Sashe 24
Captain Abbas Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dakansa ya dinga nuna abinda za'a mik'o musu While Teemah na zaune a gefe ko kallo bai isheta ba dan ita gaba d'aya zuciyar ta tatafi ne ga tuanain zai 6ata mata lokaci dan bata son ta makara zuwa birthday d'in da'ake yi na k'awartan hartana zooming d'in yanda k'awayenta zasu fara cashewa ba ita, tasan da tana da waya da yau d'innan k'ira sai ya isheta.
Haka yayi sayayyansa kaca-kaca sannan ya jagorancesu suka fito daga shagon suka kuma shiga mota.
Atunanin Teemah daga nan gurin partyn zasu wuce dan harta fara murna amma sai taga ya d'auki wani hanya daban haka yaita zaga cikin gari kamar me neman wani abu daga k'arshe sai ya nufi hanyar gida.
Teemah tayi ta masa magana yafi sau a k'irga amma ko kallon 6angaren da take ma baiyi ba ballantana ya kulata balle har tasamu amsar maganar da ta masa.
Sai da taga ya d'auki hanyar gidan kafin tasake masa magana akan batun birthday party d'in, duk da bata da tabbacin zai amsata amma sai da tayi dan tasan ko bai bata amsa ba ai dai ya ji ta.
Ga mamakinta kuwa sai taji yanzun ya bata takaitacciyar amsa da " bazaki ba" ya bata amsan ne batare da ko kallon kirki ba.
Ai tanajin haka sai ta fara bori da kuka dan harga ba k'aramin haushin fita da shi d'in nan tayi yau ba, data sani dama adaidaitan ta hau..........
data sani dama Habibu driver ne ya kaita.......
Data sani tayi shi yafi sau ak'irga.
Shikuwa koda yaga tana kukan sai bai kulata ba illah juya kan motar da yayi ya shiga u-turn ya dawo da baya,murna tafara daganin hakan atunaninta zai kai tan ne, dan daman wucewarsu unguwar su Leemah (birthday girl) kenan dataga bayada niyyar shiga shine tamasa magana dajin amasr daya bata kuwa sai tafara wannan iskancin kukan.
Ganin yasake wucewa sai kawai ta yi tagumi dan zuwa yanzun tagama sawa ranta tayi missing birthday d'in kenan har ma tanaji aranta cewar ya wuceta already.
Hanyar Jerusalem ward ya d'auka dake gefen nursing school, sai kuma tafara tunanin toh me suka zo yi anan kuma?
Kar dai wata yarinyar kuma ya kwaso acikin unguwar nan kuma?
Kauda kai tayi gefe tare da jan tsaki aranta ta kuma fad'in mutun sai kwashe-kwashen tsiya har arn......ma bai bari ba.
YETIM care foundation (gidan marayu) taga yayi parking awurin ya fito sai da tayi kalle-kalle kafin ita ma tafito tabiyo bayansa suka shiga ciki.
Sun tarar ma ana wani programme sai basu wani dad'e ba suka fito bayan ya gaiggaisa da mutanen wurin akan sai gobe insha Allahu zai dawo.
Mota suka koma yaja ya nufi hanyar gida.
Yanzun kam da suka fito bata wani tsaya mamaki ba bud'e bakinta tayi ta tambayeshi muryarta wasai tace" yayah yaushe kasan nan wurin?
Sai da ya kalleta kafin yace "Mahmud ne ya kawo ni nima kwanaki"
"Sai ta sake cewa " toh shi yah Mahmud d'in wa ya nuna masa ai naga shima bai san nan garin ba akace"?
"Toh sai ki jira idan yazo ki masa wannan tambayar?
Yayi maganan ne fuskarsa ba yabo ba fallasa sai ta d'an ji dad'in hakan hartaji tasamu k'arfin gwiwar sake yi masa magana, aikuwa ta kuma cewa" yayah toh ni mai yasa kak'i ka kaini inda mummy tace ka kaini d'in?"
" Banyi ra'ayi bane"
ya bata amsa a takaice.
