Sashe 56
Baqeer Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Ɗakinta ta koma tana share hawaye, tunaninta ɗaya yanzu idan yaran suka dawo daga makaranta me zata basu? Ɗakin kawai take bi da kallo tana tunanin ita yanzu ba wani abu gareta ba bare ta ɗaga ta sayar ta samu abinda zasu ci abinci, idanunta ne suka kai kan wata tshowar akwatin garwa ta maigidan da ta daɗe a ajiye a ɗakin nata, ba komai yake yi da ita ba sai haɗa ƙura don haka ta tashi ta janyota ta karkaɗe ƙurar kai tasa hijabinta ta sunkuci akwatin ta fice ta kaiwa ƴan gwangwan, ko ɗari biyar suka bata ai dai ta isheta ta samar musu da abinda zasu ji, da kallo kishiyarta ta bita tana ayyana lallai yau akwai bala'i a gidan don kuwa tasan ba ƙaramin ɓaci rayuka zasu yi ba akan wannan matacciyar akwatin.
*****
Tunda suka bar gidan babu wanda yayi magana har sai da suka hau titi sosai suka yi nisa da unguwar ta mariri. "Who is he to you?" Ya tambayeta. Waiwayowa tayi ta kalleshi tace "na'am J, magana kake yi?" Ƙara maimaita tambayar yayi yace "Who is he to you? naga kin damu sosai da al'amuranshi". Shiru tayi ta kasa amsa mishi don sai ta samu kanta itama da yiwa kanta makamanciyar tambayar da yayi mata "waye shi a wajenta? Akwai wata dangantaka ne a tsakaninsu bayan kasancewar shi yaya ga ƙawarta Maryam?" Kasa bawa kanta amsa tayi don haka tayi shiru bata amsa Junaid ɗin ba, shima sai bai ƙara tambayarta ba jin tayi shiru sai dai yana jin fargaba akan abinda zuciyarshi ke neman saƙa mishi sai dai kuma idan ya tuna wacece Zeey ɗin da yadda take kallon maza ƴaƴan manya masu ji da kyau da class a ba komai ba sai ya samu ƴar nutsuwa kaɗan don yasan babu abinda zata yi da gurgu sai dai kuma tambayarshi anan itace waye shi a wajen Zeey ɗin data damu dashi da yawa har haka?
Har suka ƙarasa gidansu babu wata hira a tsakaninsu kowa da abinda yake saƙawa a cikin zuciyarshi, sai da zai sauka nema tace mishi "nagode sosai J, please ka gaishe mini da Mami kace ina sauri ne shi yasa ban shigo na gaisheta ba amma takanas zan zo na gaisheta, sai kuma batun payment ɗinka ban ji kace komai ba". Harararta yayi yace "ai bakin ki ne payment ɗin" ya mayar da ƙofar motar ya rufe ya wuce ba tare da ko waiwayowa yayi ba. Bin bayanshi tayi da kallo har ya shige cikin gidansu sannan taja motarta ta bar wurin cikin ranta tana jin ina ma zata iya mayar mishi da martanin soyayyar da yake yi mata don tasan J yana sonta shi yasa yake ɗaukar duk wasu al'alarta sai dai kuma ba zata iya ba don ba wani girmarta yayi ba beside that bata jin shi har ƙasan ranta a matsayin wanda zata iya spending the rest of her life with. Girgiza kanta tayi kawai ta kawar da wannan tunanin daga ranta, haka nan ta samu kanta da yawatawa akan titi don bata ji tana son komawa gidan Inna ba taje suyi ta faɗa tana sakar mata baƙaƙen maganganu don ma dai tana kawarwa tana mayar da abun wasa amma abun yana yi mata ciwo yadda Inna take treating ɗinta sam baya yi mata daɗi. Sai can goshin magriba ta gaji da yawon a titi ta ɗauki hanyar da zata sadata da gidan Inna tana jin koma zuwa zata yi ta tattara kayanta ta koma gida ne.
