Sashe 95
Captain Abbas Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Anty kuwa bayan tafiyar Teemah da kwana biyu sai taji damuwarta ta dawo mata sabo fil, tunaninta ya yawaita akoda yaushe bata da aiki sai zubda 'kwalla, gashi babu wanda ke zuwa gurinta ayanzun, Abbah ma 'kara nisanta kansa yayi da ita, dan tun tafiyar Teemah sau 'daya kawai ta ganshi, wannan 'dinma ta window ne lokacin shigowar sa gida kenan jin dirin mota yasa ta le'ka sai taganshi.
Ganin sa 'din kuma sai ya 'kara kashe mata zuciyar dan gaba 'daya Abbah ya lalace wani rama taga yayi na masifa, tausayinsa har se da ya sata sakin hawaye, tasan koma menene yafaru laifinta ne, mutuwa ba a hannunta yake ba, amma tasan son zuciyarta shine sanadin komai.
Komawa tayi ta jinginu da jikin window ta lumshe idanu yayinda hawaye suka ci gaba da gangarowa ta 'kasan idanun suna sau'ka saman kuncinta, samata 'daga kanta tace
" _Allah na tuba ka yafe min, ka yafe min kura kuraina, ya ubangiji Allah ka sanyaya zu'katan duk wa'danda na_ ' _kuntatawa, Ya Allah kaji'kan Mahmud ka haskaka masa 'kabarin sa_ "
Washe gari da sassafe tayiwa 'dakin Abbah tsinke, sallamrta ka'dai ya amsa saboda darajar da sallama ke da shi ga dukkan wani musulmi, daga nan yaci gaba da shirinsa be ko kalli inda take ba, kallo 'daya Anty tayi masa ta fahimci cewa shirin tafiya yakeyi dan haka sai ta zauna agefen gado ahankali tace " barka da warhaka Alhaji fatan antshi lafiya"
Da " lafiya 'kalau"
Kawai ya amsa ta atakaice.
Anty ma sai tayi shiru bata 'kara magana ba kawai ta rin'ka binsa da idanu.
Ganin kamar bashi da niyyar sake kulata sai tace dashi
" _Alhaji dan Allah kayi ha'kuri ka yafemin laifukana, ka daina fushi dani,_ _wallahi nayi dana sanin duk abubuwan dana aikata abaya, ni kaina inajin tsanar kaina akan haka_ , _bansan ya zanyi in goge laifina awurin mahallicina ba amma nasan idan kun yafeni wata'kila_ _Allah zaiji tausayina ya min afuwa_ "
_Nasan ban yi mana adalci ba koka'dan, ban kyauta wa rayuwar mu ba gaba 'daya tunda_ _gashi son kaina yasa har nayi sanadin da 'dana yarasa_ _rayuwarsa......_
Kuka ne ya kubce mata tayi na kusan mintina biyu sannan taci gaba da fa'din
" _Mahmud yace kayafe masa Alhaji, yace in ro'ka masa yafiya awurinka akan duk laifukan_ _daya maka arayuwarsa......_
Sai ta sake sakin kuka gwanin tausayi.
Abbah ma dakansa sai da ya share hawaye da jin abinda Anty take fa'di tunanin yaronsa da tausayin kansa ya 'kara kamashi, 'dansa 'kwaya tal da Allah ya bashi gashi be samu damar bashi farin cikin daya dace ba har ya bar duniya, yau gashi babu shi, Mahmud ya tafi, sai de yasan Allahn daya kar6e shi yafishi son shine, yasan kuma Allah baya ta6a barin wani dan wani yaji da'di, sai fatan Allah yayiwa Mahmud Ubangiji ya sada shi da dukkan rahamarsa.
Yana goge hawayen fuskarsa ya 'dauki 'yar 'karamar jakar kayansa daya gama shiryawa tare da 'daukan wayoyinsa ya nufi hanyar fita.
Ganin Abbah na shirin fita batare da taji kalma 'daya me kyau daga bakinsa ba yasata ta mi'ke da hanzari tace
" _Alhaji ko bazaka min magana ba dan Allah kayi min izini in tafi kano_ "
" _Allah ya kiyaye_ _hanya_ "
ya fa'da tare da ficewa abinsa daga 'dakin.