Tura b aki tayi gaba sannan tace " amma yayah k'awata ce fah ita seat mate d'ina kuma"
" Kice mata ni na hana ki zuwa"
Ya bata amsa lokacin dayake k'ok'arin tada mota.
" Dan Allah ni...........
Zata sake yin magana ya dakatar da ita da fad'in
" ya isheni please kimin shiru"
Dan dolenta tayi shiru bawai dan ta gama fad'ar abinda ke ranta ba.
Suna zuwa gida kuwa tafice daga motar da gudu tayi ciki.
Kamar anjeho ta ta fad'awa mummy ajiki tana k'ananun kuka kamar wata yarinya k'arama.
Mummyn ce tace wai nikam ke kullum bakya ganin kin k'ara girma ne Teemah?
Cikin shesh-sheka dajan magana tace..." mummy k'in kaini fah yayi ya dinga yawo dani acikin gari kamar nace masa inaso"
"dai-dai kenan maganin irinku kenan ai"
Mummyn tafad'a tare da murmushi kwance akan fuskarta.
" mummy ke kullum-kullum bazaki bi bayana ba sai shi ko?, Allah in Daddy ya dawo sai na fad'a masa nima "
tana gama fad'in hakan ta tashi tayi d'akinta da sauri amma sai dai me........ tana zuwa harta shiga tafara zuge zif d'in rigarta ai sai ta tuna da k'adangaren d'azun sai kuwa tafito da gudunta ta dawo parlourn dai-dai Abbas ma ya shigo sai ya ganta aguje
"ke lafiyarki kuwa?"
ya jefa mata tambaya da mamakin irin yanda ya gantan kamar an koro ta.
Bata kulashi ba har sai da taga kanta zaune akusa da mummyn ta kafin ta d'anji dama-dama.
Abbas d'inma k'ara sowa yayi ya zauna akan kujera yana ta kallonta so yakr yaji me yakuma korota, yarinya kamar mai ta6in hankali.
Mummyn nata ne tasake tambayarta the same abinda Abbas d'in ya tambaya, sai a sannan tace " mummy k'adangare a d'akin fa kin manta?"
"Hmm"kawai Abbas yace kuma sai a sannan ya ajiye ledojin dake rik'e a hannunsa.
Mummy kuwa masifa tafara yimata inda tace
" banason hauka ni kinga Teemah, kadangaren da aka fitar tun d'azun shine kike wannan uban gudun akansa?"
"Waye ya fitar dashi toh?
Teemah ta sake tambayar mummyn.
Mummyn ma amsa ta sake bata da fad'in " yayanki mana"
Sai ta zaro idonta waje tare da fad'in " yah mahmud ya dawo ne dama"?.
Dank'walinta mummy tayi dan tasan dagangan tayi tambayar sannan tace "bafa nason iskanci ya dawo d'in ne kuma bazaki ganshi ba, koshi kad'ai ne akace yayanki?"
'Kasa tayi da kanta sai ta jiyo muryar Abbas yana fad'in " zo ki kwashe kayan nan anan" yafad'i tare da nuna mata ledojin daya shigo dasu d'azu a hannunsa.
Dayake atsare yayi maganar sai bata wani yi iyayi ba taje ta tsugunna ta kwashe ledojin ta mik'e tsaye sannan ta kalli inda yake d'in sai suka had'a idanu, sai da ta kauda kanta kafin tace "ina zan kai kayan"
Kallonta ya tsaya yi aransa yana mamakin yanda yarinyar nan ta gama raina shi gaba d'aya ya kuma rasa dalili.
Dayake baiyi magana ba sai tayi zaton ko baiji tambayar data masan bane sai ta sake maimaitawa a karo nabiyu.
Baiyi niyar bata amsa ba dan gani yake kamar iskanci ne ke damunta baya ga haka ai tasan dai ita yayiwa siyayyar tunda da ita suka je, darajar mummy dake gurin a zaune ne yasa shi bata amsa da " naki ne "
(nikuwa nace oga Abbas d'in mar-yerm sai a hankali, in ba haka waya san meke cikin zuciyarka da har kake tunanin Teemah tasan cewa siyayyan ta ne kayi).😅
Tana jin haka sai ta fara tafiya batare da ta kuma cewa k'ala ba.