*****
Shi kuwa Bello ganin da yayi iyayen shi sun ƙi su goya mishi baya aje gidansu Asiya a nema mishi aurenta daya ɗauki dukkanin buri ya ɗaura akai yasa shi niƙar gari ya tafi garin Rano inda Baffanshi babban yayan mahaifin shi yake da zama ya kai mishi ƙarar su Baban akan ya samu yarinya har sun daidaita kansu amma su Baba sun ce ba zai aureta ba. Nan fa Baffan ya rufe ido yayi ta faɗa yana cewa "don me yaro ya girma ya kai munzalin ajiye iyali zasu ce ba zai yi aure ba, to shi ba zai lamunci wannan ba dole aje a nema mishi auren tunda dai ya nuna buƙatar hakan kuma yana da abinda zai riƙe matar dashi". Haka nan Bello ya ɗauke shi a sabuwar motarshi daya saya don ba ƙaramin alheri ya samu ba a gasar nan da yaje suka tafi Kano. Duk yadda Baban Bello yaso yayi wa ɗan uwanshi bayanin dalilin da yasa suka ce Bello ba zai auri Asiya ba ya toshe kunne yaƙi karɓar uzurin su don kafin tahowarsu sai da Bello ya jiƙa shi da kuɗi don haka yace tunda dai yaji ya gani kuma yana da abinda zai riƙe matar to su ƙyale shi ya aureta, haka nan dai ba don su Baban sun so ba aka je gidansu Asiya aka nema mishi aurenta, shi kanshi Babanta da yaga iyayen Bello ne suka zo neman auren nata sai da yaji mamaki don yasan dai Bello abokin Baqeer ne asalin manemin auren ƴar tashi sai kuma yanzu iyayenshi suzo da wani zance na daban kuma don haka ya dakatar dasu sai da ya shiga gida ya kira Asiya ya tambayeta da saninta iyayen Bello suka zo neman aurenta? Babu kunya Asiya ta amsa mishi da eh, "to ina maganar Baqeer ta kwana da zaki sa abokinshi a nema mishi auren ki?" Sai cewa tayi "Baba Baqeer fa ya zama gurgu ta yaya za'a yi na aureshi?"
Ɗan jim yayi kafin yace "ai shikenan tunda Bellon kika zaɓa, kin dai tabbatar kina son shi ko?" Ɗaga kai tayi alamun amsawa tana murmushin farin cikin ganin Baban bai bata wata matsala ba ya amince, sai Innarta ce tace "amma Mallam sai ka biye mata bayan kasan yaron nan Baqeer yayi wahala da ita ba kuma shi yace ya fasa ba sai ita da taƙi shi saboda kawai Allah ya jarabce shi da larura". Sai ce mata yayi "to in banda abunki shi da ya nakasa yanzu wane batun aure zai yi? Ai sai a bawa mai lafiya dama tunda kuma Allah ya kawo mijin ai ba zamu ƙi aurar da ita ba saboda wani dalili can". "Haka ne" kawai tace ba don ta gamsu da bayanin da yayin ba. Haka nan ya koma wajen iyayen Bello ya karɓi kuɗin aurensu nan dai aka tsayar da magana aka sa rana watanni uku masu zuwa. To sai muce Allah ya tabbatar da alkhairi....
*ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU*.