Anty kam kuka tasanya har tana 'dan bubbuga kanta da hannunta, nadama da takaici ne duk suka ha'du sukayi mata yawa, duk da tana farin ciki da barinta da Abbah yayi amma kuma halin dayake cikin ya matu'kar tsaya mata arai, tasan dama ba ze ta6a hanata zuwa kano ba, baze ta6a shiga tsakaninta da ahalinta ba, shi akullum ma burinsa taringa ziyartar su tare da mutunta familynta sa6anin nata halin.
Zata je ta nemi gafarar iyayenta ta gyara dukkan kurakuranta na baya, ta faranta musu a matsayinta na 'ya agare su.
Ko zata samu su yafe mata laifukanta garesu.
*****
Daddy musamman ya baro Dubai yataho domin ya amsa gayyatar Abbas inda suka je shi da Daddyn Abuja suka halacci taron 'karin girmansa inda daga ranar ya amsa matsayinsa na *CAPTAIN* .
Tun acan Daddynsa yafara wa Yayan sa magana akan Abbas 'din, complain ya shigar akan cewa wai yayi-yayi dashi ya yi aure amma ya'ki, shi kuma duk wannan abubuwan ba farin ciki suke saka shi ba, dan ko wani irin matsayi mutun yakai aduniya matu'kar bashi da iyali toh darajarsa ragaggiya ce, gara tun wuri kayi wa 'danka magana yafito da mata inbahaka ba wallahi da kaina zan za6a masa mata idan nagaji da magana.
Murmushi Daddy yayi sannan yace
"Haba Hassan kabarshi mana yasamu nutsuwa, yaushe ma yasamu ya zauna da har za'a fara yi masa maganar aure, shi auren de lokacine idan lokacin yayi kuwa ba se ka tsaya 6ata bakinka ba, da kansa zakaga ya furta, dan Allah ka sarara masa Al-Hassan ka raba masa hankali"
Kauda kai Daddyn Abuja yayi wanda Daddy yafahimci cewa maganar tasa bata wani shiga ransa ba amma de yasan Hassan 'din ba ze taka maganar sa ba tunda ya furta, dan Hassan na matu'kar bashi girmansa sosai.
Daddy daga can ya wuche ko Abuja be dawo ba, saboda baya son ha'duwa da Teemah a dai-dai wannan lokacin dan uasan rigimarta yawa ne da ita.
Abbas kam tare suka dawo gida shida Daddynsa, dan har yanzu acikin hutunsa yake be gama ba.
Sai da yazo gida kafin su Ummah suka shirya wata 'kwarya-'kwaryar walimah acikin gida na tayashi murna, yaji da'di sosai da hakan barin ma daya ga Fateemah ta 'dan saki ranta yanzun bakamar da ba, gashi ta 'dan yi kyan gani duk da hijab ta zun6ula har 'kasa amma hakan be hanashi fahimtar canjawarta ba.
Ahankali ya 'kara fahimtar rungumar 'kaddara da tayi saboda ko a dinning yaga yanzu tana ' dan sake wa taci abinci harma ayi hira da ita, duk da murmusho yafi yawa anata fuskar amma sometimes takan jefa nata ka'dan.
Idan Hannah na makaranta kuwa sau tari da Ummah zaka same ta tmsuna ta'di abinsu, ko kuma ta yi kwanciyarta akan cinyar Ummahn tana shagwa6arta wani lokaci har bacci takeyi agurinta.
*Bayan sati 'daya......*
Teemah ha'kurin ta yafara gazawa ganin har yanzu Yayah Abbas be sake mata maganar tafiyan ba, kuma xe mata yayi idan yadawo zai kata, tayi 'ko'karin kiyaye duk wani abu da tasan ze sa shi canja ra'ayi amma shiru bata ji yace komai ba.
Bata san me zata ce dashi ba dan haka sai ta fara bawa Ummah labari ka'dan-ka'dan, sai tace da Ummahn " _Yayah fah uace zamu je wurin Mummy da Anty in gaishesu amma kuma naji be sake_ _maganan ba_ "
" _Antyn naki ba kince tana kano ba_ ?
