Sashe 77
Captain Abbas Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daga nan suka zarce hiran rayuwa acikin hiran ne Teemah ta tuna da mahaifiyarta, take kuwa sai jikinta yayi sanyi tafara bawa Matar Umar labarin rashin jin iyayen nata da batayi ba gashi tarasa yazata yi ta same su tace kota 'kira gidan 'kanin mahaifinta ma (Daddyn Abuja)
bata samun gamsashshiyar amsa daga wurin su.
Ta tausaya wa Teemah har ranta da jin cewa tun bayan aurenta da kwanaki ka'dan bata 'kara jin iyayenta ba, gashi guri da nisa ba kusa ba balle ta je ta ganosu, bayan hakama garin ba zaman lafiya ake yi ba dole hankalin Teemah yatashi.
'Dan tunani ka'dan matar Umar tayi sai tace da Teemahn ta 'dauko wayarta suyi wani abu.
Tashi tayi taje ta 'dauko wayar sai matar Umar tace ta gwada 'kiran Mahmud su gaisa tunda basuyi waya da safiyar yau ba sai ta tambaye shi ko yanada layin Umman Abujan kode wani haka acan tace yatura mata domin tayi loosing wasu contact 'din ta kuma tana son ta 'kira su ne.
Koda ta 'kira shin kuwa sai yace bashi da numbern kowa sai na Abbas, amma zai tambaye shi sai ya tura masa idan yaturo zai mata sending.
Da " _toh_ " ta amsa masa daga nan sai ta kashe 'kiran.
Shiru matar Umar tayi tana tunanin wata mafita dan kuwa tana ganin kamar idan Mahmud ya turo numbers 'din shirinta ya wargaje, taso ne kowa ya zamana bashi da contact 'din tsakaninsu.
Teemah kuwa tsayawa tayi tana kallon ta domin jin manufar hakan daga bakinta.
Tsawon mintina biyar suna ahaka sai ga 'kiran Mahmud yadawo wayar Teemah, bin wayar tayi da kallo kafin daga bisani ta 'daga wayar ta sada shi da kunnan ta.
Daga 'daya 6angaren Mahmud jikinsa da sanyi yake ce mata " _Tayi ha'kuri zuwa wani lokaci dan Abbas_ ' _din yanzu_ yana cikin maiduguri yana kan aiki kuma anyanke gaba 'daya network 'din Borno harma da wasu garuruwan dake makwabta ka dasu, so ba zai same shi ayanzun ba sai de ko inya 'kira shi ko kuma idan yadawo sai suje gurin Abbah yabasu numbern Daddyn Abujan inyaso sai ya ha'da ta da su Hannah. Daga 'karshe yace taringa yiwa Abbas 'din addu'a pls, yanzu shima ake fa'da masa cewar maidugurin ba lafiya ahalin yanzu an kai musu harin bazata.
Teemah ji tayi hankalinta yatashi da batun Mahmud 'din na 'karshe.
Tana sau'ke wayar tafara dialling numbern Abbas amma baya tafiya, tayi harta gaji ta ha'kura.
Yanda abin ya tsaye mata kuwa har yasa tafara hawaye, yanzun hankalinta yafi kullum tashi saboda damuwarta sun kara yawaita ne musamman data ji cewa Yah Abbas na cikin maiduguri kuma ankai hari ga kuma iyayenta a damaturu kuma bata samunsu awaya ga kuma sarka'kiyar Anty to me ke faruwa ne ? Abin nan na matu'kar damunta sosai.
Da 'kyar Matar Umar ta lallashe ta ta samu ta 'dan nutsu sai ta ringa kwantar mata da hankali ta ce mata bari suyi wani game wata'kila zata samu jin labarin iyayen nata idan tayi sa'a.
Tace Teemah ta 'kira Hannah tace mata tana hanya yau zataje dubo iyayenta.
