Sashe 104
Triplets Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A ɓangaren ita kuma Rimsha, sosai ta kara jin haushin Lion, saboda yadda suka kwana suka tashi bai nemeta ba, bata yi zaton haka daga gare shi ba, hakan yasa ta kara ji a ranta da gaske cewa baya sonta, kowa ya sani tana bala'in sonsa na kin karawa, baki ma ya yi kaɗan ya iya zayyana yadda take son shi.
Hakan yasa abin ya yi mugun taɓata sosai, har wani irin zazzaɓi mai zafi gaske take ji, idan baku manta ba ita fa time da daddynta ya hana ta kallon shi a Tv tun suna Abuja bata kai haka ba ma, sai da ta kwanta a gadon asibiti, a lokacin ma bata san menene matsayarsa a wajenta ba, bata san cewa tana son shi ne ko dai iya burgewa ɗin bace ba, bare kuma yanzu da ya zama mijinta, suka zama abu guda, ta saba da shi, soyayyarsa ya karu a zuciyarta na wuce misali.
Sai abin ya yi muguwar jijjigata, sai dai fa wani abu guda game da ita wanda nasan tabbas kun manta da shi, duk daɗi duk wuya, duk yadda Rimsha ta kai ga son abu, to fa bata jurar walaƙanci a kan wannan abin, nasan dayawanku kun manta zamanta a Ilorin kwara State, to PRINCESS TEEMA dai ban manta ba ni, kuma bari na tuna maku, time da kausar ta yi mata walaƙanci a kan abinci, a haka ta zauna da yunwa duk da Iya Kausar ɗin ta ce tayi hakuri ta ci, amma taki ci sai dai suka sayi drinks ita da Ayla, time da Kausar still ta sake yi mata rigima a kan kayan sakawarta, kun tuna ta ce ba zata sanya kayar ba, har ta ɗauko tsohon nata ta saka, kun tuna? Bugu da kari kunsan saboda ba zata iya jurar walaƙanci bane ba yasa suka baro gidansu Kausar, duk da abin ya haɗu da yi mata fyaɗen da Borda Jami'u ya so ya yi, so haka zuciyarta take, ba zata iya jurar walaƙanci ba, wasu abubuwa da kuke gani take yi wa Lion, sau da dama Malika ce take sanyata yi, amma banda haka ko shi ɗin ba bazata ɗauki walaƙanci daga wajensa ba, haka ƴaƴan Nawazuddeen suke, Malika tasan cewa shi Lion tamkar bugun zuciyar Rimshar ne, already ta yi saurin kamuwa da sonsa tun kananun shekarunta, so hakan yasa ta tayata yakin neman soyayyarsa, badon taimaka mata da ta yi ba, da ko kusa ko alama Lion ba zai so ta ba, Malika tana kaunarta sosai yasa take kaunar duk abin da take so, idan baku manta ba Rimsha bata sanya kananan kaya, bata sanya irinsu wandunan Jeans da sauransu, har Kausar tana mata horo da su idan bata son ta sanya mata kaya, amma baku yi mamakin meyasa take sanya kananan kaya a gidan Lion ba? Tun kuma basu fara soyayya ba, to Malika ce take sanyata sakawa saboda wasu dalilai guda biyu, na farko shi Lion bai ma san irin dressing na Hausawa ba, kuma ba kyau zata yi mashi ba ko da ya gani, saboda su a al'adarsu kowa ya sani mace ta bayyanar da surar jikinta shi ne kyau da birgewa, so idan mace bata yi hakan bama su ganin mahaukaciya mara sanin abin da take yi suke yi mata, kada ku ga laifinsu haka al'adar duk wani Bature yake, in ma musulmi ko Kristen, duk tafiyarsu kusan ɗaya ce, banbancin kawai ibada ne, wani Baturen ma idan ya kalli mace da common doguwar riga ce har kasa, tambayarta zai yi anya yau kanta lafiya kuwa? Ko dai mijinta ne ya mutu? Yasa ta sanya buyagin haukar da ta sanya a jikinta nan? So haka suke rayuwarsu tun iyaye da kakanin, na tabbata koda baku taɓa zama a cikinsu ba, to kuna kallonsu a Tv, yadda kuke