← Book details Captain Abbas Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 78 OF 163

Sashe 78

Captain Abbas Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Farin cikin Teemah yau baya 6oyuwa yanda taji muryar iyayen nata ita ka'dai sai tana sakin murmushi musamman idan ta tuna cewa daddy zai zo nextweek sai take ganin kamar matsalarta ta kusan zuwa karshe, dan tagama sawa ranta cewar daddy na zuwa zata ma'kale masa sai ya tafi da ita ko dan ta huta da fitinar su Anty ma.

Sosai take jin farin ciki wanda hakan yagama bayyana kansa azahiri kowa ya kalleta take zai gane hakan, sai de deepdown her heart tana jin zuciyarta ajagule kamar bata da nutsuwa, da 'kyar tasamu ta lalu6o damuwar tata da dare bayan ta kwanta bacci alokacin ta zurfafa tunanin ta sai data gano 6oyayyiyar damuwar tata.

Lumshe idanu tayi take tausayin sa ya tsarga mata azuci ta ringa tuno rayuwar su dashi abaya abu na 'karshe data tuno shine ranar da za'a 'daura auren ta da Mahmud daya zo yabata gift har cikin 'dakinta.

Tsintar kanta tayi da tausaya wa rayuwarsu shida ita take ta tashi tayo alwala tazo ta tada sallah bayan ta sallame ta ringa jero addu'o'i na nema musu kariya wurin mahallici, musamman ma shi da yake fama da 'yan ta addah.

Mahmud kuwa sosai ya samu tarba wurin shehin malami kakan Umar abokinsa, yayi masa tambayoyi akan abubuwan da ke faruwa dashi, Mahmud duk yayi masa bayani.

Sosai ya jinajina wa al'amarin tare da sanar da Mahmud 'din cewa matsalarsa ba abin damuwa bace matu'kar za'a yi anfani da abinda 'qur'ani ya karantar, yace matsalar sa bakomai bace face matsalar aljanu amma da iznin Allah komai zai daidaita.

Atake yabashi wani ruwan addu'a ha'de da ganyen magarya yace yayi bismillah yasha ya kuma wanke fuskarsa.

Hakan Mahmud yayi kamar yanda malamin ya umarce sa da yi daga nan yabashi wasu addu'o'i yace ya ringa yi akoda yaushe sannan ya yaiwata yin istighfari, sadaka da neman yardar Allah akowani lokaci.

Washegari malamin ya ha'dawa Mahmud magunguna na islamic medicine tare da bashi wata jarka da ke chike da ruwan rubutu yayi masa bayanin yanda zai na anfani dasu.

Sosai Mahmud yaji da'din al'amarin harma yarasa da me zai sakawa malamin, banki ya tafi yaje ya chiro ku'di kusan 200 thousand naira ya kawo yabashi, amma fir ya'ki kar6a, sunyi-sunyi ya kar6a ya'ki Mahmud kamar ze yi kuka domin gani yayi kamar in be kar6a ba tamkar wani nauyi ne akansa.

Dayaga sun dage ne shine ya kar6i twenty thousand yace ya isa Allah ya sa adace yakuma bada sa'a, yace da Mahmud 'din shi bashi da matsala da ku'di amma ze iya ya bayar da sadakan ku'din ga koma wanene inyaga me shi nada bu'kata.

Godiyar Mahmud kamar su yi wa malamin rumfah suka masa sallama suka fito da niyyar tafiya.

Taxi suka tara suka hau tun acikin unguwa suka samu, dayake cikin unguwa ne sai suke tafiyar ahankali.

Wani gida suka wuce daf da zasu fita a unguwar ginin 'kasa duk ya lalace ma katangar gidan ruwa duk ya wanketa ta dawo yar guntuwa har kana hango abinda ke faruwa acikin gidan, 'kofar gidan ma da wani tsohon buhu aka tare shi daga shi kuwa babu komai.

Acikin 'yan sakanni Mahmud ya gama karanto fasalin gidan, take kuwa zuciyarsa ta karye, tausayin wahalar da al'ummah suke ciki duk yabi ya cika masa zuciya.