Hakan kuwa akayi Teemah ta 'kira Hannah ta gaya mata abinda matar Umar 'din ta ce ta fa'da sai taji Hannah ta rikice tana mata masifar waye yace mata ta hau hanya, tasan kuwa irin abinda ke faruwa awancen yankin, tace tun wuri ki nemi damar da zaki koma gida inba so kike kiyi tafiyar banza ba"
Cikin sanyin murya Teemah tace
" _tafiyar banza kuma Hannah, nida zanje inga mummy da Daddy nah_ ?
" _angaya miki mummy tana can ne? Me yasa baki_ _fa'dawa Ummah ba kafin ki fara shirin tafiyar?_
arikice Hannah take duk wannan maganar.
Matar umar najin haka aranta tace " _anzo gurin_ "
Domin wayar a handsfree take duk atare suke jin komai.
Suna jinta ta cikin wayar tana ta kwallah 'kiran _Ummah_ arikice, _Ummah_ !...... _Ummah_ !!......... _Ummah kinji abinda Teemah ta ke shirin_ _yi kuwa? Wai fah takama hanyar zuwa_ _damaturu ayau 'din nan._
Kar6ar wayar Ummah tayi tana kar6a itama tafara fa'din " _Fateemah meyasa kika yanke wannan shawaran batare da kin sanar_ _dani ba!_
shiru Teemah tayi Ummah kuwa sai taci gaba da magana tace " _ina Mahmud 'din yake?_
Sai alokacin Teemah tace
" _Nabarshi agida yasani a mota ne shi ya koma gida_ "
Azabure Ummah tace
" _kina nufin amota zakiyi duk wannan doguwar tafiyar_ _Fateeemah kuma ke_ _ka'dai?_
" _a ina kuke yanzun?_
Ummah tasake tambayarta.
Kame-kame Teemah tafara kamar irin zata fa'di wurin 'din nan sai Ummah ta tare ta da fa'din " _koma a ina ne ki maza ki dakatar da tafiyar nan ki koma gida dan kuwa Khadeeja basu_ ' _kasar nan a halin_ _yanzu suna Dubai"_
Wani sanyin da'di Teemah taji ya ratsata take farin ciki ya bayyana akan fuskarta tana murmushi tace " _har Dubai mummy ta tafi shine bata sanar dani ba_ _Ummah.....toh ki tura min numbernta idan na koma sai_ _in' kirata."!_
Da sauri Ummah ta tare ta da fadin
" _Ehh zan tura miki amma ki kula da zarar kun shigo cikin gari ki ce da su su sau'ke_ _ki ki nemi mota ki koma gida indai bakuyi nisa ba, in kuma_ _kunyi nisa ki iso_ _nan Abuja"_
" ah ah bamuyi nisa ba Ummah"
Teemah ta da ita.
" _toh maza ki koma gida zansa Hannah ta tura miki layin Mummyn naki_ _yanzu"_
Ummah ta 'karasa da mita inda take cewa
" _amma ni wallahi wannan karan Mahmud be birge ni ba, taya zai biye shirmenki yasaki_ _amota ke ka'dai kuma ya kwantar da hankalinsa agida_ _da sunan kinyi tafiya, wannan ai rashin hankali ne, inkin koma gida ki_ _ha'da ni dashi dan_ _Allah"_ !
Da " _toh_ " Teemah ta amsa mata sannan ta yanke 'kiran tana me farin ciki da wannan al'amarin har tsalle ta buga ta rungume matar Umar da 'karfi tana me zuba mata ruwan godiya da wannan babban kyautan datayi mata, itama dariyar takeyi tana me nuna farin cikinta afili ganin yau Teemah tasaki ranta sosai.
Mintina biyu basu cika ba taji wayar ta tayi 'karan shigowan text, da sauri ta 'daga ta duba sai kuwa taga international number aka turo mata harda 'karamin plus a afarkon numbers 'din.
Godiya ta 'kara yiwa Allah tare da fa'din " _Yah mahmud ka gafarceni na maka sharri nasan yanzun zuciyar_ _Ummah acike take taf da jin haushinka amma_ _zan warware komai_ _daga baya_ ".
Take ta gwada 'kiran layin da aka turo matan sai kuwa taji yashiga.