Haushi mummy taji da wautar Teemahn sai kawai ta k'irata amsaw tayi kafin ta dawo da baya " baki da hankali ne Teemah?,bazaki iya bud'an bakinki kiyi godiya ba bayan mutun ya miki kyauta, bakinki ciwo yake yine? ko kuma iskanci da rashin hankalin kinne yayi k'wari"
" Kiyi hak'uri mummy daman inada niyyar yi "
Teeman tafad'a da kwa6a66an fuska
mummy kuwa tsaki kawai taja ta kauda kanta gefe dan halin Teemah gaba d'aya yafara isanta.
Ita kuwa sai ta juya ta kallo inda yake kamar baya wurin kansa na k'asa fuskarsa na kallon wayarsa dake rik'e a hannunsa sai tace " nagode yayah"
Ko ya nuna yasan ma da shi take bai nuna ba balle tasa ran yajita, sai ta k'ara maimaitawa ai kuwa sai taga ya d'aga waya yasa a kunnensa yafara magana cikin natsuwa kamar bashiba, jitayi ya matuk'ar birgeta ashe daman yana magana haka anatse, tsabar yanda ta tsaya kallonsa har abinda ke rik'e da hannun damanta ya fara zamewa, taroshi tayi da wuri ta daidaita rik'on ledan sannan ta d'an juyo ta kalli mummy da k'asan ido gani tayi mummyn na hararar ta.
Sai kawai tace " mummy kinga yak'i ya kulani ko "
"Toh tsoronki yake jine Teemah da godiya ma sai an saki kafin kimasa"
sai Teemahn tace " "toh ai shine mummy"
"Shine me?
Mummyn ta sake tambayarta.
Amma kafin Teemahn tasake magana sai mummyn ta kuma cewa " jeki ajiye kayan sai ki dawo kima sa godiyan kafin nan yagama wayar ma ".
Tanajin haka sai ta juya da farin ciki a zuciyarta har tana ayyana babu wanda zai sake ganin ta ma ayau kam, dan batayi niyyar yiwa mutun godiya ba ita kam tunda bata rok'i kaya agun mutun ba.
Amma sai dai me.........tana fara tafiya sai ta tuno da abinda ke d'akinta.
Sai ta fasa shiga kawai ta nufi hanyar d'akin mummy
" Karki kuskura kishigan min d'aki "
Muryar mummy tajiyo tana fad'in haka.
Kwafa tayi sannan ta karkata kanta gefe " ayyah mummy toh ina zan kai"?
" Baki da d'aki ne ke"?cewar mummyn. Teemah ma sai tasake fad'in
" mummy toh kizo ki rakani d'akin nawa "
" karkije inhar saina rakaki"
Dajin hakan tasan mummy ba rakata zatayi ba tunda tafad'i haka sai kawai ta nufi d'akin nata tsoro fal ranta.
Koda taje bakin d'akin ahankali ta tura k'ofar sai ta mimmik'a kayan hannun nata da sauri sannan ta kuma jan k'ofar ta rufe sai ta wuce kitchen tafita ta k'ofar baya tayi zamanta awaje.
Tana zaune awurin tanata sake-saken missing birthday da tayi kusan 15mins can sai ta ga Abbas ya fita amma ganin yana d'an sauri sai ta gane cewa masallaci zashi.
" Mthceeeeew" taja dogon tsaki tare da banka masa harara dan a duk sanda ta kalli Abbas d'in sake tunowa take da batun birthday d'in daya hanata zuwa "mugu kawai " ta k'ara fad'i afili..
(Ni kuwa nace kanki akeji y'an mata).😜
Bata tashi awurin ba sai da taga gari yad'an fara duhu kafin ta tashi ta zagaya ta shiga ta k'ofar parlour.
