayi ganin ya kaikaito a hankali yana dubansa..!
“Turaki..!!”
Turaki ya amsa da “Rankaidad’e.!!”
Mahmood yaci gaba da fad’in “Kar ka sake ambaton sunan mutumin nan a nan, nasan mai ya kawo shi ba komai bane ya kawoshi illa tsananin soyayyar da yake mata..!”
Turaki ya jinjina kai yace “Toh amma Rankaidad’e gani nayi baka gabatar da kanka gareta ba tukuna.. Bamuda tabbacin If she feels the same for you, a tunanina sabida binciken gaskiya da kake cikin Masarauta shiyasa ka aurota gudun kar Waliyyinta ya bada aurenta ga wani wanda hakan ka iya hana kasancewarta cikin Masarauta... Tunda yanzu komai ya fito fili inaga ya kamata ka sauwak’e mata tun kafin ka kaiga sanar da ita matsayinka a wajenta..!”
Burki yayi had’ida k’urama Turaki idanu ganin cewa da gaske yake fad’in duk abubuwan da yake fad’i, lallai ya yarda notin kan Turaki sun kwance...!
Saida yayi gyaran murya hannayensa hard’e Ta baya ya soma furta “Idan na sauwak’a mata sai shi kuma ya aureta ko yaya..?! Kai ka tab’a jin Sarki mace talakansa ya aura..?!” Ya k’arashe yana duban Turakin k’asa k’asa
Turaki ya jinjina kai yace “Toh idan kuwa haka ne, ya zama dole Sarki ya Sauk’e kansa ya sanar da ita how he feels..!”
Ya katse Turaki da fad’in “What if zuciyarta na k’aunar Likitan nan ne..?!!”
Turaki ya jinina kai yace “Then sai ka sawwak’e mata, Ta cancanci Farin ciki, Dan bazai yuwu kaita ajiyeta a d’aki ba tareda sanin madafar rayuwarta ba..!”
Muguwar kallo ya kuma aikawa Turaki ba tareda yace komai ba..! Lokaci guda yake furta “Have I ever told you neman shawarinka is useless sometimes...!!”
Turaki ya jinjina kai yace “Kasha fad’in haka Rankaidad’e, Allah ya huci ran Amale tuba nake..! Na barka lafiya Rankaidad’e...!” Ya k’arashe murmushi saman fuskarsa yana mai bud’e motarsa, yasan cewa k’arshe za’a nemosa ne...!
Da kallo kurum ya raka Turaki har ya shige yana tsaye a wajen hannayensa hard’e Ta baya... Duk duniyar nan Turaki ne kawai mai yab’a masa magana yanda yaga Dama.! Ya kuma fuzar da wani hucin yana tunanin al’amarin... Ta yaya zai fara tunk’ararta da batun, Ta yaya zai soma sanar da ita cewa shid’in mijinta ita matarsa ce..! Mai zai faru idan tak’i amincewa da hakan..!?
Girmansa fah ya fad’i kenan musamman yanzu da yasan cewa su d’in ‘yanuwan juna ne matsayin k’anwa take masa..! Ya fuzar da fuci mai d’umin gaske yana mai shafe fuskarsa da duka hannayensa biyu..!
Kai tsaye sashensa ya koma yanda ya baro Ja’afar na jiransa..!
Daga bakin k’ofa ya tsaya yana duban yanda Ja’afar Ke shafa wani k’atoton hoton Mahmood da ‘yanuwansa su Duka hud’un sunyi shiga irinta Mulki saman Dawakai akai masu hoton, sunyi bala’in yin kyau kana ganinsu kaga ‘ya’yan Sarauta..!
Ja’afar yasa hannunsa yana share hawayen dake gangaro masa yake kuma shafan hoton, a hankali Mahmood ya k’araso ya tsaya bayansa hannayensa hard’e yake duban hoton shima, lokaci guda yake furta “Kai yafi cancanta ka kasance cikin hoton nan, amma bata baka daman hakan ba, she deprived you your right, komai a nan da kake gani naka ne..! Everything is yours, sarautar da komai Naka ne ba nasu bane..! Duk abinda Ke cikin hoton nan ba komai bane face k’arya..!!”