" _Assalamu alaikum_ "
Tajiyo muryar Mummy na fa'din haka.
Lumshe idanu tayi sai taji zuciyarta ta karye take hawaye ya ratso tacikin lumsassun idanun ya gangaro kan kumatunta,
Ahankali tace " _mummy ke ce_ ?
Ita kanta mummy jikinta rawa yafara da jin muryar 'yar tata bayan tsawon wasu kwanaki, sai tace " _nice mamana ya kike"_
" _Mummy shine kika manta dani keda daddy kuka yi tafiyarku wata 'kasa kuka barni anan ko_ _nemana baku 'kara yi ba, mummy daman idan anyiwa mutun aure_ _mantawa ake yi dashi?,mummy ina daddy na yake inji muryarsa"_
Shiru mummy tayi tausayin 'yartata na ratsa zuciya da gangan jikinta ita ma ba 'karamin dauriya tayi ba harta kai tsawon wannan lokacin bata nemeta ba, takan yawaita jero numbers 'din Teemah kamar zata 'kira amma sai ta fasa saboda bin dokar da Daddyn yakafa mata bata son ta karya masa dokarsa har ransa ya 6aci shiyasa takasa 'kiran Teemah koda sau 'daya ne.
ahankali tafurta " _hoo Teemah irin wannan tambayoyin wanne daga ciki zan fara amsa miki?_
" _Duk kansu mummy_ "
Teemah tabata amsa cikin za'kuwa.
Murmushi kawai mummy tayi sai ta fara bata ha'kuri tana mai tambayarta yanayin zamanta da Anty da kuma mijinta. Teemah tace komai normal babu matsalar komai.
Teemah taso ta sanar da Mummy matsalar dake tsakaninta da Anty amma tana tsoron abinda ze biyo baya dan tasan mummy ba shiru zatayi ba idan taji maganar dole sai ta nemi fitar da ita daga al'amarin wanda hakan ke dai dai da tsayawar numfashinta akowani lokaci.
Suna cikin yin wayar daddy ya shigo sai kuwa mummy ta mi'ka masa wayar batare da tayi masa magana ba " _waye_" ya tambayi mummyn 'kasa 'kasa yanda mummyn ka'dai zataji shi.
Sai dai Teemah ta jiyo shi itama sai ta ce dashi " _daddy_ _nice fah_ " cikin shagwa6a tayi maganar.
" _ahh ah Angel 'dina kece yau akan layi?_
" _daddy shine kaima ka manta dani ko?_
" _Waye ya gaya miki haka? bana so mu ringa damunki ne shiyasa kika jimu shiru amma yanzu_ _ma haka ina planning zan shiga lagos 'din next_ _week"._
Take tace
" _Allah daddy dagaske?_
Murmushi kawai yai mata batare da ya yi magana ba.
Sai itace tasake fa'din " _daddy dan Allah idan kazo karka tafi bamu ha'du ba akwai maganar danake_ _so ingaya maka!"_
Sai yanzun yace
" _Toh shikenan insha Allahu zan zo har gida karki damu ki kwantar da hankalinki muma_ _bamu ta6a_ _mantawa da ke ba_ _kinji_ "
*****
Yau ba 'karamin da'di take ji ba, tana gama waya dasu ta 'kira Mahmud tasanar dashi cewa yau sunyi waya da Mummy harda daddy ma"
Tambayarta yayi taya hakan yafaru kode sune suka kirata, sai tace ah ahh ita ta 'kirasu daga nan tabashi labarin yanda akayi harma da maganar da Ummah tafa'da akansa, yana dariya yace " _lallai yarinyar nan wuyanki yayi 'karfi wato harda ni acikin shirin 'karyan_ _naki_ _ko_ ?
Dariya itama tayi tare da yanke wayar.
