Sashe 17
Baqeer Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da wani irin kallon takaici ya bita kafin yace "Kina cikin gidan nan don shashanci zaki dinga bari wancan lalataccen yaron yana zuwa yana ficewa dashi yawo salon mutanen unguwa su ganshi a keken guragu suyi min dariya, owo zane ne ba zai iya ba idan anyi magana kuce bai warke ba har yanzu hannunshi nayi mishi ciwo amma ya iya ficewa yawo har sai an nemeshi kafin ya dawo gida, ni dama nasan baƙin ciki kike yi mini shi yasa kika ƙi yarda ya koma aikinshi na zane, to ai ba ni kaɗai na rasa ba harda ke uwarshi tunda kafin yayi mini maganin naira goma ai yayi miki na ɗari, kuma na faɗa miki kada ki ƙara bari wancan yaron ya shigo mini cikin gida ya fita dashi yawo, tunda dai ba zai yi zane ba sai yayi ta zama a cikin gida amma na yanke hulɗa a tsakanin shi da shi."
Murmushi tayi mai ciwo ganin yadda maigidan nata ya ware murya yana yi musu tijara a tsakar gida kamar ba shine wannan uban dake ji da Baqeer yana lallaɓashi ba amma yanzu saboda ƙaddara ta sameshi shine na farko wajen juya mishi baya babu tausayi bare tausayawa halin da yake ciki shi dai damuwarshi kawai burinshi ne da ba zai cika ba. Sai da ta gyara tsayuwarta sannan tace "Amma Mallam idan ka hana Salim shigowa wajen Baqeer waye zai tallafa mishi wajen yin buƙatun da dole yana buƙatar mataimaki, kasan dai ni mace ce akwai larurar da dole sai namiji ɗan uwanshi ne zai taimaka mishi da ita kuma shi Salim ɗin da baka son ganinsu tare shi kaɗai ne yake tallafa mishi a irin waɗannan lokutan kaga kuwa ko don wannan ai baka rabasu ba tunda dai mu muke amfana dashi ba shi yake ƙaruwa damu ba."
Tsaki yayi cikin ranshi yana ganin kuma fa haka ne dole Baqeer ɗin yana buƙatar mataimaki gara ya bar Salim ɗin yaci gaba da kula dashi tunda dai yaji ya gani shi yasa kanshi ba wani ya saka shi ba don haka yace mata "Shikenan yana iya zuwa ko don kula dashi ɗin amma sai a kula da fita dashi waje don bana so."
Sai a sannan Baqeer ya ɗago kai ya kalli mahaifinshi yana tunanin dama haka yake ko kuwa wannan ƙaddarar data sameshi ce ta mayar dashi hakan, a tunaninshi ko kowa ya juya mishi baya banda mahaifin shi mi ji dashi mai tsanani so da ƙaunar farin cikin shi, sai dai kash mutanen duniya ba'a ci musu alwashi don baka sanin asalin kalarsu sai idan wata ƙaddara ta afka maka sannan suke bayyanar maka da asalin ɓoyayyiyar fuskarsu.
*****
#Baqeer🦼
#RayuwadaKaddara
#Hawayena
#Samudarashi
#UmmuAsgar
#Ayushermuhd
*ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU.
*BAQEER*
Ayusher Muhd
Umm Asghar
*KURMAN ALLO*
Asmy b Aliyu
Jidda Aliyu
*AKWAI SIRRI*
Zee Bawa
Hajja ce
*MUTALLAB ASAD*
Nana Diso
Billy S Fari
*KULUWA*
Zee yabour
Sadiya Dan
Duka Biyar ɗin akan 2k
Hudu 1600
Uku 1200
Biyu 800
Ɗaya 500
VIP💕🔥
Duk guda ɗaya 1k
NORMAL GROUP 500
VIP 1000
ACCOUNT NUMBER
0020428430
Ishaq Fatima A. Gtb
Or
8098456130
Fatima Ishaq
Opay digital services
Shaidar biya
08098456130
KATIN MTN Ta👇
07043079282
Shaidar biya ta 07065283730
Ko a tuntubi
08086207764
0816 114 6563
+234 704 040 2435
+234 903 056 9336
Umm Asghar Ce
Da
Ayusher Muhd
*BAQEER*
*NA*
*AYUSHER MUHD*
*DA*
*UMM ASGHAR*
*ƊANƊANO DAGA RUBUTUN TAGWAYE SHAFI NA GOMA SHA ƊAYA*
Da taimakon Umma Baqeer ya koma ɗakinshi. Abincin shi ta fita ta ɗauko sai dai ko kusa ya ƙi yarda ya sanya ko loma ɗaya a bakinshi don halin da ya tsinci kanshi a ciki yafi gaban ya iya sakawa cikin shi wani abu, haka tayi ta lallaɓa shi da ban haƙuri da nasiha akan ya daure yaci ko kaɗan ne amma ya kasa, haka nan ta haƙura ta ƙyaleshi ganin duk yadda tayi dashi ya ƙi karɓar abincin da take kaiwa bakinshi, sai da ta tabbatar baya buƙatar komai kafin tayi mishi sallama ta fita daga ɗakin taja mishi ƙofar ta rufe. Tana fita hawayen da yake ta riƙewa suka samu sararin zubowa, idanu ya kai kan ƙafafun shi da ko kaɗan baya jin alamun su a jikinshi, shi kenan shi yanzu haka zai yi ta zama ya nakasa ya zama musaki ba zai iya ƙara amfanawa kanshi komai ba sai dai ayi mishi. Sai ƙoƙarin ɗaga ƙafafuwan yake yi amma ya kasa, yayi-yayi ya motsa su ko yaya ne abu yaci tura. Hannunshi mai lafiyan yasa yayi ta dukan ƙafafun ko zai ji wani feeling nan ma babu abinda yake ji.
