Sashe 96
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yanzu ace kin zo kasar 'Yar soja bazan ganki ba sai nayi cigiya? Ina Mairaman take? Duniya Mairama duk tafi sona kaf 'ya'yan babu mai girmama maganar Malamijo kamar ta." Yayi maganar batare da korafin Radhiya kada tayi masa wani abu ba daidai ba a cikin gidan.
"Uhmm Malamijo tare fa muke da..." Emzee ya soma fada masa saboda yana tunanin gara ya sani kada abin yazo masa a bazata.
Hannu ya yarfe gefe yana kallon Mairama da wani mutum yasha yadi na maza mai masifar kyau da tsada cikin wanda Baban Arifah yasa aka dinka masa.
"Ko ma waye su zo ku hadu ku ci uban 'yan iskan gidan nan"
"Su wa kenan?" Radhiya tace da doki sai dai Malamijo baya ma jinta ko kadan. Mutuwar tsaye yayi hannunsa a kahon zuci yana farfar da idanu bakinsa ya kasa hada kalmar Zayyan da yake son ambata.
Zayyan na karasowa da murmushinsa ya mika hannu ya riko hannun daman Malamijo. Ai hannuwansu na haduwa Malamijo yayi sharaf a sume ya fado masa a jiki.
Dama sun sani dole ya tsorata. Emzee ya rugu zai daga shi Zayyan yace ya wuce su gyara inda zai kwantar dashi ya ciccibe shi shi kadai tamkar ya dauki yaro karami. To abu ne babu body babu alamar body. Dama ya lafiyar kura...tuntuni babu jikin Hajiyayye mayya tazo ta karasa gawar da ba tata ba.
Tsakar gidan babu kowa sai gayyar su Hajiyayye rashin wadatar dakin yasa ta dawo dasu nan duk da ma dai akwai sanyi garin. Banda cooler din shinkafa a gefe ga ta miyar da ta wadatu da nama na tinkiyar da suka dauko jiya ga salad da su tumatir yau din bushasha za'ayi saboda jiya sun tarki sa'a. Shanun da suka dauka suna ajiye a gidan Talle ranar kasuwar dabbobi zasu kai a kwashi naira.
Da sauri Emzee ya shigo sabuwar tabarmar da ta shimfida yaran nata sun soma zama ya murtuke fuska duk da bai sansu ba "kai ku tashi"
"Yaro kai kuma daga ina?" Babban cikin nasu ya tambaya yana masa kallon raini. Ido kawai Emzee ya watsa masa yaja baya da sauri. Tsabar training sai budewa kwanjinsa yake yi musamman daga kirji, hannuwa suna murdewa irin na kakkarfan namiji. Rigar jikinsa ma kusan ta kama shi ita ta karasa tona asirin yanayin jikin nasa. Wanda ya rage akan tabarmar mai bin babban ya kalla yayi masa alamar ya tashi.
"In naki fa?"
Emzee bai sake tunani ba ya ja tabarmar ya kifar dashi a wurin ya koma gefen dakin Malamijo ya shimfide masa ita sannan ya shiga ya dauko masa filo. Radhiya dakin Yadikko tayi da sauri ta same shi a rufe da karamin kwado sai ta je na Hajjo. Nan ta tarar da komai ba yadda ta sani ba sai karajin Hajiyayye daga bayanta.
"Ke daga ina kuke ne kike leka min daki?"
Da mamaki tace "dakinki? Ina Hajjon kuma?"
Daidai nan Zayyan ya shigo da Malamijo a hannu ya kwantar dashi a inda Emzee ya nuna masa Ummi tana take masa baya hankali a tashe.
"Ku su waye ne?" Hajiyayye ta matso inda suke ta kalli Malamijo ta watsar.
Cikin salama Ummi tace mata "ni 'yarsa ce wadannan kuma yarana ne da babansu"
Tsaki taja duk da suturun jikinsu sunyi mata kwarjini amma bata so raini ya shiga tsakaninta dasu. Yadda uban yake tsoronta to kowa ma fa yaji tsoro kada a kawo mata wargi ba dauka zata yi ba.
"Me ya same Malamijon?" Tace a dakile wanda tuni ran kowa ya sosu.
"Tsorata yayi ya suma" Ummi ta bata amsa.