Ba'a jima ba sai ga 'kiran Ummah tana me sake tambayarta kota koma gidan, sai Teemah tayi mata 'karyar yanzu ta sauka za'a sata motane yanzun, sai tace idan ta koma gida zata 'kirata
" _yauwa Fateemah maza ki koma gida kinji, Allah ya tsare ya kare ya kuma_ _bada sa'a_ "
cewar Ummah
" _ameen Ummah_ , _nagode a_ ".
bata samun gamsashshiyar amsa daga wurin su.
Ta tausaya wa Teemah har ranta da jin cewa tun bayan aurenta da kwanaki ka'dan bata 'kara jin iyayenta ba, gashi guri da nisa ba kusa ba balle ta je ta ganosu, bayan hakama garin ba zaman lafiya ake yi ba dole hankalin Teemah yatashi.
'Dan tunani ka'dan matar Umar tayi sai tace da Teemahn ta 'dauko wayarta suyi wani abu.
Tashi tayi taje ta 'dauko wayar sai matar Umar tace ta gwada 'kiran Mahmud su gaisa tunda basuyi waya da safiyar yau ba sai ta tambaye shi ko yanada layin Umman Abujan kode wani haka acan tace yatura mata domin tayi loosing wasu contact 'din ta kuma tana son ta 'kira su ne.
Koda ta 'kira shin kuwa sai yace bashi da numbern kowa sai na Abbas, amma zai tambaye shi sai ya tura masa idan yaturo zai mata sending.
Da " _toh_ " ta amsa masa daga nan sai ta kashe 'kiran.
Shiru matar Umar tayi tana tunanin wata mafita dan kuwa tana ganin kamar idan Mahmud ya turo numbers 'din shirinta ya wargaje, taso ne kowa ya zamana bashi da contact 'din tsakaninsu.
Teemah kuwa tsayawa tayi tana kallon ta domin jin manufar hakan daga bakinta.
Tsawon mintina biyar suna ahaka sai ga 'kiran Mahmud yadawo wayar Teemah, bin wayar tayi da kallo kafin daga bisani ta 'daga wayar ta sada shi da kunnan ta.
Daga 'daya 6angaren Mahmud jikinsa da sanyi yake ce mata " _Tayi ha'kuri zuwa wani lokaci dan Abbas_ ' _din yanzu_ yana cikin maiduguri yana kan aiki kuma anyanke gaba 'daya network 'din Borno harma da wasu garuruwan dake makwabta ka dasu, so ba zai same shi ayanzun ba sai de ko inya 'kira shi ko kuma idan yadawo sai suje gurin Abbah yabasu numbern Daddyn Abujan inyaso sai ya ha'da ta da su Hannah. Daga 'karshe yace taringa yiwa Abbas 'din addu'a pls, yanzu shima ake fa'da masa cewar maidugurin ba lafiya ahalin yanzu an kai musu harin bazata.
Teemah ji tayi hankalinta yatashi da batun Mahmud 'din na 'karshe.
Tana sau'ke wayar tafara dialling numbern Abbas amma baya tafiya, tayi harta gaji ta ha'kura.
Yanda abin ya tsaye mata kuwa har yasa tafara hawaye, yanzun hankalinta yafi kullum tashi saboda damuwarta sun kara yawaita ne musamman data ji cewa Yah Abbas na cikin maiduguri kuma ankai hari ga kuma iyayenta a damaturu kuma bata samunsu awaya ga kuma sarka'kiyar Anty to me ke faruwa ne ? Abin nan na matu'kar damunta sosai.
Da 'kyar Matar Umar ta lallashe ta ta samu ta 'dan nutsu sai ta ringa kwantar mata da hankali ta ce mata bari suyi wani game wata'kila zata samu jin labarin iyayen nata idan tayi sa'a.
Tace Teemah ta 'kira Hannah tace mata tana hanya yau zataje dubo iyayenta.
Hakan kuwa akayi Teemah ta 'kira Hannah ta gaya mata abinda matar Umar 'din ta ce ta fa'da sai taji Hannah ta rikice tana mata masifar waye yace mata ta hau hanya, tasan kuwa irin abinda ke faruwa awancen yankin, tace tun wuri ki nemi damar da zaki koma gida inba so kike kiyi tafiyar banza ba"
Cikin sanyin murya Teemah tace
" _tafiyar banza kuma Hannah, nida zanje inga mummy da Daddy nah_ ?