Wani irin ihu yasa yana cewa "Nooo..." haɗe da dukan ƙafafun da yake jin su tamkar ba a jikin shi suke ba da ƙarfi. Duk mutanen gidan babu wanda bai ji ihun da yake yi ba don haka duk suka firfito daga ɗakunansu suna kallon ƙofar ɗakin Baqeer ɗin sai dai babu wanda ya iya ƙarasawa ya duba halin da yake ciki. Kamalu ne yaja tsaki yace "Wannan hala bayan gurguncewar harda matsalar ƙwaƙwalwa ya samu ba'a sani ba, shine aka kawo mana mahaukaci cikin gida aka ajiye" babu wanda yayi magana sai ma kallonshi da suka yi suna gasgata hasashen da yayi a cikin ransu.
Umma ce ta fito daga ɗakinta sanye da hijabi don duk abinda ake yi tana jin su hankalinta kuma yana wajen ɗanta sai dai ba zai yiwu ta katse sallar da take yi ta fito ba. Suna ganin ta Kamalu ya saki wani ɗan iskan fito cikin magana irinta ƙauraye yace "Yauwa da Allah in kin shiga sai ki faɗawa mahaukcin ɗanki bashi kaɗai bane a gidan ya ɗan sassauta murya haka nan ko don muna so mu kwanta muyi barci, ah to." Ko kallonshi bata tsaya tayi ba ta faɗa ɗakin Baqeer a gaggauce tana cewa "Baqeer lafiya kake kuwa? Ko wani wajen ne yake yi maka ciwo?" Ta ƙarasa kan katifar ta zauna sannan ta rungumo kanshi a jikinta tana shafawa kamar mai lallashin ƙaramin yaro. Jin shi a jikin Ummanshi yasa ya fashe da kuka mai tsanani, kuka irin wanda tunda ƙaddarar rasa ƙafafunshi ta afko mishi bai samu yayi kamar shi ba. Kuka yake yi yana shesheƙa abun tausayi kamar ba saurayin nan ɗan kwalisa mai ji da kyau da iya ado ba, matashi mai tsayuwa da ƙafafun shi ya nemi na kanshi abun alfaharin kowanne iyaye.
Ita kanta Umma kukan take yi don tasan yanzu ne Baqeer zai san mecece rayuwa, yanzu ne zai san asalin masoyanshi na gaskiya da masu yi mishi soyayyar bogi don ba kowa ne zai karɓi ƙaddararshi a yadda tazo musu ba, tasan da yawan mutane yanzu gudunshi zasu yi shi yasa take ƙara tausaya mishi tasan ɗaukar dangana ba abu ne mai sauƙi ba a wajen shi yanzu. Sosai yayi kuka mai yawa kafin ya tsagaita da kukan ya ɗago kai ya kalleta suka haɗa ido sai yaga ashe itama hawayen take yi, hannu yasa ya goge mata hawayen yace "Shikenan ni yanzu bani da wani amfani Umma kowa guduna yake yi saboda na zama gurgu, har Baba da ya kasance mahaifina ba zai tausaya mini ba da ƙaddarar data sameni? Yanzu tsakani na dashi sai kyara da hantara kamar ba shine wannan Baban mai yawan nuna mini soyayya da tattalin farin cikina, ashe mutanen duniya sai kana da wani amfani da zaka yi musu suke sonka daga inda ka rasa duk wata dama taka sai kowa ya juya maka baya," sai ya ƙara fashewa da kuka don wani irin ciwo yake ji a cikin zuciyarshi, ji yake yi da zai iya babu abinda zai hanashi fincikota ya jefar ko ya huta da azabar raɗaɗin da take yi mishi.