Ummah ta tambaya tana kallonta.
Sai tace
" _Ehh tatafi kano, ai shi ne yace zamu_ _wajenta_ "
"Toh inaga be shirya tafiyan bane tukunna, amma nasan tunda har ya fa'da toh babu shakka zai kaiki 'din, zai fison idan kin warawre gaba 'daya"
Cikin shagwa6a tace "Ummah nafa riga warware gaba 'daya"
" _Toh ni Fateemah ni miye nawa, ba fa dani kukayi_ _shawaran ku ba_ "
Kwa6a fuska tayi kamar zata yi kuka gani hakan yasa Ummah ta janyo ta zuwa jikinta ta kwanatar.
" _Haba Fateemah, kiyi ha'kuri mana ki 'dan 'kara bashi lokaci kinji_ "
Ummah ma biye ta ringayi da lallami har zancen ya kau.
Ita kam ma ai jinta take yi kawai, dan ko Abbas ya 'dago zancen tafiyar toh ita ba yadda zatayi ba.
Yawon ai ya isa hakan gara ta zauna wuri 'daya ta iddasa zaman takabarta inyaso daga ko ina ne ma taje.
Teemah kam ha'kurinta 'karewa yayi, kwana biyar bayan maganar da sukayi da Ummah sai taje dakanta tasame shi.
Duk yanda take ganin ta canja Abbas cewa yayi be ga hakan ba shi har yanzu dan haka tafiya ba yanzu ba.
Ranar kam kuka tasha da dare dan haushi, tana cikin kukan ne Anty ta 'kirata awayarta tana 'dauka kuwa tasake mata kuka, take Anty ta rikice ta fara tambayarta abinda ya faru, me aka mata?
cikin kukan tayi mata bayanin komai, Anty kam murmushi tayi dan take ta fahimci wayo kawai Abbas yamata dan ta saki ranta ta sake da kowa, amma duk da haka sai tace da ita
" _har kin sa na ji wani iri ma, ai inajin Abbas 'din yama fiki gaskiya, amma de kiyi ha'kuri kinji, ki bari idan na koma Lagos 'din nasan zai kawo ki tunda shi yafa'di haka, ai yawo banaki bane yanzu Fateemah, akwai sauran lokaci kinji inna samu lokaci ma zanzo na duba ki a Abujan kinji_ ?
Baki ta tura gaba ciki muryar shagwa6arta tace
" _Dan Allah Anty kizo toh, ni nagaji da zaman ne Anty, bafah na zuwa ko'ina ko shopping Hannah ce_ _ka'dai take zuwa, ni Ummah bata_ _barina in bita kuma idan ta dawo sai ta ta min dariya_ "
Murmushi Anty tayi daga 6angarenta, tana mamakin yarintar Teemah ita kam, ashe yarinya ce ' karama sosai har yanzu, tasan koda tace zata mata bayani ma 'kila ba gane manufarta zatayi ba, dan haka sai ta bar wancan tunanin kawai tace
" _Ayyah very sorry kinji, soon kema zaki fita ai yanzun be kamata kina yawo bane shiyasa amma in lokaci yayi nasan babu me hanaki fita_ "
Sosai Anty tayi ta rarrashinta har ta ha'kura tayi shiru.
Ganin ta nutsu yasa har Anty ta bata labarin kaf yanda suka yi da mahaifanta bata 6oye mata komai ba, yanda tasha gwagwarmaya kafin ya amince da ita, da 'kyar ya furta mata kalmar yafiya dan shi tsakaninsa da Allah ya tsani ganinta arayuwarsa ma.
Teemah ta tausaya mata da jin labarin, inda tasake bata 'kwarin gwiwa sosai kamar ba ita bace me zuba shagwa6a ba 'dazu.