"uhmmm" ta tabe baki "bana son hayaniya kamar yadda shi uban naku ya sani a kiyaye"
Hayaniyar da take yi ce tasa mutanen cikin gidan suka fara lekowa ganin da wa take yi. Na'e ce kawai da wasu cikin yaran. Yadikko sun tafi asibiti da Atine guda cikin jariran babu lafiya ko ta kan Malamijo bata bi ba da zasu tafi. Ita yanzu burinta kawai Atine tayi arba'in yaran su kara kwari itama ta tafi. Shekaru sama da arba'in tana zaune tamkar sharar gidansa ta kula masa da yara ya bude baki ya fada mata magana son ransa.
Kannen Mairama da suke zawarci su biyu da sauran kannensu duk sunyi zuru zuru amma ganinta sai gasu sun fara sakin fuska suna yi musu barka da zuwa.
Hajiyayye ta wani daka musu tsawa saboda tsaurin ido "ba cewa nayi idan yaran nan sun zo cin abinci kowa ya zauna a daki ba? Ko shi Malamijon bai nanata muku ba kafin shigowarsu?"
Mayunwatan yaran kananun suka matso suna jira ta zuba musu ta kalli tabarmarta "ku shiga dakinsa akwai tabarma a bani tawa zan ciyar da yaranmu"
Zayyan da Mairama sun tsaya ne kawai kallon wannan mata mai zubin mahaukata tana ta bada umarni a gidan. Daurewa tayi ta tambayi wata kanwarta matsayinta a gidan.
"Amaryar Malamijo ce"
"Amarya kuma?" A iya saninta babu sauran wuri a gidan nasu to wa ya saka. Sai gashi kafin ta tambaya ma ta bata amsa da cewa Hajjo ya saki "Malamijo Hajjo?" Tace kamar tayi kuka.
Kanenta da suke karatu a Kano gidanta su Laila duka lokacin da suka zo kafin ta wuce Abuja tasa sun tafi hutu wurin iyayensu mata. Ta san da tuni ta sami labari a wurinsu.
Babu wanda yayi motsi da Hajiyayye tace su dauke Malamijo daga kan tabarmarta ta doki cinya tana sababi wai zai farfado ya sameta ne sai ya yiwa bakin nan bayanin matsayinta.
Abin takaicin ya ishi Zayyan zaiyi magana Ummi ta dakatar dashi ta nuna masa Radhiya da take bin matar da wani irin kallon raini
"Baki ga suma yayi bane kike zancen a baki tabarma ku ci abinci?"
"Yarinya kada kice zaki yiwa Hajiyayye rashin kunya wallahi sai na farfasa miki jiki yanzun nan a wuce wurin" babban yace a kule yunwa na cin hanjinsa an tsaya ana bata musu lokaci. Ko kadan daga uwar har yaran basu da da'a.
Sai da ya gama Radhiya ta tafi gaban kulolin da ta kula suna yiwa kallon mutumci ta bude da ta ga miya ce nama ya kusan cika ta.
"Wa ya baki izinin taba min abinci? Ke idan Malamijo ya farka zan iya sawa ya hanaku sake zuwa gidan nan"
Emzee da Ibrahim Radhiya ta nunawa kulolin da hannu tamkar ba da ita ake magana ba "bros ga fa abinda ya kawomu Sumaila kuzo mu fara aiki"
Tamkar masu jira suka je zasu dauki kulolin nan yaran Hajiyayye suka yi kukan kura tamkar mayun gaske. Duk abinda suke yi Malamijo ya farfado ya ma dan bude ido da ya ga abu ya soma kankama ya runtse kayansa ya cigaba da kwanciya. Ummi da Daada wuri suka samu suka zauna saboda abin kunya ne ace suna da su Emzee su rinka saka baki suna magana da yara irin na Hajiyayye. Ummi tana da yakinin indai da yaranta a wurin bata da matsala don ko da Radhiya kadai ta barsu ta ishesu.
Wurin ke neman kacamewa Radhiya ta kira Zayyana ta nuna mata kula daya tace ta zauna a kai itama ta zauna akan daya ta dora kafa daya kan daya. Tsagerun Hajiyayye suna son tashinsu amma yadda take kada kafa ga wasu maza a tsaye a gefe wato Emzee da Ibrahim kowa ya tamke fuska duk sai suka sha jinin jikinsu. Malamijo da yaji abin baiyi masa ba ya dan kyallo ido daya yace "Zayyan"
Uba da da ne suka amsa a tare. Wai shi Malamijo a tunaninsa ko dai Hajiyayye mayar gaske ce take son tsorata shi da fatalwar surukinsa zai daure ai ba'a san Fulani da tsoro ba ya dauke kai kamar bai ganshi ba ya cigaba da cewa Emzee "ina rundunar sauran sojojin da kace zaku zo tare?"