*BAQEER*
Ayusher Muhd
Umm Asghar
*KURMAN ALLO*
Asmy b Aliyu
Jidda Aliyu
*AKWAI SIRRI*
Zee Bawa
Hajja ce
*MUTALLAB ASAD*
Nana Diso
Billy S Fari
*KULUWA*
Zee yabour
Sadiya Dan
Duka Biyar ɗin akan 2k
Hudu 1600
Uku 1200
Biyu 800
Ɗaya 500
VIP💕🔥
Duk guda ɗaya 1k
NORMAL GROUP 500
VIP 1000
ACCOUNT NUMBER
0020428430
Ishaq Fatima A. Gtb
Or
8098456130
Fatima Ishaq
Opay digital services
Shaidar biya
08098456130
KATIN MTN Ta👇
07043079282
Shaidar biya ta 07065283730
Ko a tuntubi
08086207764
0816 114 6563
+234 704 040 2435
+234 903 056 9336
*Umm Asghar Ce*
*Da*
*Ayusher Muhd*
*BAQEER*
*NA*
*AYUSHER MUHD*
*DA*
*UMM ASGHAR*
*RUBUTUN TAGWAYE SHAFI NA TALATIN DA BIYAR*
{35}
*****
Tunda suka bar gidan babu wanda yayi magana har sai da suka hau titi sosai suka yi nisa da unguwar ta mariri. "Who is he to you?" Ya tambayeta. Waiwayowa tayi ta kalleshi tace "na'am J, magana kake yi?" Ƙara maimaita tambayar yayi yace "Who is he to you? naga kin damu sosai da al'amuranshi". Shiru tayi ta kasa amsa mishi don sai ta samu kanta itama da yiwa kanta makamanciyar tambayar da yayi mata "waye shi a wajenta? Akwai wata dangantaka ne a tsakaninsu bayan kasancewar shi yaya ga ƙawarta Maryam?" Kasa bawa kanta amsa tayi don haka tayi shiru bata amsa Junaid ɗin ba, shima sai bai ƙara tambayarta ba jin tayi shiru sai dai yana jin fargaba akan abinda zuciyarshi ke neman saƙa mishi sai dai kuma idan ya tuna wacece Zeey ɗin da yadda take kallon maza ƴaƴan manya masu ji da kyau da class a ba komai ba sai ya samu ƴar nutsuwa kaɗan don yasan babu abinda zata yi da gurgu sai dai kuma tambayarshi anan itace waye shi a wajen Zeey ɗin data damu dashi da yawa har haka?
Har suka ƙarasa gidansu babu wata hira a tsakaninsu kowa da abinda yake saƙawa a cikin zuciyarshi, sai da zai sauka nema tace mishi "nagode sosai J, please ka gaishe mini da Mami kace ina sauri ne shi yasa ban shigo na gaisheta ba amma takanas zan zo na gaisheta, sai kuma batun payment ɗinka ban ji kace komai ba". Harararta yayi yace "ai bakin ki ne payment ɗin" ya mayar da ƙofar motar ya rufe ya wuce ba tare da ko waiwayowa yayi ba. Bin bayanshi tayi da kallo har ya shige cikin gidansu sannan taja motarta ta bar wurin cikin ranta tana jin ina ma zata iya mayar mishi da martanin soyayyar da yake yi mata don tasan J yana sonta shi yasa yake ɗaukar duk wasu al'alarta sai dai kuma ba zata iya ba don ba wani girmarta yayi ba beside that bata jin shi har ƙasan ranta a matsayin wanda zata iya spending the rest of her life with. Girgiza kanta tayi kawai ta kawar da wannan tunanin daga ranta, haka nan ta samu kanta da yawatawa akan titi don bata ji tana son komawa gidan Inna ba taje suyi ta faɗa tana sakar mata baƙaƙen maganganu don ma dai tana kawarwa tana mayar da abun wasa amma abun yana yi mata ciwo yadda Inna take treating ɗinta sam baya yi mata daɗi. Sai can goshin magriba ta gaji da yawon a titi ta ɗauki hanyar da zata sadata da gidan Inna tana jin koma zuwa zata yi ta tattara kayanta ta koma gida ne.