Ja’afar ya kaikaito yana dubansa, lokaci guda yasa hannunsa yana kuma goge hawayensa, a hankali yake furta “Akwai abu guda d’aya da yake ba k’Arya ba cikin hoton Yaya..! And that’s you..! Koda ace ban mallaki damata cikin Masarautar nan ba, ina Farin cikinka girma cikin gata da k’aunar mahaifinmu Yaya..! At least akwai abu guda da yake gaskiya ne a cikin Masarautar... And that’s you Yaya..! Wannan kawai idan na tuna nakanji Farin ciki..!!” Ya k’arashe cikin tsananin rawar murya irinta mai kuka..!
A hankali Mahmood ya janyo kafad’arsa ya rungume a gefen damansa, lokaci guda yake d’an bubbuga kafad’arsa yana lallashinsa irin yanda yakeyiwa Fu’ad..! A hankali Mahmood d’in yakai dubansa kan Fu’ad a cikin picture d’in... Ya saki murmushi mai sanyin gaske... Saida ya d’anyi gyaran murya kana yace “Gobe in sha Allah ka shirya zamuje wani waje..!”
Ja’afar ya jinjina masa kai a hankali yace “Toh Yaya..!”
Mahmood ya jinina kai kana sukai sallama da d’anuwan nasa ya haye samansa..!
Yana isa d’aki ya kunna computer d’insa dake hasko masa d’akinta tareda nad’o masa sautin abindake wakana...Zaune ya gansu itada Umaima da kuma mahaifiyarsa sun saka a tsakiya...
Ya zauna saman kujera yana mai bada hankalinsa sosai garesu..
**
Muhibbah ta d’ago tana dubansu su duka biyun, saida tasa bayan hannunta ta goge hawayen da suka zubo mata kana ta soma fad’in
“Kaman yanda kuka sani Sunana Saudatu, na taso ni kad’ai wajen mahaifana, mahaifi na da Mahaifiyata ‘yanuwan juna ne sabida kaman yanda suka bani labari cewa bayan mahaifina ya rasa iyayensa sai mahaifin Mahaifiyata ya d’aukesa suka baro can garin nasu domin su tsiratar da mahaifina daga wad’anda suke nemansa da sharri..!”
Ta d’anyi fasali kana yaci gaba da fad’in “Nasha yiwa iyayen tambayoyi da Dama wanda basu bani amsarsu ba sai yanzu nake ganin amsoshin tambayata garesu, daga ciki harda tambayar da nayi masu ina ne asalin garinmu, ina sauran danginsu..? Mahaifina saidai yace min kar na sake tambaya makamancin wannan..! Duk wani abinda zai tuno masa bayansa baya k’auna, sannan na kasance ina son labarun tarihi irinta gidajen Mulki da sarauta amma sam mahaifina baya k’auna, duk abinda ya shafi sarauta mahaifina baya k’aunar wannan abin...! Mun kasance muna tafiye tafiye daga gari zuwa gari tun bayan da muka rasa mahaifin Mahaifiyata wanda shine d’an uwan mahaifina da ya rainesa ya girma gabansa ya kuma ya aura masa d’iyarsa wacce ta zamto amana a garesa Wato Mahaifiyata kenan, bani mancewa mun zauna a wani gari mai suna Katakore a can k’asashen yamma... A wannan garin ne har aka sanyani makarantar boko da na Islama, mun d’anyi dogon zango a wannan garin kafin daga bisani muka soma shirye shiryen dawowa k’asashen Arewa....!” Ta d’anyi birki kana ta d’ago tana duban Gimbiya Turai tace “Bansan ko Zaki iya sanin Kakan nawa ba dan shi d’in d’anuwana ga mahaifina..!”
K’ok’aro murmushin Muhibbah ma tayi ba tareda Ta fahimci abinda take nufi da tace itad’in Gimbiya ce kuma Sarauniya, ta alak’anta maganar nata da kasancewarta d’iyaga d’anuwanta D’an Sarki jinin Sarauta..!