Gaba ka'dan sai yaga wata yarinya da bazata wuche 10-11yrs ba, kayan jikinta kuwa ko goge takalmansa aka ce za'a yi dasu sai ya hana ayi balle har su kasance ajikin mutun, tsabar yanda ko'diya da datti suka cikasu ko gane zanen zanin da kyau ma ba'a yi.

Dur'kushe take tana kwasan wani farin abu a'kasa hankalinta duk yabi ya tashi tana yi tana waiwaye ga dukkan alamu bada sanin ta ba ya kuskure ya zube.

Mahmud dakatar da drivern taxi 'din yayi bayan sun wuce yarinyar ka'dan, amma kafin Mahmud ya yi yun'kurin fitowa har wata mata ta fito ta iso inda yarinyar take tsugunne tana masifa itama ta tsugunna tana tayata kwasan abun.

Ahankali ya tako ya iso kusa dasu basu ma lura dashi ba hakan yasa wannan matar bata dakata da masifar datake yi ba amma ba da hayaniya takeyi ba tanayi ne yanda yarinyar ka'dai zata jita sai ko Mahmud daya musu la6e.

Jiyayi matar na fa'din " _yanzu fisabilillahi meram bazaki dinga kulawa ba, akullum_ _magana 'daya kike son inyita maimaita miki?, ke ko duba yanayin da aka samu 'dan_ _ku'din nan bakiyi kika zo kika zubar da alabon nan yanzu dan Allah a_ _ina kike so mu shiga mu samu ku'din da za'a siyi wani ga yara duk yunwa tabi ta ishesu,_ _badan albarkacin surfen nan da matar yakubu takawo_ _bama da yau Allah ne ka'dai yasan yanda zamu kasance, kuma muna murna zamu_ _samu abin ta6awa sai kizo kuma ki zubar?_

Ahankali Mahmud ya 'karaso kusa da su tsabar yanda yaji tausayinsu har idanunsa na tsatstsafo da ruwan hawaye amma be bari sun sau'ko ba kawai ya dinga fa'din _Alhamdulillah_ azuciyarsa da rufin asirin da Allah yayi musu, ha'ki'ka rayuwar bin Adama ma aya ce babba, yanda damuwoyin junanmu suka bambanta kowa da kalar tashi damuwar, kamar shi yanzu yanda Allah ya rufa masa asiri takowani 6angare bashida matsala da komai sai kawai ya jarabce shi da dakushewar wani sassa na jikinsa wanda hakan ya matu'kar 'daga masa hankali, balle wa'dannan, ya zasuji da damuwar su takasance akan rayuwa ce gaba 'dayanta, ha'ki'ka Allah buwayi ne gagara misali domin shine yayi al'kawrin jarabtar kowa daga cikin mutane harma da ajannu da kowani irin al'amari, sai de fatan Allah ya sassauta mana ya kuma bamu ikon cin jarabawar.

Adaidai lokacin ya iso kansu ya tsaya sai yaga sun ma gama kwashewa sauran wanda ya gaurayu da 'kasan ne suke sake kwasa.

_Comments Vote and share_

*Salmerhn ku ce*😍
[10/2, 6:02 PM] Ummiyo: 💕 *CAPTAIN ABBAS* 💕

By
*Salmerh MD*

Luv story😍

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

*Bismillahir rahmanir raheem*

_Before you go pointing your fingers at someone else, you may want to make sure your own hands are_ _clean............_

🅿 *62*

Da sauri yace " _ah ah Innah wannan ai 'kasa ce ta rage_ "

Bata 'dago taga me yi mata maganan ta bashi amsa da fa'din " ' _kyaleni yaro, inban kwashe duka ba 'dan waken ba isan yaran zaiyi ba hakan ma daya za'a ci ballantana kuma ya gaza haka_ "

Mahmud cikin tsananin mamaki yace
" _wai kina nufin wannan abin abinci za'ayi da shi Innah_ ?

Sai wannan karan matar ta dakata da kwasan abin da takeyi ta 'dago jin tambayar yayi matan kamar ta rainin hankali.