*****
Shi kuwa Bello ganin da yayi iyayen shi sun ƙi su goya mishi baya aje gidansu Asiya a nema mishi aurenta daya ɗauki dukkanin buri ya ɗaura akai yasa shi niƙar gari ya tafi garin Rano inda Baffanshi babban yayan mahaifin shi yake da zama ya kai mishi ƙarar su Baban akan ya samu yarinya har sun daidaita kansu amma su Baba sun ce ba zai aureta ba. Nan fa Baffan ya rufe ido yayi ta faɗa yana cewa "don me yaro ya girma ya kai munzalin ajiye iyali zasu ce ba zai yi aure ba, to shi ba zai lamunci wannan ba dole aje a nema mishi auren tunda dai ya nuna buƙatar hakan kuma yana da abinda zai riƙe matar dashi". Haka nan Bello ya ɗauke shi a sabuwar motarshi daya saya don ba ƙaramin alheri ya samu ba a gasar nan da yaje suka tafi Kano. Duk yadda Baban Bello yaso yayi wa ɗan uwanshi bayanin dalilin da yasa suka ce Bello ba zai auri Asiya ba ya toshe kunne yaƙi karɓar uzurin su don kafin tahowarsu sai da Bello ya jiƙa shi da kuɗi don haka yace tunda dai yaji ya gani kuma yana da abinda zai riƙe matar to su ƙyale shi ya aureta, haka nan dai ba don su Baban sun so ba aka je gidansu Asiya aka nema mishi aurenta, shi kanshi Babanta da yaga iyayen Bello ne suka zo neman auren nata sai da yaji mamaki don yasan dai Bello abokin Baqeer ne asalin manemin auren ƴar tashi sai kuma yanzu iyayenshi suzo da wani zance na daban kuma don haka ya dakatar dasu sai da ya shiga gida ya kira Asiya ya tambayeta da saninta iyayen Bello suka zo neman aurenta? Babu kunya Asiya ta amsa mishi da eh, "to ina maganar Baqeer ta kwana da zaki sa abokinshi a nema mishi auren ki?" Sai cewa tayi "Baba Baqeer fa ya zama gurgu ta yaya za'a yi na aureshi?"
Ɗan jim yayi kafin yace "ai shikenan tunda Bellon kika zaɓa, kin dai tabbatar kina son shi ko?" Ɗaga kai tayi alamun amsawa tana murmushin farin cikin ganin Baban bai bata wata matsala ba ya amince, sai Innarta ce tace "amma Mallam sai ka biye mata bayan kasan yaron nan Baqeer yayi wahala da ita ba kuma shi yace ya fasa ba sai ita da taƙi shi saboda kawai Allah ya jarabce shi da larura". Sai ce mata yayi "to in banda abunki shi da ya nakasa yanzu wane batun aure zai yi? Ai sai a bawa mai lafiya dama tunda kuma Allah ya kawo mijin ai ba zamu ƙi aurar da ita ba saboda wani dalili can". "Haka ne" kawai tace ba don ta gamsu da bayanin da yayin ba. Haka nan ya koma wajen iyayen Bello ya karɓi kuɗin aurensu nan dai aka tsayar da magana aka sa rana watanni uku masu zuwa. To sai muce Allah ya tabbatar da alkhairi....
*ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU*.
*BAQEER*
Ayusher Muhd
Umm Asghar
*KURMAN ALLO*
Asmy b Aliyu
Jidda Aliyu
*AKWAI SIRRI*
Zee Bawa
Hajja ce
*MUTALLAB ASAD*
Nana Diso
Billy S Fari
*KULUWA*
Zee yabour
Sadiya Dan
Duka Biyar ɗin akan 2k
Hudu 1600
Uku 1200
Biyu 800
Ɗaya 500
VIP💕🔥
Duk guda ɗaya 1k
NORMAL GROUP 500
VIP 1000
ACCOUNT NUMBER
0020428430
Ishaq Fatima A. Gtb
Or
8098456130
Fatima Ishaq
Opay digital services
Shaidar biya
08098456130
KATIN MTN Ta👇
07043079282
Shaidar biya ta 07065283730
Ko a tuntubi
08086207764
0816 114 6563
+234 704 040 2435
+234 903 056 9336
*Umm Asghar Ce*
*Da*
*Ayusher Muhd*
*BAQEER*
*NA*
*AYUSHER MUHD*
*DA*
*UMM ASGHAR*
*RUBUTUN TAGWAYE SHAFI NA TALATIN DA BIYAR*
{35}