Ba yaran ba Hajiyayye ma sai da cikinta ya bada sauti "soja kuma"
Emzee ya sake mazewa sai lokacin ta kula da kayan jikinsa ma. Hankalinta yayi mummunan tashi kuwa a tsorace ta cewa manyan su fita zata san abinyi. Su ma da sauri suka fita din kada rundunar sojojin su iso. Tana kallo Radhiya ta kira yaran gidan suka debo kwanaku yau ko biki ake a gidan sai haka. Abincin nan tas ta rabe musu harda kwakkwafe kular bata bar ko kwayar shinkafa ba.
Zayyan kallonta yayi ya saki murmushi kawai tana kara burge shi. Haka yake kaifi daya kuma haka yake son 'ya'yansa. Kada su cuci kowa kuma kada su bari a cuce su. Bayan ta gama ta tura kular wurin wanke wanke ta dawo kusa da Malamijo ta zauna. Hajiyayye ta rasa me ya kamata ta yi saboda bacin ran da take ciki. Wannan wane irin mutane ne suka shigo gidan da yake karkashin mulkinta suna neman chaza mata kai. Kwafa tayi ta bar wurin ta tafi daki zugar yaranta suna biye da ita ana kukan nama.
Malamijo sai lokacin ya bude ido yana murmushi a hankali yadda babu mai ji sai na kusa dashi yace "Alakakai gayyar mayu daga nan ma sai gidan tsoho"
Radhiya tace masa "fadi da karfi mana taji Malamijo a haka bazata san kana yi ba"
"Barni da ita a hakan ma kun more min su. Bana so taji ne ta dawo"
"Barka da yamma Malamijo" Zayyan yace bayan yaran sun gama dariyar kalaman Malamijo.
Jikinsa ne yayi wani mugun sanyi kamar an sare masa gwiwa ya juya ya tabbatar Zayyan din ne dai yake gani kawai sai ya koma ya kwanta ya rufe idanu.
"Mairama kirawo matar nan tazo ta tsallake ni."
"Tsallakewa kamar wata mayya"
"Yo ba mayyar bace? Aure ne na kaddara na kwasowa kaina. Yanzu don bala'i ko yaya na kalli bangaren arewa maso gabashin inda kike zaune sai in rinka gane gane"
Ibrahim da Emzee ne suka fara dariya Ummi ta hararesu. Zayyan da ya gane dashi ake dole ya rike tashi dariyar a gaban suruki.
"Kamar me da me kake gani?" Radhiya ta tambayeshi tana danne dariyarta.
"Uhmm Malamijo tare fa muke da..." Emzee ya soma fada masa saboda yana tunanin gara ya sani kada abin yazo masa a bazata.
Hannu ya yarfe gefe yana kallon Mairama da wani mutum yasha yadi na maza mai masifar kyau da tsada cikin wanda Baban Arifah yasa aka dinka masa.
"Ko ma waye su zo ku hadu ku ci uban 'yan iskan gidan nan"
"Su wa kenan?" Radhiya tace da doki sai dai Malamijo baya ma jinta ko kadan. Mutuwar tsaye yayi hannunsa a kahon zuci yana farfar da idanu bakinsa ya kasa hada kalmar Zayyan da yake son ambata.
Zayyan na karasowa da murmushinsa ya mika hannu ya riko hannun daman Malamijo. Ai hannuwansu na haduwa Malamijo yayi sharaf a sume ya fado masa a jiki.
Dama sun sani dole ya tsorata. Emzee ya rugu zai daga shi Zayyan yace ya wuce su gyara inda zai kwantar dashi ya ciccibe shi shi kadai tamkar ya dauki yaro karami. To abu ne babu body babu alamar body. Dama ya lafiyar kura...tuntuni babu jikin Hajiyayye mayya tazo ta karasa gawar da ba tata ba.
Tsakar gidan babu kowa sai gayyar su Hajiyayye rashin wadatar dakin yasa ta dawo dasu nan duk da ma dai akwai sanyi garin. Banda cooler din shinkafa a gefe ga ta miyar da ta wadatu da nama na tinkiyar da suka dauko jiya ga salad da su tumatir yau din bushasha za'ayi saboda jiya sun tarki sa'a. Shanun da suka dauka suna ajiye a gidan Talle ranar kasuwar dabbobi zasu kai a kwashi naira.
