Sashe 91
Lullubin Biri Book Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ya kashe wayar ya saka a aljihu tare da miƙewa ya fita daga office ɗin ba tare da yace da Dr Yusuf komai ba.
Fitar tasa babu jimawa Dr Yusuf ma ya biyo bayansa. inda ya same shi tsaye a bakin ƙofar room ɗin da Fillo ke ciki yana leƙenta ta cikin wani glass.
daidai da ƙarasowar Daddy da Ammi wajen, Yusuf ya isa wajensu yana kallon Aliyu da ce masa,"Malami ka kwantar da hankalinka, kayi adu'a kawai Allah yasa ta farka". Aliyu ya sauke numfashi yana komawa da baya ya zauna kan kujera.
Yusuf yace da su Daddy,"na fito ai tun É—azu ban ganku ba".
Ammi tace,"gida muka koma, da dukkan alama mutanen acikin tashin hankali suke, dan sai bayan zuwanmu da muka shigo cikin haske naga alamar hakan a tare da mahaifiyar yarinyar, ashe ko ɗankwali ma babu a jikinta, haka ma sarƙa ce ɗaure da hannunta. shine naga babu dacewar mu tsaya da ita a haka tunda mutane kowa na wucewa, dalilin da yasa muka koma gida kenan".
Yusuf yace,"Ammi wannan matar fa ba mahaifiyar yarinyar bace, ni har na fara ɗaukar maganar Inna Wuro fa, saboda ita wannan yarinyar ta taɓa kwanciya a asibitin nan, tana da matsalar aljanu da suke yawan ɗaukarta su kaita wani wajen, shi yasa nafi tunanin nima ko aljanar tata ce ta fito a siffar mutane".
Daddy yace,"a'a wannan matar mutum ce, kun riga kun san baiwar da Allah yay min, da naga aljani na san shine. ta bakin nata dai tace wasu mutanene suka sace su shine suka samu suka gudu".
Yusuf ya sauke nunfashi yace,"ofcourse an kidnapping yarinyar in ban manta ba 1month kenan".
Ammi ta nemi wuri kusa da Aliyu ta zauna, bayan ta dube shi da tausayawa ta kalli Yusuf tace,"ya jikin yarinyar?". yace"da sauƙi, nan da mintuna kaɗan ma zata farka".
Daddy yace,"mun biya ta station sun kwance sarƙar hannun matar, da ƙyar suka yarda da mu akan hakan dan tunanin su ma wai ko me laifi ce ta gudu, to amma duk da haka sun haɗo mu da police ɗaya sannan sun shigar da report wai should incase. yanzu please kasa nurse ko kuma kai da kanka kayi ƙoƙarin mata treating hannunta, tsintsiyar hannun duk ya farfashe yay caɓa-caɓa da jini wallahi, abin tausayi".
ya juya yana kallon Ammi yace,"tana ina?".
tace,"gata can wajen corrido ɗin can tana sallah, naga hankalinta duk yaƙi kwanciya, ni tausayi ma ta-ke ban wallahi".
Dr Yusuf ya kira wata nurse, yayi mata nuni da inda Mum ke zauna yace ta ɗau kayan aiki taje wajenta. ba ɓata lokaci Nurse ɗin kuwa tai treatment duk inda wani ciwo yake ajikin Mum, dauriya irin ta babba shi kaɗai ya hanata yin kuka, dan sosai take jin zafi da raɗaɗi, har aka gama ƙwayar idonta na kallon gefe ɗaya, sai bayan an gama tukunna ta ɗago tana kallon duka hannayen da aka ɗaure wajen bandage kaɗan ba mai yawa ba.
a lokacin Turaki ya bar jikin ƙofar ya shiga kaiwa da komowa a wajen hannayensa sarƙe a bayansa, idonsa ya kai bayan Mum da har yanzu ke zaune bata tashi daga wurin da tayi sallah ba, adu'a kawai take akan Allah ya tashi kafaɗun Fillo, har ga Allah tana so ta nemi ahalinta a wannan lokacin to amma ba zata iya ba har sai Fillo ta farka, yarinyar ta taimaka mata a lokacin da take neman taimako.