" _angaya miki mummy tana can ne? Me yasa baki_ _fa'dawa Ummah ba kafin ki fara shirin tafiyar?_
arikice Hannah take duk wannan maganar.
Matar umar najin haka aranta tace " _anzo gurin_ "
Domin wayar a handsfree take duk atare suke jin komai.
Suna jinta ta cikin wayar tana ta kwallah 'kiran _Ummah_ arikice, _Ummah_ !...... _Ummah_ !!......... _Ummah kinji abinda Teemah ta ke shirin_ _yi kuwa? Wai fah takama hanyar zuwa_ _damaturu ayau 'din nan._
Kar6ar wayar Ummah tayi tana kar6a itama tafara fa'din " _Fateemah meyasa kika yanke wannan shawaran batare da kin sanar_ _dani ba!_
shiru Teemah tayi Ummah kuwa sai taci gaba da magana tace " _ina Mahmud 'din yake?_
Sai alokacin Teemah tace
" _Nabarshi agida yasani a mota ne shi ya koma gida_ "
Azabure Ummah tace
" _kina nufin amota zakiyi duk wannan doguwar tafiyar_ _Fateeemah kuma ke_ _ka'dai?_
" _a ina kuke yanzun?_
Ummah tasake tambayarta.
Kame-kame Teemah tafara kamar irin zata fa'di wurin 'din nan sai Ummah ta tare ta da fa'din " _koma a ina ne ki maza ki dakatar da tafiyar nan ki koma gida dan kuwa Khadeeja basu_ ' _kasar nan a halin_ _yanzu suna Dubai"_
Wani sanyin da'di Teemah taji ya ratsata take farin ciki ya bayyana akan fuskarta tana murmushi tace " _har Dubai mummy ta tafi shine bata sanar dani ba_ _Ummah.....toh ki tura min numbernta idan na koma sai_ _in' kirata."!_
Da sauri Ummah ta tare ta da fadin
" _Ehh zan tura miki amma ki kula da zarar kun shigo cikin gari ki ce da su su sau'ke_ _ki ki nemi mota ki koma gida indai bakuyi nisa ba, in kuma_ _kunyi nisa ki iso_ _nan Abuja"_
" ah ah bamuyi nisa ba Ummah"
Teemah ta da ita.
" _toh maza ki koma gida zansa Hannah ta tura miki layin Mummyn naki_ _yanzu"_
Ummah ta 'karasa da mita inda take cewa
" _amma ni wallahi wannan karan Mahmud be birge ni ba, taya zai biye shirmenki yasaki_ _amota ke ka'dai kuma ya kwantar da hankalinsa agida_ _da sunan kinyi tafiya, wannan ai rashin hankali ne, inkin koma gida ki_ _ha'da ni dashi dan_ _Allah"_ !
Da " _toh_ " Teemah ta amsa mata sannan ta yanke 'kiran tana me farin ciki da wannan al'amarin har tsalle ta buga ta rungume matar Umar da 'karfi tana me zuba mata ruwan godiya da wannan babban kyautan datayi mata, itama dariyar takeyi tana me nuna farin cikinta afili ganin yau Teemah tasaki ranta sosai.
Mintina biyu basu cika ba taji wayar ta tayi 'karan shigowan text, da sauri ta 'daga ta duba sai kuwa taga international number aka turo mata harda 'karamin plus a afarkon numbers 'din.
Godiya ta 'kara yiwa Allah tare da fa'din " _Yah mahmud ka gafarceni na maka sharri nasan yanzun zuciyar_ _Ummah acike take taf da jin haushinka amma_ _zan warware komai_ _daga baya_ ".
Take ta gwada 'kiran layin da aka turo matan sai kuwa taji yashiga.
" _Assalamu alaikum_ "
Tajiyo muryar Mummy na fa'din haka.