Tana mi'kewa taganshi tsaye kusa da ita ga wasu su biyu ma tsaye abayansa, ita tsoro ma ya bata dan yanda taganshin take tsoro ya tsarga mata azuci.

Hannun 'yarta takama tayi baya ka'dan sannan tajuya suka nufi gidansu da saurin gaske.

Wannan gidan da Mahmud yagani 'dazu nan yaga suka shiga shima sai ya biyo su abaya amma kafinma ya iso su har sun shige ciki abinsu.

Tsayawa sukayi suna 'dan dube-dube can suka hango wani matashin saurayi da bazai wuce shekara 20 ba yana kallon su daga 'dan nesa ka'dan.

Hannu Mahmud ya masa sai kuwa ya taho da sauri kamar dama jira yake su 'kira shi.

Yana iso wa ya gaida su suka amsa sannan Mahmud ya tambayi sunansa .

Matashin yace sunan sa _Rabi'u_ .

Mahmud ne yace " _yauwa Rabi'u dan Allah ko zaka mana magana da mai gidan nan_ "

Matashin mai suna Rabi'u yace " _Allah sarki ai maigidan ya kwan biyu da rasuwa, matarsa da 'ya'yansa ne ka'dai_ _suka rayuwa_ _agidan_ "

Tausayin mutanen ne ya sake shiga dukkanin azuciyoyin su har drivern taxi 'din.

Bayani Mahmud yayi wa Rabi'u akan abinda ke tafe dasu, nan take kuwa farin ciki ya baibaye ilahirin fuskar Rabi'u yafara yi musu godiya tunma be tabbatar da gaskiyar lamarin ba, shiga gidan Rabi'u yayi yai wa matar gidan bayani wanda da 'kyar ta amince da batun da Rabi'un yazo mata dashi, domin ita rayuwar yanzu tsoro yake bata, mutane sam babu tsoron Allah azu'katansu, dayawansu basa taimako saboda Allah sai dan su cuceka ko dan wani abu daban, ita kuwa da take ta fama tana lalla6a rayuwarta da 'yan yaranta guda hu'du sam bata son wata sabuwar fitina ta 6ullo musu.

Da 'kyar Rabi'u ya shawo kanta ta yadda ta amince da su Mahmud 'din sannan Rabi'u yakoma yayi musu iso.

Su Mahmud basu tsinke da al'amarin matar ba har sai da suka sanya kawunansu acikin gidan, inda suka ga komai kamar ba inda 'dan adam ke rayuwa ba, babu komai da zai birge mutun acikin gidan face tarkace da tsummokara, Mahmud sosai ya tausaya musu jikinsa yayi sanyi 'kalau.

Rabi'u ne da kansa ya je ya janyo wata ru6a66iyar tabarma ya shinfi'da musu suka zauna akai, ganin yanayin matar ne yasa Umar yayi mata bayani abayyane cewa ta saki jikinta karta ji tsoro sadaka suka kawo musu ba cutar da su zasu yi ba, amma intaga kamar bata yadda dasu ba har yanzun tana iya yi musu bayani sai sukoma inda suka fito.

Rabi'u ne yayi saurin taran maganar da fa'din " _ah ah ai baza 'ayi haka ba nariga nayi mata bayani 'dazun ai kuma ta fahimta_ "

Mahmud kam shiru yayi yana sauraransu yariga da yasawa ransa cewa ze taimaka musu cikin abinda Allah ya hore masa, so ko matar nan zata na dukansa tana koransa ne ba ze fasa ba.

Ku'di masu yawa Mahmud yaciro ya mi'kawa Umar shikuma ya bawa Rabi'u yace ya nemo masu gyara su 'dan 'kara tsayin katangar gidan saboda rufin asirin masu gidan, sannan yaciro wannan ku'din da malam ya'ki kar6a ya mi'kawa matar yace wannan sadaka ce taringa siyawa yaran abinci me kyau suna ci ba irin wannan ba, sannan kuma ta na siya musu omo da sabulu sunayin wanki akan lokaci, yace karta damu da 'karewar ku'din insha Allahu ze dawo ba da'dewa ba ya sake dubasu.
Chapter 78 · 0% Book details