duk da bayanta yake kallo haka yayi tsaye sai kallonta yake ya kasa ko da motsi, ya kuma kasa ɗauke idonsa akanta, yana jin wani irin abu na shigarsa, yana jin kamar yana so yaga ko wace, gaba ɗaya bai san dai taƙamemen abinda yake ji a tare da shi ba.
yay ajiyar zuciya ya juya ya koma bakin ƙofar, yaci gaba da kallon Fillo yana ta adu'a cikin ransa, bini-bini sai ya kalli agogo ya duba time, cikar lokacin da likita ya ɗiba kawai yake jira, da dukkan fatansa na in lokaci ya cika ta farka lafiya lau. sai dai haka ɗaya kuma yaji totally ya kasa samun nutsuwa, zuciyarsa na masa wani irin zillo, tunaninsa da hankalinsa ya rabu waje biyu, so yake yaci gaba da tsayuwa anan har sanda Fillo zata farka, haka kuma so yake ya bar wajen yaje wajen waccan matar da bai san wacece ba.
ba tare da sani ba ya bar wajen ya nufa wurin da Mum ke zaune har yanzu, ya tsuguna ta gefenta daga ɗan bayanta, ba tare da sanin taƙaimemen abinda zai yi ba, idan ma magana zai mata shi bai san me zaice mata ba, zuciyarsa ce kawai ta kawo shi.
ya buɗe bakinsa zai furta abinda bai san zai ce ba sai ga Ammi ta ƙaraso wajen, bai iya ce mata komai ba ya bita da kallo har ta zagaya ta gaban Mum ta tsuguna agabanta.
Ammi tace,"kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki Hajiya, Ɗana ya tabbatar min da cewar ƴarki zata farka cikin amincewar ubangiji, kuma zata farka lafiya lau insha'Allah".
a sannan Mum ta É—ago da kanta tace,"Allah ya amsa, amma Hajiya lokaci yaja da yawa, har yanzu fa shiru".
tai maganar muryarta É—auke da sautin damuwa.
Ammi ta ƙara cewa,"adu'a zamu ci gaba da yi". Mum bata iya magana ba illa gyaɗa kanta kawai da tayi. bata san me take ji a tare da ita ba, amma dai tana jin zuciyarta na ƙara matsuwa da zullumin son kasancewa acikin ahalinta, ba abinda idanuwanta ke da muradi yanzu sama da su ga Babanta, taga ƴaƴanta tukunna ta sami kwanciyar hankali.
Umma ta ƙaraso wajen, Ammi ta ɗauke kanta daga kallonta, Umma bata kula hakan ba tace,"Ammin Yara wannan itace mahaifiyar yarinyar da Aliyu ya buge ɗin?". Ammi ta kauda fuska gefe tace,"umm ita ce". ta faɗa tana miƙewa ta bar wajen, Umma ta zagaya ta ɗaya ɓarin ta zauna kusa da Mum, suka gaisa tana yi mata adua da sanar mata cewar itama mahaifiya ce wurin yaron da ya bigesu ɗin.
Mum tace,"Allah sarki, mun gode sosai. kun tsaya mana baku bari mun wahala ba".
Umma tace,"to ai hakan ya zama dole akan wanda yasan hakkin bawa".
ta faɗa idonta na kan Turaki da har sannan yake tsugune daga can gefe, kamar wani mutum mutumi sai bin kowa yake da ido, shi abinda ya ɗaure masa kai tun zuwan Ammi wajen yaji tana batun mahaifiyar Fillo, shi yasa yaji kamar ƙafafunsa ma ba zasu iya ɗagawa ba dan haka kawai yaji jikinsa duk yay sanyi, kuma Allah Allah yake yaga fuskar matar.
ganin tsananin kamar dake tsakanin Turaki da Mum wanda Ammi bata lura da hakan ba yasa Umma ce masa,"sannu fa, ya mai jiki?".