Anty najin da'din kasancewa da ita dan ko ba komai takan 'de be mata kewa, gashi tana 'ko'karin bata shawarwari masu kyau duk da take yarinya 'karama amma akwai ta da ilimi, bayan sata ahanya data tayi lokacin suna Lagos, Anty tamkar sa'arta ta maida ita dan duk shawaranta da ita takeyi yanzu, in abune ma ya dameta Teemah take sanarwa su jajanta tare sosai take janta ajiki tana jinta tamkar 6arin zuciyarta ce.
Ganin sa 'din kuma sai ya 'kara kashe mata zuciyar dan gaba 'daya Abbah ya lalace wani rama taga yayi na masifa, tausayinsa har se da ya sata sakin hawaye, tasan koma menene yafaru laifinta ne, mutuwa ba a hannunta yake ba, amma tasan son zuciyarta shine sanadin komai.
Komawa tayi ta jinginu da jikin window ta lumshe idanu yayinda hawaye suka ci gaba da gangarowa ta 'kasan idanun suna sau'ka saman kuncinta, samata 'daga kanta tace
" _Allah na tuba ka yafe min, ka yafe min kura kuraina, ya ubangiji Allah ka sanyaya zu'katan duk wa'danda na_ ' _kuntatawa, Ya Allah kaji'kan Mahmud ka haskaka masa 'kabarin sa_ "
Washe gari da sassafe tayiwa 'dakin Abbah tsinke, sallamrta ka'dai ya amsa saboda darajar da sallama ke da shi ga dukkan wani musulmi, daga nan yaci gaba da shirinsa be ko kalli inda take ba, kallo 'daya Anty tayi masa ta fahimci cewa shirin tafiya yakeyi dan haka sai ta zauna agefen gado ahankali tace " barka da warhaka Alhaji fatan antshi lafiya"
Da " lafiya 'kalau"
Kawai ya amsa ta atakaice.
Anty ma sai tayi shiru bata 'kara magana ba kawai ta rin'ka binsa da idanu.
Ganin kamar bashi da niyyar sake kulata sai tace dashi
" _Alhaji dan Allah kayi ha'kuri ka yafemin laifukana, ka daina fushi dani,_ _wallahi nayi dana sanin duk abubuwan dana aikata abaya, ni kaina inajin tsanar kaina akan haka_ , _bansan ya zanyi in goge laifina awurin mahallicina ba amma nasan idan kun yafeni wata'kila_ _Allah zaiji tausayina ya min afuwa_ "
_Nasan ban yi mana adalci ba koka'dan, ban kyauta wa rayuwar mu ba gaba 'daya tunda_ _gashi son kaina yasa har nayi sanadin da 'dana yarasa_ _rayuwarsa......_
Kuka ne ya kubce mata tayi na kusan mintina biyu sannan taci gaba da fa'din
" _Mahmud yace kayafe masa Alhaji, yace in ro'ka masa yafiya awurinka akan duk laifukan_ _daya maka arayuwarsa......_
Sai ta sake sakin kuka gwanin tausayi.
Abbah ma dakansa sai da ya share hawaye da jin abinda Anty take fa'di tunanin yaronsa da tausayin kansa ya 'kara kamashi, 'dansa 'kwaya tal da Allah ya bashi gashi be samu damar bashi farin cikin daya dace ba har ya bar duniya, yau gashi babu shi, Mahmud ya tafi, sai de yasan Allahn daya kar6e shi yafishi son shine, yasan kuma Allah baya ta6a barin wani dan wani yaji da'di, sai fatan Allah yayiwa Mahmud Ubangiji ya sada shi da dukkan rahamarsa.
Yana goge hawayen fuskarsa ya 'dauki 'yar 'karamar jakar kayansa daya gama shiryawa tare da 'daukan wayoyinsa ya nufi hanyar fita.
Ganin Abbah na shirin fita batare da taji kalma 'daya me kyau daga bakinsa ba yasata ta mi'ke da hanzari tace
" _Alhaji ko bazaka min magana ba dan Allah kayi min izini in tafi kano_ "
" _Allah ya kiyaye_ _hanya_ "
ya fa'da tare da ficewa abinsa daga 'dakin.