Lumshe idanu tayi sai taji zuciyarta ta karye take hawaye ya ratso tacikin lumsassun idanun ya gangaro kan kumatunta,
Ahankali tace " _mummy ke ce_ ?
Ita kanta mummy jikinta rawa yafara da jin muryar 'yar tata bayan tsawon wasu kwanaki, sai tace " _nice mamana ya kike"_
" _Mummy shine kika manta dani keda daddy kuka yi tafiyarku wata 'kasa kuka barni anan ko_ _nemana baku 'kara yi ba, mummy daman idan anyiwa mutun aure_ _mantawa ake yi dashi?,mummy ina daddy na yake inji muryarsa"_
Shiru mummy tayi tausayin 'yartata na ratsa zuciya da gangan jikinta ita ma ba 'karamin dauriya tayi ba harta kai tsawon wannan lokacin bata nemeta ba, takan yawaita jero numbers 'din Teemah kamar zata 'kira amma sai ta fasa saboda bin dokar da Daddyn yakafa mata bata son ta karya masa dokarsa har ransa ya 6aci shiyasa takasa 'kiran Teemah koda sau 'daya ne.
ahankali tafurta " _hoo Teemah irin wannan tambayoyin wanne daga ciki zan fara amsa miki?_
" _Duk kansu mummy_ "
Teemah tabata amsa cikin za'kuwa.
Murmushi kawai mummy tayi sai ta fara bata ha'kuri tana mai tambayarta yanayin zamanta da Anty da kuma mijinta. Teemah tace komai normal babu matsalar komai.
Teemah taso ta sanar da Mummy matsalar dake tsakaninta da Anty amma tana tsoron abinda ze biyo baya dan tasan mummy ba shiru zatayi ba idan taji maganar dole sai ta nemi fitar da ita daga al'amarin wanda hakan ke dai dai da tsayawar numfashinta akowani lokaci.
Suna cikin yin wayar daddy ya shigo sai kuwa mummy ta mi'ka masa wayar batare da tayi masa magana ba " _waye_" ya tambayi mummyn 'kasa 'kasa yanda mummyn ka'dai zataji shi.
Sai dai Teemah ta jiyo shi itama sai ta ce dashi " _daddy_ _nice fah_ " cikin shagwa6a tayi maganar.
" _ahh ah Angel 'dina kece yau akan layi?_
" _daddy shine kaima ka manta dani ko?_
" _Waye ya gaya miki haka? bana so mu ringa damunki ne shiyasa kika jimu shiru amma yanzu_ _ma haka ina planning zan shiga lagos 'din next_ _week"._
Take tace
" _Allah daddy dagaske?_
Murmushi kawai yai mata batare da ya yi magana ba.
Sai itace tasake fa'din " _daddy dan Allah idan kazo karka tafi bamu ha'du ba akwai maganar danake_ _so ingaya maka!"_
Sai yanzun yace
" _Toh shikenan insha Allahu zan zo har gida karki damu ki kwantar da hankalinki muma_ _bamu ta6a_ _mantawa da ke ba_ _kinji_ "
*****
Yau ba 'karamin da'di take ji ba, tana gama waya dasu ta 'kira Mahmud tasanar dashi cewa yau sunyi waya da Mummy harda daddy ma"
Tambayarta yayi taya hakan yafaru kode sune suka kirata, sai tace ah ahh ita ta 'kirasu daga nan tabashi labarin yanda akayi harma da maganar da Ummah tafa'da akansa, yana dariya yace " _lallai yarinyar nan wuyanki yayi 'karfi wato harda ni acikin shirin 'karyan_ _naki_ _ko_ ?
Dariya itama tayi tare da yanke wayar.
Ba'a jima ba sai ga 'kiran Ummah tana me sake tambayarta kota koma gidan, sai Teemah tayi mata 'karyar yanzu ta sauka za'a sata motane yanzun, sai tace idan ta koma gida zata 'kirata
" _yauwa Fateemah maza ki koma gida kinji, Allah ya tsare ya kare ya kuma_ _bada sa'a_ "
cewar Ummah
" _ameen Ummah_ , _nagode a_ ".