ganinsu a Tv ma abin wasa ne, rayuwarsu ta zahiri ta fi hakan, a Tv ai sai sun kawata shi yadda zai ja ra'ayin ƴan kallo, kuma wani lokaci a film suna yin abin da zai ja ra'ayin jama'a ce kawai dan su cigaba da samawa kasarsu kuɗin shiga, banda haka rayuwarsu ta zahiriya ma ai ya ninninka haka, wannan dalilin yasa Malika take sanyata yin dressing irin nasu, dan kada ya ganta da shigar hausawa ya yi mata kallon wata mahaukaciya mai tsummokarai a jiki. Abu na biyu kuma Malikar ta yi amfani da rauninsa ne a wajen, tasan dayawan Turawa suna bala'in son mace mai shape, baya da kuma breast tula tula, abin yana tashin kansu sosai, so idan Rimsha tana sanya irinsu a baya ba zasu fitar mata da shape nata ba, hakan yasa ta sanyata rinƙa saka irin waɗan nan kaya, kuma ta dalilin hakan ne ya ja ra'ayin Lion ɗin, yana tsananin kaunar shape na Rimsha sosai, tudun mazaunanta ba ma sai na yi magana ba, kunsan yana bala'i sonsu, barema kuma tula tulanta, kunga kuwa Malika ta kafa mashi tarko ne kuma ya afka ba tare da sanin shi ba, Malika ta yi abubuwa da dama wa Rimsha wanda baki ba zai faɗesu ba, wasu lokuta idan Rimshar ta yi wani abin da bata saba yi ba, ko kuma ba'a al'adarmu ta Hausa Fulani ba, to idan kuka bincika da sa hannun Malika, ba komai yasa Malikar ta taimaka mata ba a lokacin face dalilai guda biyu, na farko tasan Rimshar ta yi shigar sauri wa soyayyar Lion ɗin, kuma tabbas a kansa tana iya mutuwa, dan idan baku manta ba ta sha suma a kansa sosai, na biyu kuma a time ɗin tana da matsala a ƙwaƙwalwarta na razana da birkicewa da ta samu daga Daular Mutuwa, abu kaɗan yana razanata ta suma, sai abin ya zo ya haɗe mata da soyayyarsa, wanda idan ba'ayi dace ba tsab zai kasheta har lahira, hakan yasa Malikar ta taimaka mata sosai dan tana kaunarta da iya gaskiya, ita ɗin aljanace mai mutunci kuma bata manta halacci, dama dayawan al'janu basu manta halacci a rayuwa, nasan kowa tana son sanin wacece Malika, lokacin sanin hakan ya kusa zuwa, zata gaya maku wacece ita da kanta.
So a wannan karon fushin da Rimshar ta yi ma da sa hannun Malika, ba wai kuma ta tayata yin fushin bane, a'a, dama kun san ita Malika a koda yaushe ita take ƙoƙarin ɓoyewa Rimshar duk wasu laifuka da Lion ya yi mata a baya, sai ta rufe mata idanu ba zata taɓa damuwa da laifin ba, ita dai soyayyrsa kawai ta sani, a lokacin tana yi mata hakan ce saboda ta ceci rayuwarta, sannan kuma su danne komai su hakura dan su sami soyayyarsa, banda haka da wlh Rimsha ba zata ɗauki wasu abubuwa da ya yi mata a bayaba, saboda bata da zuciyar jurar walaƙanci ko kaɗan, ba zata iya ɗauka ba. So a yanzu da Malikar ta fahimci Lion fa ko zai mutu ba zai dai'na son Rimshar ba, ta rigada ta zama jinin jikinsa, shi ne yasa sai ta tsame hannunta daga lamarinsu ta koma gefe guda tana kallon masoyan tana jin daɗi abinta, shiyasa Rimsha ta kalli laifinsa a wannan karon, shiyasa ta kalli kamar walaƙanci ya yi mata, hakan yasa ta ce ko zata mutu ba zata ɗauki hakan ba, shiyasa ta ɗauki fushi mai zafi da shi, dama mai hakuri bai iya fushi ba, idan ka kure mai hakuri to wlh ka kuka da kanka, dan sai ka ɗanɗani bakinciki, ga shi kuma ya kara ɓata mata rai yadda ya kwana ya tashi bai kirata ya rarrasheta ba, abin ya kara baƙanta mata rai, sai take ganin ai walakancin ya yi yawa over.