Turaki yaji kamar ba da shi take ba, lura da hakan yasa Umma cewa,"da kai nake". ta faÉ—a tana murmushi.
yana sauke idonsa a ƙasa yace,"Alhamdulillah".
tace,"to Allah ya bada lafiya, dan Allah ina daɗa bayar da haƙuri a madadin yarona".
shi dai bai iya cewa komai ba, ya zama kamar wani soko ko me neman gafara. kuma Umman na yin shiru ta hango Nuratu da Mommi na nufo su, har da Inna Wuro dake goye da Farha.
itace a gaba ta taho tana cewa da Umma,"Falmata ni dai Amadu ya rantse yace min ba aljanu ba ne mutanene shisa ma na iya shigowa asibitin nan amma da a waje zan tsaya gaskiya, dan ban iya saka kaina a masifa, Aliyun ma ni da wurin ƴan sanda aka kaishi tunda ance har yanzu yarinyar bata farka ba, ko kawai ayi kotu da ɗan banza kowa kuma sai yay ta kansa kar aja kuɗin Amadu ya ƙare".
Umma ta miƙe tana cewa,"sannu da zuwa Inna".
tana rufe baki Nuratu da Mommi suka iso wajen, dai-dai kuma da miƙewar Turaki. yana tashi idonsa ya kai kan Mommi, ta ke idanuwansa suka firfito waje yana binta da kallo me ban mamaki da al'ajabi, me yake gani?, dama da gaske akwai fuska biyu a duniya?, wannan matar ai photocopy ɗin Fillo ce.
Mommi da ta iso gabansa ta ɗaga masa hannu alamar sannu. mamaki na bala'i ya ƙara kama shi, bai san lokacin da ya kamo hannunta ba ya jata zuwa room ɗin da Fillo ke ciki.
ganin hakan yasa kowa miƙewa yabi bayansu da kallo harta kuwa da Mum da taji su Umma na cewa,"ikon Allah wannan yaron na da lafiya kuwa". Nuratu tace,"ah wannan sai dai mahaukaci". ta faɗa tana bin bayansu da sauri.
Inna Wuro tace,"ah tou haka duk zaku yi ta gamuwa da gamonku, ance aljanu ku ka kwaso kun dage mutanene, ni dai da naga ba zan iya ba ai ta kaina zanyi, wa zai zo ya wahala, haka kawai a shanyen ƙafa ko wuya banji ba ban gani ba".
Umma ta dafa kafaɗar Mum dake bin bayan Nuratu da kallo tana jin shigar wani al'amari me girma a tare da ita. a hankali Umma tace,"am sorry to say, amma ɗanki bai da lafiyar ƙwaƙwalwa ko?". Mum ta juyo da kallonta gareta tace,"ɗana kuma?". ta tambaya da mamaki.
Umma tace,"ehh fa, wanda ke zaune anan kusa da ke". kan Mum ya ƙara ƙullewa tace,"me kike son cewa ne?". ta tambaya tana jin ƙirjinta na bugawa.
jin ƙarar saukar mari ya tattara hankalinsu kan su Turaki gaba ɗaya, Nuratu ce a gabansa tana huci tana faɗin,"baka da hankali ne?, ya daga ganin mahaifiyata zaka kama hannunta, ko an faɗa maka mu kafirai ne kamarka?, shashashan banza da wofi, to wallahi in baka bar asibitin nan cikin gaggawa ba sai nasa ƴan sanda sun zo sun tafi da kai yanzu".
Turaki ya ɗago da fuskarsa yana dafe da kuncinsa, hoton fuskar tasa ya shiga cikin ƙwayar idon Hajiya Ramla da suka ƙaraso wajen da sassarfa. cikin zafin nama Turaki ya ɗaga hannu zai saukewa Nuratu zazzafan mari Hajiya Ramla ta zaro ido waje tana faɗin,"Babana". ta faɗa da ƙarfin sautin da yay amsa kuwa a wajen.