D'an zaman da tayi awajen sai ta manta da batun tsoron k'adangaren, dan haka tana shigowa sai ta wuce d'akinta saboda tana sauri taga tayi sallahr maghrib dan lokacin yad'an shige kad'an.
Haka yayi sayayyansa kaca-kaca sannan ya jagorancesu suka fito daga shagon suka kuma shiga mota.
Atunanin Teemah daga nan gurin partyn zasu wuce dan harta fara murna amma sai taga ya d'auki wani hanya daban haka yaita zaga cikin gari kamar me neman wani abu daga k'arshe sai ya nufi hanyar gida.
Teemah tayi ta masa magana yafi sau a k'irga amma ko kallon 6angaren da take ma baiyi ba ballantana ya kulata balle har tasamu amsar maganar da ta masa.
Sai da taga ya d'auki hanyar gidan kafin tasake masa magana akan batun birthday party d'in, duk da bata da tabbacin zai amsata amma sai da tayi dan tasan ko bai bata amsa ba ai dai ya ji ta.
Ga mamakinta kuwa sai taji yanzun ya bata takaitacciyar amsa da " bazaki ba" ya bata amsan ne batare da ko kallon kirki ba.
Ai tanajin haka sai ta fara bori da kuka dan harga ba k'aramin haushin fita da shi d'in nan tayi yau ba, data sani dama adaidaitan ta hau..........
data sani dama Habibu driver ne ya kaita.......
Data sani tayi shi yafi sau ak'irga.
Shikuwa koda yaga tana kukan sai bai kulata ba illah juya kan motar da yayi ya shiga u-turn ya dawo da baya,murna tafara daganin hakan atunaninta zai kai tan ne, dan daman wucewarsu unguwar su Leemah (birthday girl) kenan dataga bayada niyyar shiga shine tamasa magana dajin amasr daya bata kuwa sai tafara wannan iskancin kukan.
Ganin yasake wucewa sai kawai ta yi tagumi dan zuwa yanzun tagama sawa ranta tayi missing birthday d'in kenan har ma tanaji aranta cewar ya wuceta already.
Hanyar Jerusalem ward ya d'auka dake gefen nursing school, sai kuma tafara tunanin toh me suka zo yi anan kuma?
Kar dai wata yarinyar kuma ya kwaso acikin unguwar nan kuma?
Kauda kai tayi gefe tare da jan tsaki aranta ta kuma fad'in mutun sai kwashe-kwashen tsiya har arn......ma bai bari ba.
YETIM care foundation (gidan marayu) taga yayi parking awurin ya fito sai da tayi kalle-kalle kafin ita ma tafito tabiyo bayansa suka shiga ciki.
Sun tarar ma ana wani programme sai basu wani dad'e ba suka fito bayan ya gaiggaisa da mutanen wurin akan sai gobe insha Allahu zai dawo.
Mota suka koma yaja ya nufi hanyar gida.
Yanzun kam da suka fito bata wani tsaya mamaki ba bud'e bakinta tayi ta tambayeshi muryarta wasai tace" yayah yaushe kasan nan wurin?
Sai da ya kalleta kafin yace "Mahmud ne ya kawo ni nima kwanaki"
"Sai ta sake cewa " toh shi yah Mahmud d'in wa ya nuna masa ai naga shima bai san nan garin ba akace"?
"Toh sai ki jira idan yazo ki masa wannan tambayar?
Yayi maganan ne fuskarsa ba yabo ba fallasa sai ta d'an ji dad'in hakan hartaji tasamu k'arfin gwiwar sake yi masa magana, aikuwa ta kuma cewa" yayah toh ni mai yasa kak'i ka kaini inda mummy tace ka kaini d'in?"
" Banyi ra'ayi bane"
ya bata amsa a takaice.
Tura b aki tayi gaba sannan tace " amma yayah k'awata ce fah ita seat mate d'ina kuma"
" Kice mata ni na hana ki zuwa"
Ya bata amsa lokacin dayake k'ok'arin tada mota.