Shi kuma har ga Allah ba wai baya son kiranta ɗin bane, dannewa kawai ya yi bai kira ɗin ba, saboda abin da ya sanya a gabansa, a wannan point da yake a ciki sam baya son ya biye mata, dan zata caza mashi kai sosai bayan wanda yake ciki, shi ne dalilin da yasa ya danne ya jure ya kyaleta ɗin, amma shi da kansa yana ji a jikinsa, har wani zazzaɓi shi ma yake ji na barinta a cikin damuwa da ya yi, tun daren jiyan yasan bai kyauta ba, bayan abin ya faru da ya kwanta zai yi barci, zuciyarsa ta ɗan yi sanyi, shi da kansa yasan bai yi mata adalci ba duba da yanayin karantar shekarunta, bai kamata ya haɗa hankalinsa da nata ba, kuma gaskiya Areef ya gaya mashi, son shi yasa take damuwa da shi, idan da bata son shi ko zai shekara miliyan bai zo in da take ba, ba zata taɓa damuwa ba, bugu da kari kuma ga abin da ya yi mata 30 days back, ta bakin mommar tasu yanzu ne yakamata ya lallaɓata ya biyata dakon soyayyarsa da ta yi na tsawon shekaru, so a takaice dai shi da kansa yasan sam bai kyauta mata ba, ya danne zuciyarsa ce kawai ya kyaleta sai ya kammala aikin da yake gabansa, idan sun haɗu a U.s sai ya ɗauki kayansa ya lallaɓata, sai dai fa bai sawa ransa cewa zai bata hakuri ba, babu wannan tunanin a ransa, tunaninsa dai shi ne idan sun haɗu a U.s ba shikenan sun ga juna ba? A tunaninsa daga haka zata sauko su koma normal, abin da bai sani ba shi ne ita fa a wannan karon da gasken gaske take yin fushin nata, babu alamar zata sauko ma, dan ta zo har wuya, ga Malika ta zame hannunta, ta bar Rimshar ta ɗan wanashi kaɗan, wata kila daga haka ya fara sanin darajar mum da dad ɗinta, dan abin yana bakantawa Malikar rai yadda Lion ɗin yake yi wa mum da dad ɗin, sam bata so, to ita ma kenan, bare kuma Rimsha da take ƴar cikinsu, ai idan ta sani zasu yi yaki da shi ba kaɗan ba, dan wlh zata iya rabuwa da shi tsab akan iyayenta, barema mum ɗinta, bazata iya jurar wani ya yi masu walakanci ba.
Hakan yasa abin ya yi mugun taɓata sosai, har wani irin zazzaɓi mai zafi gaske take ji, idan baku manta ba ita fa time da daddynta ya hana ta kallon shi a Tv tun suna Abuja bata kai haka ba ma, sai da ta kwanta a gadon asibiti, a lokacin ma bata san menene matsayarsa a wajenta ba, bata san cewa tana son shi ne ko dai iya burgewa ɗin bace ba, bare kuma yanzu da ya zama mijinta, suka zama abu guda, ta saba da shi, soyayyarsa ya karu a zuciyarta na wuce misali.
Sai abin ya yi muguwar jijjigata, sai dai fa wani abu guda game da ita wanda nasan tabbas kun manta da shi, duk daɗi duk wuya, duk yadda Rimsha ta kai ga son abu, to fa bata jurar walaƙanci a kan wannan abin, nasan dayawanku kun manta zamanta a Ilorin kwara State, to PRINCESS TEEMA dai ban manta ba ni, kuma bari na tuna maku, time da kausar ta yi mata walaƙanci a kan abinci, a haka ta zauna da yunwa duk da Iya Kausar ɗin ta ce tayi hakuri ta ci, amma taki ci sai dai suka sayi drinks ita da Ayla, time da Kausar still ta sake yi mata rigima a kan kayan sakawarta, kun tuna ta ce ba zata sanya kayar ba, har ta ɗauko tsohon nata ta saka, kun tuna? Bugu da kari kunsan saboda ba zata iya jurar walaƙanci bane ba yasa suka baro gidansu Kausar, duk da abin ya haɗu da yi mata fyaɗen da Borda Jami'u ya so ya yi, so haka zuciyarta take, ba zata iya jurar walaƙanci ba, wasu abubuwa da kuke gani take yi wa Lion, sau da dama Malika ce take sanyata yi, amma banda haka ko shi ɗin ba bazata ɗauki walaƙanci daga wajensa ba, haka ƴaƴan