Fitar tasa babu jimawa Dr Yusuf ma ya biyo bayansa. inda ya same shi tsaye a bakin ƙofar room ɗin da Fillo ke ciki yana leƙenta ta cikin wani glass.
daidai da ƙarasowar Daddy da Ammi wajen, Yusuf ya isa wajensu yana kallon Aliyu da ce masa,"Malami ka kwantar da hankalinka, kayi adu'a kawai Allah yasa ta farka". Aliyu ya sauke numfashi yana komawa da baya ya zauna kan kujera.
Yusuf yace da su Daddy,"na fito ai tun É—azu ban ganku ba".
Ammi tace,"gida muka koma, da dukkan alama mutanen acikin tashin hankali suke, dan sai bayan zuwanmu da muka shigo cikin haske naga alamar hakan a tare da mahaifiyar yarinyar, ashe ko ɗankwali ma babu a jikinta, haka ma sarƙa ce ɗaure da hannunta. shine naga babu dacewar mu tsaya da ita a haka tunda mutane kowa na wucewa, dalilin da yasa muka koma gida kenan".
Yusuf yace,"Ammi wannan matar fa ba mahaifiyar yarinyar bace, ni har na fara ɗaukar maganar Inna Wuro fa, saboda ita wannan yarinyar ta taɓa kwanciya a asibitin nan, tana da matsalar aljanu da suke yawan ɗaukarta su kaita wani wajen, shi yasa nafi tunanin nima ko aljanar tata ce ta fito a siffar mutane".
Daddy yace,"a'a wannan matar mutum ce, kun riga kun san baiwar da Allah yay min, da naga aljani na san shine. ta bakin nata dai tace wasu mutanene suka sace su shine suka samu suka gudu".
Yusuf ya sauke nunfashi yace,"ofcourse an kidnapping yarinyar in ban manta ba 1month kenan".
Ammi ta nemi wuri kusa da Aliyu ta zauna, bayan ta dube shi da tausayawa ta kalli Yusuf tace,"ya jikin yarinyar?". yace"da sauƙi, nan da mintuna kaɗan ma zata farka".
Daddy yace,"mun biya ta station sun kwance sarƙar hannun matar, da ƙyar suka yarda da mu akan hakan dan tunanin su ma wai ko me laifi ce ta gudu, to amma duk da haka sun haɗo mu da police ɗaya sannan sun shigar da report wai should incase. yanzu please kasa nurse ko kuma kai da kanka kayi ƙoƙarin mata treating hannunta, tsintsiyar hannun duk ya farfashe yay caɓa-caɓa da jini wallahi, abin tausayi".
ya juya yana kallon Ammi yace,"tana ina?".
tace,"gata can wajen corrido ɗin can tana sallah, naga hankalinta duk yaƙi kwanciya, ni tausayi ma ta-ke ban wallahi".
Dr Yusuf ya kira wata nurse, yayi mata nuni da inda Mum ke zauna yace ta ɗau kayan aiki taje wajenta. ba ɓata lokaci Nurse ɗin kuwa tai treatment duk inda wani ciwo yake ajikin Mum, dauriya irin ta babba shi kaɗai ya hanata yin kuka, dan sosai take jin zafi da raɗaɗi, har aka gama ƙwayar idonta na kallon gefe ɗaya, sai bayan an gama tukunna ta ɗago tana kallon duka hannayen da aka ɗaure wajen bandage kaɗan ba mai yawa ba.
a lokacin Turaki ya bar jikin ƙofar ya shiga kaiwa da komowa a wajen hannayensa sarƙe a bayansa, idonsa ya kai bayan Mum da har yanzu ke zaune bata tashi daga wurin da tayi sallah ba, adu'a kawai take akan Allah ya tashi kafaɗun Fillo, har ga Allah tana so ta nemi ahalinta a wannan lokacin to amma ba zata iya ba har sai Fillo ta farka, yarinyar ta taimaka mata a lokacin da take neman taimako.