Kanshi ta dafa cikin sigar lallashi tace "Kayi haƙuri Baqeer kowa da kake gani da yadda ƙaddara take zuwa mishi ba kuma ka taɓa sanin asalin masu ƙaunarka sai idan wata ƙaddara ta same ka, mahaifinka ba gudunka yake yi ba ya dai kasa karɓar ƙaddarar data same ka yayi haƙuri ya gane cewa komai daya faru nufin Allah ne, babu wani daya isa ya tsara maka rayuwa face abinda Allah ya hukunta zai sameka don haka nake jan hankalinka daka cire damuwar komai daga ranka ka sanya dangana a cikin ranka, nakasa ba kasawa bace jarrabawar rayuwa ce." Haka nan dai tayi ta mishi nasiha har ta samu ya daina kukan ya koma sauke ajiyar zuciya kawai cikin hukuncin Allah kuma sai bacci mai nauyi ya ɗauke shi, ganin da tayi ya samu bacci sai ta gyara mishi kwanciyar shi ta mayar mishi da kanshi akan pillow ta janyo abun rufar shi ta rufe shi, sai da ta tofe shi da addu'a sannan ta tashi ta kashe mishi fitila ta fita.
Tana fitowa suka haɗa ido da Baba dake tsaye a ƙofar ɗakinshi ya kalmashe hannu a ƙirji yana watsa mata wani irin wulaƙantaccen kallo, ashe duk abinda ke faruwa yana ji bai dai yi niyyar fitowa bane sai da yaga lokaci yaja Fatima dake da girkin ranar bata je ɗakin shi ba sannan ya fito. "Saboda nakasashe musakin ɗanki kika bar ni ina jira har yanzu?" Ya watso mata tambayar cikin faɗa tamkar ya mance dare ne yanzun komai ƙanƙantar sauti ɗauka yake yi. A sanyaye ta ƙaraso daf dashi sannan tace a taƙaice "kayi haƙuri" don bata son jan magana mai tsawo a tsakaninsu, tasan halinshi sarai ba haƙuri ne dashi ba don ya kwana yana yi mata tijara ba damunshi yayi ba ita kuwa yanzu bata da lokacin biye mishi suyi tashin hankali damuwar halin da ɗanta yake ciki ne a gabanta. Har ta wuce shi ta shige ɗakin nashi ta karkaɗe gado ta hau ta kwanta bai shigo ba, sai zuwa can kuma har bacci ya fara ɗaukarta taji motsin shigowar shi ɗakin.
Murmushi tayi mai ciwo ganin yadda maigidan nata ya ware murya yana yi musu tijara a tsakar gida kamar ba shine wannan uban dake ji da Baqeer yana lallaɓashi ba amma yanzu saboda ƙaddara ta sameshi shine na farko wajen juya mishi baya babu tausayi bare tausayawa halin da yake ciki shi dai damuwarshi kawai burinshi ne da ba zai cika ba. Sai da ta gyara tsayuwarta sannan tace "Amma Mallam idan ka hana Salim shigowa wajen Baqeer waye zai tallafa mishi wajen yin buƙatun da dole yana buƙatar mataimaki, kasan dai ni mace ce akwai larurar da dole sai namiji ɗan uwanshi ne zai taimaka mishi da ita kuma shi Salim ɗin da baka son ganinsu tare shi kaɗai ne yake tallafa mishi a irin waɗannan lokutan kaga kuwa ko don wannan ai baka rabasu ba tunda dai mu muke amfana dashi ba shi yake ƙaruwa damu ba."
Tsaki yayi cikin ranshi yana ganin kuma fa haka ne dole Baqeer ɗin yana buƙatar mataimaki gara ya bar Salim ɗin yaci gaba da kula dashi tunda dai yaji ya gani shi yasa kanshi ba wani ya saka shi ba don haka yace mata "Shikenan yana iya zuwa ko don kula dashi ɗin amma sai a kula da fita dashi waje don bana so."
Sai a sannan Baqeer ya ɗago kai ya kalli mahaifinshi yana tunanin dama haka yake ko kuwa wannan ƙaddarar data sameshi ce ta mayar dashi hakan, a tunaninshi ko kowa ya juya mishi baya banda mahaifin shi mi ji dashi mai tsanani so da ƙaunar farin cikin shi, sai dai kash mutanen duniya ba'a ci musu alwashi don baka sanin asalin kalarsu sai idan wata ƙaddara ta afka maka sannan suke bayyanar maka da asalin ɓoyayyiyar fuskarsu.