A haka suka k’arasa cikin sashen, yanda suka tadda Kuyangin fin na da, saidai wannan karon wasu ne ba wad’ancan Kuyangin data tadda sanda ta farka ta tsinci kanta cikin d’akin ba.. Gaba d’aya suka zube masu suna kwasan gaisuwa.. Hadimar guda tace da Gimbiya Muhibbah an shirya mata ruwan wanka da komai da komai.. Sannan ko akwai wani abu da Gimbiya Ke buk’ata..?
Umaima ce ta jinjina kai tace “Kuna iya tafiya, Gimbiya hutu take buk’ata..!!”
Hadimar ta kuma duk’awa tayi godiya kana suka sa kai suka fice..!
Muhibbah Ta d’an dubi Umaima ta rausayar da idanu tana mai furta “Nifah wllhi duk ban saba da wad’annan abubuwan ba, sai inajin gaba d’aya kaman wata duniya ta daban nake, nafi sabawa da yin komai ma kaina..!”
Murmushi Umaima tai tace “Da sannu zaki saba da d’abi’u da al’adun Gidan nan..! Muje na zab’a miki tufafin da zaki saka..!”
Ta janyo hannunta suka nufi closet tare..!
Gimbiya Turai ta raka su da kallo murmushi saman fuskarta, mik’ewa tayi itama ta nufi closet d’in tana tayasu zab’an tufafin... Dashike almuru ya riga ya sako kai, dare ya riga ya soma shigowa hakan ya sanyasu zab’a mata tufafi mai sauk’i sanyawa irinta masu mulki da sarauta..!
**
A can b’angaren su Mahmood kuwa ko takan Giwa da ayarinta bai kuma biba tinda ya tabbata an fice dasu daga cikin Masarautar an tafi dasu asibiti domin nema masu taimako Ta gaggawa, iyaka taimakon da zai iya masu kenan dama a fice dasu daga Masarautar a nema masu agajin halin da suke ciki dukda cewa sune silan jefa mawunansu cikin wannan yanayi da suka tsinci kawunansu ciki...!
A parlor ya tadda Ja’afar da Turaki suna jiran sauk’owarsa bayan komai ya d’an lafa, Turaki ya mik’e yana fad’ida Ja’afar “Kaga ga Rankaidad’e d’in ya fito... Ni zanje na baiwa Ansar masauk’i dan yace min idan yaji k’arfin jikinsa gobe yake komawa Bauchi..!”
Ja’afar yace “Bazai bari ya kwana biyu ba.. Kuma ai akwai masauk’i cikin Masarautar nan, inaga basai ya fice..!”
Muryar Mahmood suka sinkaya yana fad’in “Mutumin nan baida masauk’i cikin Masarautar nan..!!”
Ja’afar ya had’iyi sauran kalamansa, Turaki ya jinjina kai yace “Dama can gidana zamu tafi your Highness..! Allah ya huci zuciyar Sarki mai jiran nad’i, Baban Zahra’u, kuma Angon Gimbiya Saudah Muhibbah..!!” Ya k’arashe yana mai d’ago masa hannu alamun jinjina..
Yasan ‘yan tsiyar Turaki ne suka motsa hakan yasa sam baibi takan Turaki ba saima zama da yayi saman kujera ya d’aura k’afarsa d’aya bisa d’aya yana murza zobban hannunsa a hankali..!
Turaki ya risina yace “Rankaidad’e ni zan wuce, Masarauta is all settle now..!”
Ya d’ago idanu guda yana duban Turaki ya dubi Ja’afar dake gefe... D’an gyaran murya yayi ya ambato sunan Ja’afar..!
J’afar ya amsa cikeda risinawa irin yanda k’aramin k’ani keyiwa babban wa..
Tambayarsa yayi Mahaifiyarsu..
Ja’afar yace “Tana can tareda..!” Yayi shiru ya kasa k’arasa sunan Muhibbah..!
Mahmood ya tsaresa da idanu.. K’ok’arin saita kansa Ja’afar yayi yace “Tana can tareda Gimbiya Muhibbah, Tana sashenta..!”
Ya jinina kai a hankali sai kuma ya mik’e yana mai furta “Ka jirani a nan ina dawowa..!” Ja’afar ya jinjina kai a hankali yana mai amsa masa, duban Turaki Mahmood d’in yayi lokaci guda ya soma takawa, Turaki na biye dashi yasan hakan na nufin rakiya zai masa..!