duk da bayanta yake kallo haka yayi tsaye sai kallonta yake ya kasa ko da motsi, ya kuma kasa ɗauke idonsa akanta, yana jin wani irin abu na shigarsa, yana jin kamar yana so yaga ko wace, gaba ɗaya bai san dai taƙamemen abinda yake ji a tare da shi ba.
yay ajiyar zuciya ya juya ya koma bakin ƙofar, yaci gaba da kallon Fillo yana ta adu'a cikin ransa, bini-bini sai ya kalli agogo ya duba time, cikar lokacin da likita ya ɗiba kawai yake jira, da dukkan fatansa na in lokaci ya cika ta farka lafiya lau. sai dai haka ɗaya kuma yaji totally ya kasa samun nutsuwa, zuciyarsa na masa wani irin zillo, tunaninsa da hankalinsa ya rabu waje biyu, so yake yaci gaba da tsayuwa anan har sanda Fillo zata farka, haka kuma so yake ya bar wajen yaje wajen waccan matar da bai san wacece ba.
ba tare da sani ba ya bar wajen ya nufa wurin da Mum ke zaune har yanzu, ya tsuguna ta gefenta daga ɗan bayanta, ba tare da sanin taƙaimemen abinda zai yi ba, idan ma magana zai mata shi bai san me zaice mata ba, zuciyarsa ce kawai ta kawo shi.
ya buɗe bakinsa zai furta abinda bai san zai ce ba sai ga Ammi ta ƙaraso wajen, bai iya ce mata komai ba ya bita da kallo har ta zagaya ta gaban Mum ta tsuguna agabanta.
Ammi tace,"kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki Hajiya, Ɗana ya tabbatar min da cewar ƴarki zata farka cikin amincewar ubangiji, kuma zata farka lafiya lau insha'Allah".
a sannan Mum ta É—ago da kanta tace,"Allah ya amsa, amma Hajiya lokaci yaja da yawa, har yanzu fa shiru".
tai maganar muryarta É—auke da sautin damuwa.
Ammi ta ƙara cewa,"adu'a zamu ci gaba da yi". Mum bata iya magana ba illa gyaɗa kanta kawai da tayi. bata san me take ji a tare da ita ba, amma dai tana jin zuciyarta na ƙara matsuwa da zullumin son kasancewa acikin ahalinta, ba abinda idanuwanta ke da muradi yanzu sama da su ga Babanta, taga ƴaƴanta tukunna ta sami kwanciyar hankali.
Umma ta ƙaraso wajen, Ammi ta ɗauke kanta daga kallonta, Umma bata kula hakan ba tace,"Ammin Yara wannan itace mahaifiyar yarinyar da Aliyu ya buge ɗin?". Ammi ta kauda fuska gefe tace,"umm ita ce". ta faɗa tana miƙewa ta bar wajen, Umma ta zagaya ta ɗaya ɓarin ta zauna kusa da Mum, suka gaisa tana yi mata adua da sanar mata cewar itama mahaifiya ce wurin yaron da ya bigesu ɗin.
Mum tace,"Allah sarki, mun gode sosai. kun tsaya mana baku bari mun wahala ba".
Umma tace,"to ai hakan ya zama dole akan wanda yasan hakkin bawa".
ta faɗa idonta na kan Turaki da har sannan yake tsugune daga can gefe, kamar wani mutum mutumi sai bin kowa yake da ido, shi abinda ya ɗaure masa kai tun zuwan Ammi wajen yaji tana batun mahaifiyar Fillo, shi yasa yaji kamar ƙafafunsa ma ba zasu iya ɗagawa ba dan haka kawai yaji jikinsa duk yay sanyi, kuma Allah Allah yake yaga fuskar matar.
ganin tsananin kamar dake tsakanin Turaki da Mum wanda Ammi bata lura da hakan ba yasa Umma ce masa,"sannu fa, ya mai jiki?".