*****
#Baqeer🦼
#RayuwadaKaddara
#Hawayena
#Samudarashi
#UmmuAsgar
#Ayushermuhd
*ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU.
*BAQEER*
Ayusher Muhd
Umm Asghar
*KURMAN ALLO*
Asmy b Aliyu
Jidda Aliyu
*AKWAI SIRRI*
Zee Bawa
Hajja ce
*MUTALLAB ASAD*
Nana Diso
Billy S Fari
*KULUWA*
Zee yabour
Sadiya Dan
Duka Biyar ɗin akan 2k
Hudu 1600
Uku 1200
Biyu 800
Ɗaya 500
VIP💕🔥
Duk guda ɗaya 1k
NORMAL GROUP 500
VIP 1000
ACCOUNT NUMBER
0020428430
Ishaq Fatima A. Gtb
Or
8098456130
Fatima Ishaq
Opay digital services
Shaidar biya
08098456130
KATIN MTN Ta👇
07043079282
Shaidar biya ta 07065283730
Ko a tuntubi
08086207764
0816 114 6563
+234 704 040 2435
+234 903 056 9336
Umm Asghar Ce
Da
Ayusher Muhd
*BAQEER*
*NA*
*AYUSHER MUHD*
*DA*
*UMM ASGHAR*
*ƊANƊANO DAGA RUBUTUN TAGWAYE SHAFI NA GOMA SHA ƊAYA*
Da taimakon Umma Baqeer ya koma ɗakinshi. Abincin shi ta fita ta ɗauko sai dai ko kusa ya ƙi yarda ya sanya ko loma ɗaya a bakinshi don halin da ya tsinci kanshi a ciki yafi gaban ya iya sakawa cikin shi wani abu, haka tayi ta lallaɓa shi da ban haƙuri da nasiha akan ya daure yaci ko kaɗan ne amma ya kasa, haka nan ta haƙura ta ƙyaleshi ganin duk yadda tayi dashi ya ƙi karɓar abincin da take kaiwa bakinshi, sai da ta tabbatar baya buƙatar komai kafin tayi mishi sallama ta fita daga ɗakin taja mishi ƙofar ta rufe. Tana fita hawayen da yake ta riƙewa suka samu sararin zubowa, idanu ya kai kan ƙafafun shi da ko kaɗan baya jin alamun su a jikinshi, shi kenan shi yanzu haka zai yi ta zama ya nakasa ya zama musaki ba zai iya ƙara amfanawa kanshi komai ba sai dai ayi mishi. Sai ƙoƙarin ɗaga ƙafafuwan yake yi amma ya kasa, yayi-yayi ya motsa su ko yaya ne abu yaci tura. Hannunshi mai lafiyan yasa yayi ta dukan ƙafafun ko zai ji wani feeling nan ma babu abinda yake ji.
Wani irin ihu yasa yana cewa "Nooo..." haɗe da dukan ƙafafun da yake jin su tamkar ba a jikin shi suke ba da ƙarfi. Duk mutanen gidan babu wanda bai ji ihun da yake yi ba don haka duk suka firfito daga ɗakunansu suna kallon ƙofar ɗakin Baqeer ɗin sai dai babu wanda ya iya ƙarasawa ya duba halin da yake ciki. Kamalu ne yaja tsaki yace "Wannan hala bayan gurguncewar harda matsalar ƙwaƙwalwa ya samu ba'a sani ba, shine aka kawo mana mahaukaci cikin gida aka ajiye" babu wanda yayi magana sai ma kallonshi da suka yi suna gasgata hasashen da yayi a cikin ransu.
Umma ce ta fito daga ɗakinta sanye da hijabi don duk abinda ake yi tana jin su hankalinta kuma yana wajen ɗanta sai dai ba zai yiwu ta katse sallar da take yi ta fito ba. Suna ganin ta Kamalu ya saki wani ɗan iskan fito cikin magana irinta ƙauraye yace "Yauwa da Allah in kin shiga sai ki faɗawa mahaukcin ɗanki bashi kaɗai bane a gidan ya ɗan sassauta murya haka nan ko don muna so mu kwanta muyi barci, ah to." Ko kallonshi bata tsaya tayi ba ta faɗa ɗakin Baqeer a gaggauce tana cewa "Baqeer lafiya kake kuwa? Ko wani wajen ne yake yi maka ciwo?" Ta ƙarasa kan katifar ta zauna sannan ta rungumo kanshi a jikinta tana shafawa kamar mai lallashin ƙaramin yaro. Jin shi a jikin Ummanshi yasa ya fashe da kuka mai tsanani, kuka irin wanda tunda ƙaddarar rasa ƙafafunshi ta afko mishi bai samu yayi kamar shi ba. Kuka yake yi yana shesheƙa abun tausayi kamar ba saurayin nan ɗan kwalisa mai ji da kyau da iya ado ba, matashi mai tsayuwa da ƙafafun shi ya nemi na kanshi abun alfaharin kowanne iyaye.