Suna tafe yana furta “Kasan irin kalaman da zaka Ke furtawa gaban k’anina..!!”
Turaki ya had’iyi dariyarsa yace “Tuba nake Rankaidad’e... Yanzu shi Ansar d’in Dawakai nawa za’a basa kyautarsu..!” Had’iye maganar nasa yayi ganin ya kaikaito a hankali yana dubansa..!
“Turaki..!!”
Turaki ya amsa da “Rankaidad’e.!!”
Mahmood yaci gaba da fad’in “Kar ka sake ambaton sunan mutumin nan a nan, nasan mai ya kawo shi ba komai bane ya kawoshi illa tsananin soyayyar da yake mata..!”
Turaki ya jinjina kai yace “Toh amma Rankaidad’e gani nayi baka gabatar da kanka gareta ba tukuna.. Bamuda tabbacin If she feels the same for you, a tunanina sabida binciken gaskiya da kake cikin Masarauta shiyasa ka aurota gudun kar Waliyyinta ya bada aurenta ga wani wanda hakan ka iya hana kasancewarta cikin Masarauta... Tunda yanzu komai ya fito fili inaga ya kamata ka sauwak’e mata tun kafin ka kaiga sanar da ita matsayinka a wajenta..!”
Burki yayi had’ida k’urama Turaki idanu ganin cewa da gaske yake fad’in duk abubuwan da yake fad’i, lallai ya yarda notin kan Turaki sun kwance...!
Saida yayi gyaran murya hannayensa hard’e Ta baya ya soma furta “Idan na sauwak’a mata sai shi kuma ya aureta ko yaya..?! Kai ka tab’a jin Sarki mace talakansa ya aura..?!” Ya k’arashe yana duban Turakin k’asa k’asa
Turaki ya jinjina kai yace “Toh idan kuwa haka ne, ya zama dole Sarki ya Sauk’e kansa ya sanar da ita how he feels..!”
Ya katse Turaki da fad’in “What if zuciyarta na k’aunar Likitan nan ne..?!!”
Turaki ya jinina kai yace “Then sai ka sawwak’e mata, Ta cancanci Farin ciki, Dan bazai yuwu kaita ajiyeta a d’aki ba tareda sanin madafar rayuwarta ba..!”
Muguwar kallo ya kuma aikawa Turaki ba tareda yace komai ba..! Lokaci guda yake furta “Have I ever told you neman shawarinka is useless sometimes...!!”
Turaki ya jinjina kai yace “Kasha fad’in haka Rankaidad’e, Allah ya huci ran Amale tuba nake..! Na barka lafiya Rankaidad’e...!” Ya k’arashe murmushi saman fuskarsa yana mai bud’e motarsa, yasan cewa k’arshe za’a nemosa ne...!
Da kallo kurum ya raka Turaki har ya shige yana tsaye a wajen hannayensa hard’e Ta baya... Duk duniyar nan Turaki ne kawai mai yab’a masa magana yanda yaga Dama.! Ya kuma fuzar da wani hucin yana tunanin al’amarin... Ta yaya zai fara tunk’ararta da batun, Ta yaya zai soma sanar da ita cewa shid’in mijinta ita matarsa ce..! Mai zai faru idan tak’i amincewa da hakan..!?
Girmansa fah ya fad’i kenan musamman yanzu da yasan cewa su d’in ‘yanuwan juna ne matsayin k’anwa take masa..! Ya fuzar da fuci mai d’umin gaske yana mai shafe fuskarsa da duka hannayensa biyu..!
Kai tsaye sashensa ya koma yanda ya baro Ja’afar na jiransa..!
Daga bakin k’ofa ya tsaya yana duban yanda Ja’afar Ke shafa wani k’atoton hoton Mahmood da ‘yanuwansa su Duka hud’un sunyi shiga irinta Mulki saman Dawakai akai masu hoton, sunyi bala’in yin kyau kana ganinsu kaga ‘ya’yan Sarauta..!