Anty kam kuka tasanya har tana 'dan bubbuga kanta da hannunta, nadama da takaici ne duk suka ha'du sukayi mata yawa, duk da tana farin ciki da barinta da Abbah yayi amma kuma halin dayake cikin ya matu'kar tsaya mata arai, tasan dama ba ze ta6a hanata zuwa kano ba, baze ta6a shiga tsakaninta da ahalinta ba, shi akullum ma burinsa taringa ziyartar su tare da mutunta familynta sa6anin nata halin.
Zata je ta nemi gafarar iyayenta ta gyara dukkan kurakuranta na baya, ta faranta musu a matsayinta na 'ya agare su.
Ko zata samu su yafe mata laifukanta garesu.
*****
Daddy musamman ya baro Dubai yataho domin ya amsa gayyatar Abbas inda suka je shi da Daddyn Abuja suka halacci taron 'karin girmansa inda daga ranar ya amsa matsayinsa na *CAPTAIN* .
Tun acan Daddynsa yafara wa Yayan sa magana akan Abbas 'din, complain ya shigar akan cewa wai yayi-yayi dashi ya yi aure amma ya'ki, shi kuma duk wannan abubuwan ba farin ciki suke saka shi ba, dan ko wani irin matsayi mutun yakai aduniya matu'kar bashi da iyali toh darajarsa ragaggiya ce, gara tun wuri kayi wa 'danka magana yafito da mata inbahaka ba wallahi da kaina zan za6a masa mata idan nagaji da magana.
Murmushi Daddy yayi sannan yace
"Haba Hassan kabarshi mana yasamu nutsuwa, yaushe ma yasamu ya zauna da har za'a fara yi masa maganar aure, shi auren de lokacine idan lokacin yayi kuwa ba se ka tsaya 6ata bakinka ba, da kansa zakaga ya furta, dan Allah ka sarara masa Al-Hassan ka raba masa hankali"
Kauda kai Daddyn Abuja yayi wanda Daddy yafahimci cewa maganar tasa bata wani shiga ransa ba amma de yasan Hassan 'din ba ze taka maganar sa ba tunda ya furta, dan Hassan na matu'kar bashi girmansa sosai.
Daddy daga can ya wuche ko Abuja be dawo ba, saboda baya son ha'duwa da Teemah a dai-dai wannan lokacin dan uasan rigimarta yawa ne da ita.
Abbas kam tare suka dawo gida shida Daddynsa, dan har yanzu acikin hutunsa yake be gama ba.
Sai da yazo gida kafin su Ummah suka shirya wata 'kwarya-'kwaryar walimah acikin gida na tayashi murna, yaji da'di sosai da hakan barin ma daya ga Fateemah ta 'dan saki ranta yanzun bakamar da ba, gashi ta 'dan yi kyan gani duk da hijab ta zun6ula har 'kasa amma hakan be hanashi fahimtar canjawarta ba.
Ahankali ya 'kara fahimtar rungumar 'kaddara da tayi saboda ko a dinning yaga yanzu tana ' dan sake wa taci abinci harma ayi hira da ita, duk da murmusho yafi yawa anata fuskar amma sometimes takan jefa nata ka'dan.
Idan Hannah na makaranta kuwa sau tari da Ummah zaka same ta tmsuna ta'di abinsu, ko kuma ta yi kwanciyarta akan cinyar Ummahn tana shagwa6arta wani lokaci har bacci takeyi agurinta.
*Bayan sati 'daya......*
Teemah ha'kurin ta yafara gazawa ganin har yanzu Yayah Abbas be sake mata maganar tafiyan ba, kuma xe mata yayi idan yadawo zai kata, tayi 'ko'karin kiyaye duk wani abu da tasan ze sa shi canja ra'ayi amma shiru bata ji yace komai ba.
Bata san me zata ce dashi ba dan haka sai ta fara bawa Ummah labari ka'dan-ka'dan, sai tace da Ummahn " _Yayah fah uace zamu je wurin Mummy da Anty in gaishesu amma kuma naji be sake_ _maganan ba_ "
" _Antyn naki ba kince tana kano ba_ ?
Ummah ta tambaya tana kallonta.