" Dan Allah ni...........
Zata sake yin magana ya dakatar da ita da fad'in
" ya isheni please kimin shiru"
Dan dolenta tayi shiru bawai dan ta gama fad'ar abinda ke ranta ba.
Suna zuwa gida kuwa tafice daga motar da gudu tayi ciki.
Kamar anjeho ta ta fad'awa mummy ajiki tana k'ananun kuka kamar wata yarinya k'arama.
Mummyn ce tace wai nikam ke kullum bakya ganin kin k'ara girma ne Teemah?
Cikin shesh-sheka dajan magana tace..." mummy k'in kaini fah yayi ya dinga yawo dani acikin gari kamar nace masa inaso"
"dai-dai kenan maganin irinku kenan ai"
Mummyn tafad'a tare da murmushi kwance akan fuskarta.
" mummy ke kullum-kullum bazaki bi bayana ba sai shi ko?, Allah in Daddy ya dawo sai na fad'a masa nima "
tana gama fad'in hakan ta tashi tayi d'akinta da sauri amma sai dai me........ tana zuwa harta shiga tafara zuge zif d'in rigarta ai sai ta tuna da k'adangaren d'azun sai kuwa tafito da gudunta ta dawo parlourn dai-dai Abbas ma ya shigo sai ya ganta aguje
"ke lafiyarki kuwa?"
ya jefa mata tambaya da mamakin irin yanda ya gantan kamar an koro ta.
Bata kulashi ba har sai da taga kanta zaune akusa da mummyn ta kafin ta d'anji dama-dama.
Abbas d'inma k'ara sowa yayi ya zauna akan kujera yana ta kallonta so yakr yaji me yakuma korota, yarinya kamar mai ta6in hankali.
Mummyn nata ne tasake tambayarta the same abinda Abbas d'in ya tambaya, sai a sannan tace " mummy k'adangare a d'akin fa kin manta?"
"Hmm"kawai Abbas yace kuma sai a sannan ya ajiye ledojin dake rik'e a hannunsa.
Mummy kuwa masifa tafara yimata inda tace
" banason hauka ni kinga Teemah, kadangaren da aka fitar tun d'azun shine kike wannan uban gudun akansa?"
"Waye ya fitar dashi toh?
Teemah ta sake tambayar mummyn.
Mummyn ma amsa ta sake bata da fad'in " yayanki mana"
Sai ta zaro idonta waje tare da fad'in " yah mahmud ya dawo ne dama"?.
Dank'walinta mummy tayi dan tasan dagangan tayi tambayar sannan tace "bafa nason iskanci ya dawo d'in ne kuma bazaki ganshi ba, koshi kad'ai ne akace yayanki?"
'Kasa tayi da kanta sai ta jiyo muryar Abbas yana fad'in " zo ki kwashe kayan nan anan" yafad'i tare da nuna mata ledojin daya shigo dasu d'azu a hannunsa.
Dayake atsare yayi maganar sai bata wani yi iyayi ba taje ta tsugunna ta kwashe ledojin ta mik'e tsaye sannan ta kalli inda yake d'in sai suka had'a idanu, sai da ta kauda kanta kafin tace "ina zan kai kayan"
Kallonta ya tsaya yi aransa yana mamakin yanda yarinyar nan ta gama raina shi gaba d'aya ya kuma rasa dalili.
Dayake baiyi magana ba sai tayi zaton ko baiji tambayar data masan bane sai ta sake maimaitawa a karo nabiyu.
Baiyi niyar bata amsa ba dan gani yake kamar iskanci ne ke damunta baya ga haka ai tasan dai ita yayiwa siyayyar tunda da ita suka je, darajar mummy dake gurin a zaune ne yasa shi bata amsa da " naki ne "
(nikuwa nace oga Abbas d'in mar-yerm sai a hankali, in ba haka waya san meke cikin zuciyarka da har kake tunanin Teemah tasan cewa siyayyan ta ne kayi).😅
Tana jin haka sai ta fara tafiya batare da ta kuma cewa k'ala ba.