Nawazuddeen suke, Malika tasan cewa shi Lion tamkar bugun zuciyar Rimshar ne, already ta yi saurin kamuwa da sonsa tun kananun shekarunta, so hakan yasa ta tayata yakin neman soyayyarsa, badon taimaka mata da ta yi ba, da ko kusa ko alama Lion ba zai so ta ba, Malika tana kaunarta sosai yasa take kaunar duk abin da take so, idan baku manta ba Rimsha bata sanya kananan kaya, bata sanya irinsu wandunan Jeans da sauransu, har Kausar tana mata horo da su idan bata son ta sanya mata kaya, amma baku yi mamakin meyasa take sanya kananan kaya a gidan Lion ba? Tun kuma basu fara soyayya ba, to Malika ce take sanyata sakawa saboda wasu dalilai guda biyu, na farko shi Lion bai ma san irin dressing na Hausawa ba, kuma ba kyau zata yi mashi ba ko da ya gani, saboda su a al'adarsu kowa ya sani mace ta bayyanar da surar jikinta shi ne kyau da birgewa, so idan mace bata yi hakan bama su ganin mahaukaciya mara sanin abin da take yi suke yi mata, kada ku ga laifinsu haka al'adar duk wani Bature yake, in ma musulmi ko Kristen, duk tafiyarsu kusan ɗaya ce, banbancin kawai ibada ne, wani Baturen ma idan ya kalli mace da common doguwar riga ce har kasa, tambayarta zai yi anya yau kanta lafiya kuwa? Ko dai mijinta ne ya mutu? Yasa ta sanya buyagin haukar da ta sanya a jikinta nan? So haka suke rayuwarsu tun iyaye da kakanin, na tabbata koda baku taɓa zama a cikinsu ba, to kuna kallonsu a Tv, yadda kuke ganinsu a Tv ma abin wasa ne, rayuwarsu ta zahiri ta fi hakan, a Tv ai sai sun kawata shi yadda zai ja ra'ayin ƴan kallo, kuma wani lokaci a film suna yin abin da zai ja ra'ayin jama'a ce kawai dan su cigaba da samawa kasarsu kuɗin shiga, banda haka rayuwarsu ta zahiriya ma ai ya ninninka haka, wannan dalilin yasa Malika take sanyata yin dressing irin nasu, dan kada ya ganta da shigar hausawa ya yi mata kallon wata mahaukaciya mai tsummokarai a jiki. Abu na biyu kuma Malikar ta yi amfani da rauninsa ne a wajen, tasan dayawan Turawa suna bala'in son mace mai shape, baya da kuma breast tula tula, abin yana tashin kansu sosai, so idan Rimsha tana sanya irinsu a baya ba zasu fitar mata da shape nata ba, hakan yasa ta sanyata rinƙa saka irin waɗan nan kaya, kuma ta dalilin hakan ne ya ja ra'ayin Lion ɗin, yana tsananin kaunar shape na Rimsha sosai, tudun mazaunanta ba ma sai na yi magana ba, kunsan yana bala'i sonsu, barema kuma tula tulanta, kunga kuwa Malika ta kafa mashi tarko ne kuma ya afka ba tare da sanin shi ba, Malika ta yi abubuwa da dama wa Rimsha wanda baki ba zai faɗesu ba, wasu lokuta idan Rimshar ta yi wani abin da bata saba yi ba, ko kuma ba'a al'adarmu ta Hausa Fulani ba, to idan kuka bincika da sa hannun Malika, ba komai yasa Malikar ta taimaka mata ba a lokacin face dalilai guda biyu, na farko tasan Rimshar ta yi shigar sauri wa soyayyar Lion ɗin, kuma tabbas a kansa tana iya mutuwa, dan idan baku manta ba ta sha suma a kansa sosai, na biyu kuma a time ɗin tana da matsala a ƙwaƙwalwarta na razana da birkicewa da ta samu daga Daular Mutuwa, abu kaɗan yana razanata ta suma, sai abin ya zo ya haɗe mata da soyayyarsa, wanda idan ba'ayi dace ba tsab zai kasheta har lahira, hakan yasa Malikar ta taimaka mata sosai dan tana kaunarta da iya gaskiya, ita ɗin aljanace mai mutunci kuma bata manta halacci, dama dayawan al'janu basu manta halacci a rayuwa, nasan kowa tana son sanin wacece Malika, lokacin sanin hakan ya kusa zuwa, zata gaya maku wacece ita da kanta.