Turaki yaji kamar ba da shi take ba, lura da hakan yasa Umma cewa,"da kai nake". ta faÉ—a tana murmushi.
yana sauke idonsa a ƙasa yace,"Alhamdulillah".
tace,"to Allah ya bada lafiya, dan Allah ina daɗa bayar da haƙuri a madadin yarona".
shi dai bai iya cewa komai ba, ya zama kamar wani soko ko me neman gafara. kuma Umman na yin shiru ta hango Nuratu da Mommi na nufo su, har da Inna Wuro dake goye da Farha.
itace a gaba ta taho tana cewa da Umma,"Falmata ni dai Amadu ya rantse yace min ba aljanu ba ne mutanene shisa ma na iya shigowa asibitin nan amma da a waje zan tsaya gaskiya, dan ban iya saka kaina a masifa, Aliyun ma ni da wurin ƴan sanda aka kaishi tunda ance har yanzu yarinyar bata farka ba, ko kawai ayi kotu da ɗan banza kowa kuma sai yay ta kansa kar aja kuɗin Amadu ya ƙare".
Umma ta miƙe tana cewa,"sannu da zuwa Inna".
tana rufe baki Nuratu da Mommi suka iso wajen, dai-dai kuma da miƙewar Turaki. yana tashi idonsa ya kai kan Mommi, ta ke idanuwansa suka firfito waje yana binta da kallo me ban mamaki da al'ajabi, me yake gani?, dama da gaske akwai fuska biyu a duniya?, wannan matar ai photocopy ɗin Fillo ce.
Mommi da ta iso gabansa ta ɗaga masa hannu alamar sannu. mamaki na bala'i ya ƙara kama shi, bai san lokacin da ya kamo hannunta ba ya jata zuwa room ɗin da Fillo ke ciki.
ganin hakan yasa kowa miƙewa yabi bayansu da kallo harta kuwa da Mum da taji su Umma na cewa,"ikon Allah wannan yaron na da lafiya kuwa". Nuratu tace,"ah wannan sai dai mahaukaci". ta faɗa tana bin bayansu da sauri.
Inna Wuro tace,"ah tou haka duk zaku yi ta gamuwa da gamonku, ance aljanu ku ka kwaso kun dage mutanene, ni dai da naga ba zan iya ba ai ta kaina zanyi, wa zai zo ya wahala, haka kawai a shanyen ƙafa ko wuya banji ba ban gani ba".
Umma ta dafa kafaɗar Mum dake bin bayan Nuratu da kallo tana jin shigar wani al'amari me girma a tare da ita. a hankali Umma tace,"am sorry to say, amma ɗanki bai da lafiyar ƙwaƙwalwa ko?". Mum ta juyo da kallonta gareta tace,"ɗana kuma?". ta tambaya da mamaki.
Umma tace,"ehh fa, wanda ke zaune anan kusa da ke". kan Mum ya ƙara ƙullewa tace,"me kike son cewa ne?". ta tambaya tana jin ƙirjinta na bugawa.
jin ƙarar saukar mari ya tattara hankalinsu kan su Turaki gaba ɗaya, Nuratu ce a gabansa tana huci tana faɗin,"baka da hankali ne?, ya daga ganin mahaifiyata zaka kama hannunta, ko an faɗa maka mu kafirai ne kamarka?, shashashan banza da wofi, to wallahi in baka bar asibitin nan cikin gaggawa ba sai nasa ƴan sanda sun zo sun tafi da kai yanzu".
Turaki ya ɗago da fuskarsa yana dafe da kuncinsa, hoton fuskar tasa ya shiga cikin ƙwayar idon Hajiya Ramla da suka ƙaraso wajen da sassarfa. cikin zafin nama Turaki ya ɗaga hannu zai saukewa Nuratu zazzafan mari Hajiya Ramla ta zaro ido waje tana faɗin,"Babana". ta faɗa da ƙarfin sautin da yay amsa kuwa a wajen.