Ja’afar yasa hannunsa yana share hawayen dake gangaro masa yake kuma shafan hoton, a hankali Mahmood ya k’araso ya tsaya bayansa hannayensa hard’e yake duban hoton shima, lokaci guda yake furta “Kai yafi cancanta ka kasance cikin hoton nan, amma bata baka daman hakan ba, she deprived you your right, komai a nan da kake gani naka ne..! Everything is yours, sarautar da komai Naka ne ba nasu bane..! Duk abinda Ke cikin hoton nan ba komai bane face k’arya..!!”
Ja’afar ya kaikaito yana dubansa, lokaci guda yasa hannunsa yana kuma goge hawayensa, a hankali yake furta “Akwai abu guda d’aya da yake ba k’Arya ba cikin hoton Yaya..! And that’s you..! Koda ace ban mallaki damata cikin Masarautar nan ba, ina Farin cikinka girma cikin gata da k’aunar mahaifinmu Yaya..! At least akwai abu guda da yake gaskiya ne a cikin Masarautar... And that’s you Yaya..! Wannan kawai idan na tuna nakanji Farin ciki..!!” Ya k’arashe cikin tsananin rawar murya irinta mai kuka..!
A hankali Mahmood ya janyo kafad’arsa ya rungume a gefen damansa, lokaci guda yake d’an bubbuga kafad’arsa yana lallashinsa irin yanda yakeyiwa Fu’ad..! A hankali Mahmood d’in yakai dubansa kan Fu’ad a cikin picture d’in... Ya saki murmushi mai sanyin gaske... Saida ya d’anyi gyaran murya kana yace “Gobe in sha Allah ka shirya zamuje wani waje..!”
Ja’afar ya jinjina masa kai a hankali yace “Toh Yaya..!”
Mahmood ya jinina kai kana sukai sallama da d’anuwan nasa ya haye samansa..!
Yana isa d’aki ya kunna computer d’insa dake hasko masa d’akinta tareda nad’o masa sautin abindake wakana...Zaune ya gansu itada Umaima da kuma mahaifiyarsa sun saka a tsakiya...
Ya zauna saman kujera yana mai bada hankalinsa sosai garesu..
**
Muhibbah ta d’ago tana dubansu su duka biyun, saida tasa bayan hannunta ta goge hawayen da suka zubo mata kana ta soma fad’in
“Kaman yanda kuka sani Sunana Saudatu, na taso ni kad’ai wajen mahaifana, mahaifi na da Mahaifiyata ‘yanuwan juna ne sabida kaman yanda suka bani labari cewa bayan mahaifina ya rasa iyayensa sai mahaifin Mahaifiyata ya d’aukesa suka baro can garin nasu domin su tsiratar da mahaifina daga wad’anda suke nemansa da sharri..!”
Ta d’anyi fasali kana yaci gaba da fad’in “Nasha yiwa iyayen tambayoyi da Dama wanda basu bani amsarsu ba sai yanzu nake ganin amsoshin tambayata garesu, daga ciki harda tambayar da nayi masu ina ne asalin garinmu, ina sauran danginsu..? Mahaifina saidai yace min kar na sake tambaya makamancin wannan..! Duk wani abinda zai tuno masa bayansa baya k’auna, sannan na kasance ina son labarun tarihi irinta gidajen Mulki da sarauta amma sam mahaifina baya k’auna, duk abinda ya shafi sarauta mahaifina baya k’aunar wannan abin...! Mun kasance muna tafiye tafiye daga gari zuwa gari tun bayan da muka rasa mahaifin Mahaifiyata wanda shine d’an uwan mahaifina da ya rainesa ya girma gabansa ya kuma ya aura masa d’iyarsa wacce ta zamto amana a garesa Wato Mahaifiyata kenan, bani mancewa mun zauna a wani gari mai suna Katakore a can k’asashen yamma... A wannan garin ne har aka sanyani makarantar boko da na Islama, mun d’anyi dogon zango a wannan garin kafin daga bisani muka soma shirye shiryen dawowa k’asashen Arewa....!” Ta d’anyi birki kana ta d’ago tana duban Gimbiya Turai tace “Bansan ko Zaki iya sanin Kakan nawa ba dan shi d’in d’anuwana ga mahaifina..!”