Da sauri Emzee ya shigo sabuwar tabarmar da ta shimfida yaran nata sun soma zama ya murtuke fuska duk da bai sansu ba "kai ku tashi"
"Yaro kai kuma daga ina?" Babban cikin nasu ya tambaya yana masa kallon raini. Ido kawai Emzee ya watsa masa yaja baya da sauri. Tsabar training sai budewa kwanjinsa yake yi musamman daga kirji, hannuwa suna murdewa irin na kakkarfan namiji. Rigar jikinsa ma kusan ta kama shi ita ta karasa tona asirin yanayin jikin nasa. Wanda ya rage akan tabarmar mai bin babban ya kalla yayi masa alamar ya tashi.
"In naki fa?"
Emzee bai sake tunani ba ya ja tabarmar ya kifar dashi a wurin ya koma gefen dakin Malamijo ya shimfide masa ita sannan ya shiga ya dauko masa filo. Radhiya dakin Yadikko tayi da sauri ta same shi a rufe da karamin kwado sai ta je na Hajjo. Nan ta tarar da komai ba yadda ta sani ba sai karajin Hajiyayye daga bayanta.
"Ke daga ina kuke ne kike leka min daki?"
Da mamaki tace "dakinki? Ina Hajjon kuma?"
Daidai nan Zayyan ya shigo da Malamijo a hannu ya kwantar dashi a inda Emzee ya nuna masa Ummi tana take masa baya hankali a tashe.
"Ku su waye ne?" Hajiyayye ta matso inda suke ta kalli Malamijo ta watsar.
Cikin salama Ummi tace mata "ni 'yarsa ce wadannan kuma yarana ne da babansu"
Tsaki taja duk da suturun jikinsu sunyi mata kwarjini amma bata so raini ya shiga tsakaninta dasu. Yadda uban yake tsoronta to kowa ma fa yaji tsoro kada a kawo mata wargi ba dauka zata yi ba.
"Me ya same Malamijon?" Tace a dakile wanda tuni ran kowa ya sosu.
"Tsorata yayi ya suma" Ummi ta bata amsa.
"uhmmm" ta tabe baki "bana son hayaniya kamar yadda shi uban naku ya sani a kiyaye"
Hayaniyar da take yi ce tasa mutanen cikin gidan suka fara lekowa ganin da wa take yi. Na'e ce kawai da wasu cikin yaran. Yadikko sun tafi asibiti da Atine guda cikin jariran babu lafiya ko ta kan Malamijo bata bi ba da zasu tafi. Ita yanzu burinta kawai Atine tayi arba'in yaran su kara kwari itama ta tafi. Shekaru sama da arba'in tana zaune tamkar sharar gidansa ta kula masa da yara ya bude baki ya fada mata magana son ransa.
Kannen Mairama da suke zawarci su biyu da sauran kannensu duk sunyi zuru zuru amma ganinta sai gasu sun fara sakin fuska suna yi musu barka da zuwa.
Hajiyayye ta wani daka musu tsawa saboda tsaurin ido "ba cewa nayi idan yaran nan sun zo cin abinci kowa ya zauna a daki ba? Ko shi Malamijon bai nanata muku ba kafin shigowarsu?"
Mayunwatan yaran kananun suka matso suna jira ta zuba musu ta kalli tabarmarta "ku shiga dakinsa akwai tabarma a bani tawa zan ciyar da yaranmu"
Zayyan da Mairama sun tsaya ne kawai kallon wannan mata mai zubin mahaukata tana ta bada umarni a gidan. Daurewa tayi ta tambayi wata kanwarta matsayinta a gidan.
"Amaryar Malamijo ce"
"Amarya kuma?" A iya saninta babu sauran wuri a gidan nasu to wa ya saka. Sai gashi kafin ta tambaya ma ta bata amsa da cewa Hajjo ya saki "Malamijo Hajjo?" Tace kamar tayi kuka.
Kanenta da suke karatu a Kano gidanta su Laila duka lokacin da suka zo kafin ta wuce Abuja tasa sun tafi hutu wurin iyayensu mata. Ta san da tuni ta sami labari a wurinsu.
Babu wanda yayi motsi da Hajiyayye tace su dauke Malamijo daga kan tabarmarta ta doki cinya tana sababi wai zai farfado ya sameta ne sai ya yiwa bakin nan bayanin matsayinta.
Abin takaicin ya ishi Zayyan zaiyi magana Ummi ta dakatar dashi ta nuna masa Radhiya da take bin matar da wani irin kallon raini
"Baki ga suma yayi bane kike zancen a baki tabarma ku ci abinci?"
"Yarinya kada kice zaki yiwa Hajiyayye rashin kunya wallahi sai na farfasa miki jiki yanzun nan a wuce wurin" babban yace a kule yunwa na cin hanjinsa an tsaya ana bata musu lokaci. Ko kadan daga uwar har yaran basu da da'a.