So a wannan karon fushin da Rimshar ta yi ma da sa hannun Malika, ba wai kuma ta tayata yin fushin bane, a'a, dama kun san ita Malika a koda yaushe ita take ƙoƙarin ɓoyewa Rimshar duk wasu laifuka da Lion ya yi mata a baya, sai ta rufe mata idanu ba zata taɓa damuwa da laifin ba, ita dai soyayyrsa kawai ta sani, a lokacin tana yi mata hakan ce saboda ta ceci rayuwarta, sannan kuma su danne komai su hakura dan su sami soyayyarsa, banda haka da wlh Rimsha ba zata ɗauki wasu abubuwa da ya yi mata a bayaba, saboda bata da zuciyar jurar walaƙanci ko kaɗan, ba zata iya ɗauka ba. So a yanzu da Malikar ta fahimci Lion fa ko zai mutu ba zai dai'na son Rimshar ba, ta rigada ta zama jinin jikinsa, shi ne yasa sai ta tsame hannunta daga lamarinsu ta koma gefe guda tana kallon masoyan tana jin daɗi abinta, shiyasa Rimsha ta kalli laifinsa a wannan karon, shiyasa ta kalli kamar walaƙanci ya yi mata, hakan yasa ta ce ko zata mutu ba zata ɗauki hakan ba, shiyasa ta ɗauki fushi mai zafi da shi, dama mai hakuri bai iya fushi ba, idan ka kure mai hakuri to wlh ka kuka da kanka, dan sai ka ɗanɗani bakinciki, ga shi kuma ya kara ɓata mata rai yadda ya kwana ya tashi bai kirata ya rarrasheta ba, abin ya kara baƙanta mata rai, sai take ganin ai walakancin ya yi yawa over.
Shi kuma har ga Allah ba wai baya son kiranta ɗin bane, dannewa kawai ya yi bai kira ɗin ba, saboda abin da ya sanya a gabansa, a wannan point da yake a ciki sam baya son ya biye mata, dan zata caza mashi kai sosai bayan wanda yake ciki, shi ne dalilin da yasa ya danne ya jure ya kyaleta ɗin, amma shi da kansa yana ji a jikinsa, har wani zazzaɓi shi ma yake ji na barinta a cikin damuwa da ya yi, tun daren jiyan yasan bai kyauta ba, bayan abin ya faru da ya kwanta zai yi barci, zuciyarsa ta ɗan yi sanyi, shi da kansa yasan bai yi mata adalci ba duba da yanayin karantar shekarunta, bai kamata ya haɗa hankalinsa da nata ba, kuma gaskiya Areef ya gaya mashi, son shi yasa take damuwa da shi, idan da bata son shi ko zai shekara miliyan bai zo in da take ba, ba zata taɓa damuwa ba, bugu da kari kuma ga abin da ya yi mata 30 days back, ta bakin mommar tasu yanzu ne yakamata ya lallaɓata ya biyata dakon soyayyarsa da ta yi na tsawon shekaru, so a takaice dai shi da kansa yasan sam bai kyauta mata ba, ya danne zuciyarsa ce kawai ya kyaleta sai ya kammala aikin da yake gabansa, idan sun haɗu a U.s sai ya ɗauki kayansa ya lallaɓata, sai dai fa bai sawa ransa cewa zai bata hakuri ba, babu wannan tunanin a ransa, tunaninsa dai shi ne idan sun haɗu a U.s ba shikenan sun ga juna ba? A tunaninsa daga haka zata sauko su koma normal, abin da bai sani ba shi ne ita fa a wannan karon da gasken gaske take yin fushin nata, babu alamar zata sauko ma, dan ta zo har wuya, ga Malika ta zame hannunta, ta bar Rimshar ta ɗan wanashi kaɗan, wata kila daga haka ya fara sanin darajar mum da dad ɗinta, dan abin yana bakantawa Malikar rai yadda Lion ɗin yake yi wa mum da dad ɗin, sam bata so, to ita ma kenan, bare kuma Rimsha da take ƴar cikinsu, ai idan ta sani zasu yi yaki da shi ba kaɗan ba, dan wlh zata iya rabuwa da shi tsab akan iyayenta, barema mum ɗinta, bazata iya jurar wani ya yi masu walakanci ba.