Ita kanta Umma kukan take yi don tasan yanzu ne Baqeer zai san mecece rayuwa, yanzu ne zai san asalin masoyanshi na gaskiya da masu yi mishi soyayyar bogi don ba kowa ne zai karɓi ƙaddararshi a yadda tazo musu ba, tasan da yawan mutane yanzu gudunshi zasu yi shi yasa take ƙara tausaya mishi tasan ɗaukar dangana ba abu ne mai sauƙi ba a wajen shi yanzu. Sosai yayi kuka mai yawa kafin ya tsagaita da kukan ya ɗago kai ya kalleta suka haɗa ido sai yaga ashe itama hawayen take yi, hannu yasa ya goge mata hawayen yace "Shikenan ni yanzu bani da wani amfani Umma kowa guduna yake yi saboda na zama gurgu, har Baba da ya kasance mahaifina ba zai tausaya mini ba da ƙaddarar data sameni? Yanzu tsakani na dashi sai kyara da hantara kamar ba shine wannan Baban mai yawan nuna mini soyayya da tattalin farin cikina, ashe mutanen duniya sai kana da wani amfani da zaka yi musu suke sonka daga inda ka rasa duk wata dama taka sai kowa ya juya maka baya," sai ya ƙara fashewa da kuka don wani irin ciwo yake ji a cikin zuciyarshi, ji yake yi da zai iya babu abinda zai hanashi fincikota ya jefar ko ya huta da azabar raɗaɗin da take yi mishi.
Kanshi ta dafa cikin sigar lallashi tace "Kayi haƙuri Baqeer kowa da kake gani da yadda ƙaddara take zuwa mishi ba kuma ka taɓa sanin asalin masu ƙaunarka sai idan wata ƙaddara ta same ka, mahaifinka ba gudunka yake yi ba ya dai kasa karɓar ƙaddarar data same ka yayi haƙuri ya gane cewa komai daya faru nufin Allah ne, babu wani daya isa ya tsara maka rayuwa face abinda Allah ya hukunta zai sameka don haka nake jan hankalinka daka cire damuwar komai daga ranka ka sanya dangana a cikin ranka, nakasa ba kasawa bace jarrabawar rayuwa ce." Haka nan dai tayi ta mishi nasiha har ta samu ya daina kukan ya koma sauke ajiyar zuciya kawai cikin hukuncin Allah kuma sai bacci mai nauyi ya ɗauke shi, ganin da tayi ya samu bacci sai ta gyara mishi kwanciyar shi ta mayar mishi da kanshi akan pillow ta janyo abun rufar shi ta rufe shi, sai da ta tofe shi da addu'a sannan ta tashi ta kashe mishi fitila ta fita.
Tana fitowa suka haɗa ido da Baba dake tsaye a ƙofar ɗakinshi ya kalmashe hannu a ƙirji yana watsa mata wani irin wulaƙantaccen kallo, ashe duk abinda ke faruwa yana ji bai dai yi niyyar fitowa bane sai da yaga lokaci yaja Fatima dake da girkin ranar bata je ɗakin shi ba sannan ya fito. "Saboda nakasashe musakin ɗanki kika bar ni ina jira har yanzu?" Ya watso mata tambayar cikin faɗa tamkar ya mance dare ne yanzun komai ƙanƙantar sauti ɗauka yake yi. A sanyaye ta ƙaraso daf dashi sannan tace a taƙaice "kayi haƙuri" don bata son jan magana mai tsawo a tsakaninsu, tasan halinshi sarai ba haƙuri ne dashi ba don ya kwana yana yi mata tijara ba damunshi yayi ba ita kuwa yanzu bata da lokacin biye mishi suyi tashin hankali damuwar halin da ɗanta yake ciki ne a gabanta. Har ta wuce shi ta shige ɗakin nashi ta karkaɗe gado ta hau ta kwanta bai shigo ba, sai zuwa can kuma har bacci ya fara ɗaukarta taji motsin shigowar shi ɗakin.