Sai tace
" _Ehh tatafi kano, ai shi ne yace zamu_ _wajenta_ "
"Toh inaga be shirya tafiyan bane tukunna, amma nasan tunda har ya fa'da toh babu shakka zai kaiki 'din, zai fison idan kin warawre gaba 'daya"
Cikin shagwa6a tace "Ummah nafa riga warware gaba 'daya"
" _Toh ni Fateemah ni miye nawa, ba fa dani kukayi_ _shawaran ku ba_ "
Kwa6a fuska tayi kamar zata yi kuka gani hakan yasa Ummah ta janyo ta zuwa jikinta ta kwanatar.
" _Haba Fateemah, kiyi ha'kuri mana ki 'dan 'kara bashi lokaci kinji_ "
Ummah ma biye ta ringayi da lallami har zancen ya kau.
Ita kam ma ai jinta take yi kawai, dan ko Abbas ya 'dago zancen tafiyar toh ita ba yadda zatayi ba.
Yawon ai ya isa hakan gara ta zauna wuri 'daya ta iddasa zaman takabarta inyaso daga ko ina ne ma taje.
Teemah kam ha'kurinta 'karewa yayi, kwana biyar bayan maganar da sukayi da Ummah sai taje dakanta tasame shi.
Duk yanda take ganin ta canja Abbas cewa yayi be ga hakan ba shi har yanzu dan haka tafiya ba yanzu ba.
Ranar kam kuka tasha da dare dan haushi, tana cikin kukan ne Anty ta 'kirata awayarta tana 'dauka kuwa tasake mata kuka, take Anty ta rikice ta fara tambayarta abinda ya faru, me aka mata?
cikin kukan tayi mata bayanin komai, Anty kam murmushi tayi dan take ta fahimci wayo kawai Abbas yamata dan ta saki ranta ta sake da kowa, amma duk da haka sai tace da ita
" _har kin sa na ji wani iri ma, ai inajin Abbas 'din yama fiki gaskiya, amma de kiyi ha'kuri kinji, ki bari idan na koma Lagos 'din nasan zai kawo ki tunda shi yafa'di haka, ai yawo banaki bane yanzu Fateemah, akwai sauran lokaci kinji inna samu lokaci ma zanzo na duba ki a Abujan kinji_ ?
Baki ta tura gaba ciki muryar shagwa6arta tace
" _Dan Allah Anty kizo toh, ni nagaji da zaman ne Anty, bafah na zuwa ko'ina ko shopping Hannah ce_ _ka'dai take zuwa, ni Ummah bata_ _barina in bita kuma idan ta dawo sai ta ta min dariya_ "
Murmushi Anty tayi daga 6angarenta, tana mamakin yarintar Teemah ita kam, ashe yarinya ce ' karama sosai har yanzu, tasan koda tace zata mata bayani ma 'kila ba gane manufarta zatayi ba, dan haka sai ta bar wancan tunanin kawai tace
" _Ayyah very sorry kinji, soon kema zaki fita ai yanzun be kamata kina yawo bane shiyasa amma in lokaci yayi nasan babu me hanaki fita_ "
Sosai Anty tayi ta rarrashinta har ta ha'kura tayi shiru.
Ganin ta nutsu yasa har Anty ta bata labarin kaf yanda suka yi da mahaifanta bata 6oye mata komai ba, yanda tasha gwagwarmaya kafin ya amince da ita, da 'kyar ya furta mata kalmar yafiya dan shi tsakaninsa da Allah ya tsani ganinta arayuwarsa ma.
Teemah ta tausaya mata da jin labarin, inda tasake bata 'kwarin gwiwa sosai kamar ba ita bace me zuba shagwa6a ba 'dazu.
Anty najin da'din kasancewa da ita dan ko ba komai takan 'de be mata kewa, gashi tana 'ko'karin bata shawarwari masu kyau duk da take yarinya 'karama amma akwai ta da ilimi, bayan sata ahanya data tayi lokacin suna Lagos, Anty tamkar sa'arta ta maida ita dan duk shawaranta da ita takeyi yanzu, in abune ma ya dameta Teemah take sanarwa su jajanta tare sosai take janta ajiki tana jinta tamkar 6arin zuciyarta ce.