Haushi mummy taji da wautar Teemahn sai kawai ta k'irata amsaw tayi kafin ta dawo da baya " baki da hankali ne Teemah?,bazaki iya bud'an bakinki kiyi godiya ba bayan mutun ya miki kyauta, bakinki ciwo yake yine? ko kuma iskanci da rashin hankalin kinne yayi k'wari"
" Kiyi hak'uri mummy daman inada niyyar yi "
Teeman tafad'a da kwa6a66an fuska
mummy kuwa tsaki kawai taja ta kauda kanta gefe dan halin Teemah gaba d'aya yafara isanta.
Ita kuwa sai ta juya ta kallo inda yake kamar baya wurin kansa na k'asa fuskarsa na kallon wayarsa dake rik'e a hannunsa sai tace " nagode yayah"
Ko ya nuna yasan ma da shi take bai nuna ba balle tasa ran yajita, sai ta k'ara maimaitawa ai kuwa sai taga ya d'aga waya yasa a kunnensa yafara magana cikin natsuwa kamar bashiba, jitayi ya matuk'ar birgeta ashe daman yana magana haka anatse, tsabar yanda ta tsaya kallonsa har abinda ke rik'e da hannun damanta ya fara zamewa, taroshi tayi da wuri ta daidaita rik'on ledan sannan ta d'an juyo ta kalli mummy da k'asan ido gani tayi mummyn na hararar ta.
Sai kawai tace " mummy kinga yak'i ya kulani ko "
"Toh tsoronki yake jine Teemah da godiya ma sai an saki kafin kimasa"
sai Teemahn tace " "toh ai shine mummy"
"Shine me?
Mummyn ta sake tambayarta.
Amma kafin Teemahn tasake magana sai mummyn ta kuma cewa " jeki ajiye kayan sai ki dawo kima sa godiyan kafin nan yagama wayar ma ".
Tanajin haka sai ta juya da farin ciki a zuciyarta har tana ayyana babu wanda zai sake ganin ta ma ayau kam, dan batayi niyyar yiwa mutun godiya ba ita kam tunda bata rok'i kaya agun mutun ba.
Amma sai dai me.........tana fara tafiya sai ta tuno da abinda ke d'akinta.
Sai ta fasa shiga kawai ta nufi hanyar d'akin mummy
" Karki kuskura kishigan min d'aki "
Muryar mummy tajiyo tana fad'in haka.
Kwafa tayi sannan ta karkata kanta gefe " ayyah mummy toh ina zan kai"?
" Baki da d'aki ne ke"?cewar mummyn. Teemah ma sai tasake fad'in
" mummy toh kizo ki rakani d'akin nawa "
" karkije inhar saina rakaki"
Dajin hakan tasan mummy ba rakata zatayi ba tunda tafad'i haka sai kawai ta nufi d'akin nata tsoro fal ranta.
Koda taje bakin d'akin ahankali ta tura k'ofar sai ta mimmik'a kayan hannun nata da sauri sannan ta kuma jan k'ofar ta rufe sai ta wuce kitchen tafita ta k'ofar baya tayi zamanta awaje.
Tana zaune awurin tanata sake-saken missing birthday da tayi kusan 15mins can sai ta ga Abbas ya fita amma ganin yana d'an sauri sai ta gane cewa masallaci zashi.
" Mthceeeeew" taja dogon tsaki tare da banka masa harara dan a duk sanda ta kalli Abbas d'in sake tunowa take da batun birthday d'in daya hanata zuwa "mugu kawai " ta k'ara fad'i afili..
(Ni kuwa nace kanki akeji y'an mata).😜
Bata tashi awurin ba sai da taga gari yad'an fara duhu kafin ta tashi ta zagaya ta shiga ta k'ofar parlour.
D'an zaman da tayi awajen sai ta manta da batun tsoron k'adangaren, dan haka tana shigowa sai ta wuce d'akinta saboda tana sauri taga tayi sallahr maghrib dan lokacin yad'an shige kad'an.