Sai da ya gama Radhiya ta tafi gaban kulolin da ta kula suna yiwa kallon mutumci ta bude da ta ga miya ce nama ya kusan cika ta.
"Wa ya baki izinin taba min abinci? Ke idan Malamijo ya farka zan iya sawa ya hanaku sake zuwa gidan nan"
Emzee da Ibrahim Radhiya ta nunawa kulolin da hannu tamkar ba da ita ake magana ba "bros ga fa abinda ya kawomu Sumaila kuzo mu fara aiki"
Tamkar masu jira suka je zasu dauki kulolin nan yaran Hajiyayye suka yi kukan kura tamkar mayun gaske. Duk abinda suke yi Malamijo ya farfado ya ma dan bude ido da ya ga abu ya soma kankama ya runtse kayansa ya cigaba da kwanciya. Ummi da Daada wuri suka samu suka zauna saboda abin kunya ne ace suna da su Emzee su rinka saka baki suna magana da yara irin na Hajiyayye. Ummi tana da yakinin indai da yaranta a wurin bata da matsala don ko da Radhiya kadai ta barsu ta ishesu.
Wurin ke neman kacamewa Radhiya ta kira Zayyana ta nuna mata kula daya tace ta zauna a kai itama ta zauna akan daya ta dora kafa daya kan daya. Tsagerun Hajiyayye suna son tashinsu amma yadda take kada kafa ga wasu maza a tsaye a gefe wato Emzee da Ibrahim kowa ya tamke fuska duk sai suka sha jinin jikinsu. Malamijo da yaji abin baiyi masa ba ya dan kyallo ido daya yace "Zayyan"
Uba da da ne suka amsa a tare. Wai shi Malamijo a tunaninsa ko dai Hajiyayye mayar gaske ce take son tsorata shi da fatalwar surukinsa zai daure ai ba'a san Fulani da tsoro ba ya dauke kai kamar bai ganshi ba ya cigaba da cewa Emzee "ina rundunar sauran sojojin da kace zaku zo tare?"
Ba yaran ba Hajiyayye ma sai da cikinta ya bada sauti "soja kuma"
Emzee ya sake mazewa sai lokacin ta kula da kayan jikinsa ma. Hankalinta yayi mummunan tashi kuwa a tsorace ta cewa manyan su fita zata san abinyi. Su ma da sauri suka fita din kada rundunar sojojin su iso. Tana kallo Radhiya ta kira yaran gidan suka debo kwanaku yau ko biki ake a gidan sai haka. Abincin nan tas ta rabe musu harda kwakkwafe kular bata bar ko kwayar shinkafa ba.
Zayyan kallonta yayi ya saki murmushi kawai tana kara burge shi. Haka yake kaifi daya kuma haka yake son 'ya'yansa. Kada su cuci kowa kuma kada su bari a cuce su. Bayan ta gama ta tura kular wurin wanke wanke ta dawo kusa da Malamijo ta zauna. Hajiyayye ta rasa me ya kamata ta yi saboda bacin ran da take ciki. Wannan wane irin mutane ne suka shigo gidan da yake karkashin mulkinta suna neman chaza mata kai. Kwafa tayi ta bar wurin ta tafi daki zugar yaranta suna biye da ita ana kukan nama.
Malamijo sai lokacin ya bude ido yana murmushi a hankali yadda babu mai ji sai na kusa dashi yace "Alakakai gayyar mayu daga nan ma sai gidan tsoho"
Radhiya tace masa "fadi da karfi mana taji Malamijo a haka bazata san kana yi ba"
"Barni da ita a hakan ma kun more min su. Bana so taji ne ta dawo"
"Barka da yamma Malamijo" Zayyan yace bayan yaran sun gama dariyar kalaman Malamijo.
Jikinsa ne yayi wani mugun sanyi kamar an sare masa gwiwa ya juya ya tabbatar Zayyan din ne dai yake gani kawai sai ya koma ya kwanta ya rufe idanu.
"Mairama kirawo matar nan tazo ta tsallake ni."
"Tsallakewa kamar wata mayya"
"Yo ba mayyar bace? Aure ne na kaddara na kwasowa kaina. Yanzu don bala'i ko yaya na kalli bangaren arewa maso gabashin inda kike zaune sai in rinka gane gane"
Ibrahim da Emzee ne suka fara dariya Ummi ta hararesu. Zayyan da ya gane dashi ake dole ya rike tashi dariyar a gaban suruki.
"Kamar me da me kake gani?" Radhiya ta tambayeshi tana danne dariyarta.