Sashe 126
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Salame na jin ta ce Daada hankalinta ya sake tashi don Zayyan ne mutum na karshe da zata so yasan wannan abu. Jikinta ya hau bari musamman da idanunta su ka sauka akan Alhaji Indararo da Maman Danmama. Radhiya ko a jikinta sai ma kara kwantar da murya da tayi.
"Ummi tana gidan Malamijo"
"Ke kuma kina ina?"
"Gidan Gwaggo Salame" ta fada tare da kara sautin kukan kamar lokacin ma dukanta ake yi.
Cikin fada yace "Can nace kije ko nan mijinki ya tura ki?"
"Kiji tsoron Allah Radhiya me nayi miki kike kara kuka haka" Salame tayi maganar tana komawa kalar tausayi sosai.
Shi kuwa Zayyan kukan 'yarsa har kokon ransa yake jinsa. Lallabata ya koma yi don yaji me ya faru "Alheran dena kukan ko waye ya taba min ke ba kyalewa zanyi ba"
Ba kunya ta sakarwa Salame murmushi sannan tasa speaker ta kure volume din wayar "Daada dukana tayi da wayar rediyo fatar bayana ta cire..."
"Laaaaahhhh kuji min yarinya...ba Rahima nazo duka ba kika tare? Ni ina ruwana da 'ya'yan gidanku me zai kaini dukanku...." idanunta har sun fara tara kwalla saboda wani sauyin numfashi da take iya jiyowa na Zayyan ransa ya soma baci.
"Wai don na gane ashe tana sonka kuma ita ta makanta Ummi don ta auri Alha...."
Salame kasa hakuri tayi tasa hannu ta toshe bakin Radhiya saboda yadda Zayyan yace "ME???" da karfi.
Alh Indararo yana jin haka shi kuma ya wawurota ji kake tas-tas ya tsittsinka mata mari. Zayyan da ya zata tasa 'yar ake duka a kidime ya kashe wayar ya kira Mairama.
Baiwar Allah bata san me ake yi ba tana tare dasu Innawuro ana hira ta dauka. Abinda bata taba ji ba wato Zayyan ya daga mata murya taji a yau. Zai iya hakuri da komai banda taba masa 'ya'ya ba kuma wai don bashi da kara ba sai don yasan wacece Salame a da lokacin da bata ji kunyar kai masa kokon barar soyayya ba alhali yana neman kanwarta. Abu na biyu kuwa bai wuce shekarun da ya kwasa cike da tsananin kewar iyalinsa. Yanzu da ya sami dama ta biyu ba zaiyi wasa da ita yana ji yana gani 'ya'yansa suna zubar da hawaye ba. Bashi da uwa ba uba sai mata sai su. Baya fata amma ya sani ana chanja mata amma jininsa bazai iya taba chanja shi ba.
"Kije gidan yayarki Salame ki dauko min Alheran sannan gobe zanzo na dauketa mu koma gida"
Tashi tayi ta matsa daga cikin mutane hankali a tashe "Sojana ban fahimceka ba"
"Nima ban fahimta ba Fillo.."yace cike da damuwa "Alheran ta kirani yanzu wai Salame tana dukanta da wayar rediyo...."
Ko karshen zancen bata tsaya ji ba ta koma ciki da sauri danunta sun kada sunyi ja. Nanatawa take yi yau ko ita ko Salame...ta gaji da wannan halayya da take nuna mata. Rahima ma a yanzu ba bari zata yi ta tabata ba bare kuma Radhiyanta. Wani dauke kai da take yi akanta ba shine yake nufin bata son abarta ba. Bata hada son 'ya'yanta da komai sai dai sanin rayuwa da kyaun hali yasa bata sangartasu da soyayya ba.
"Mairama ina zaki haka lokaci guda kin fita hayyacinki" cewar Yadikko tana tasowa ta riketa.
"Gidan Salame zani Yadikko. Kuzo muje kuyi shaida ayi min tsakani da ita domin na rantse zan nuna mata duk abinda nake yi ba wai rashin sanin ciwon kai bane. Idan zumunci dani ne bata so a yau ni da kaina zansa wuka na datse shi uban kowa ma ya huta"
Mama cire DK tayi da take shayarwa ta mikawa Laila ta dafa Mairama "kiyi hakuri ki fadi me tayi miki"
Kowa ya ga Mairama yasan tana cikin bacin rai dama ga ta da zuciya. Hakurinta da yawan kau da kai shine yake sawa a ga kamar bata da fushi.
"Babansu Karami ya kirani yanzu wai Salame tana dukan wannan yarinya da wayar rediyo"
"Me kika ce?" Malamijo yace da sauri yana nufosu. Hayaniya yake ji har soro shine ya fito.
Cikin kankanin lokaci Malamijo, Nene Marka, Yadikko da Hajjo su ka hadu da Mairama zasu tafi gidan Salame kowa ya kasa gane me yake faruwa. Mairama ta kira Radhiya amma tana dauka kuka kawai ta rinka yi bata ce komai ba. Zasu fita ta ga Mama Zainab a tsaye bata da niyar binsu.
"Yanzun nan in fada miki ana dukan 'yarki amma ki tsaya a nan Zainab" cewar Mairama.
Gani tayi abin ya shafi danginsu bai dace ta tura kai ba "Kuje ku dawo Ummin Awwab"
Fushin nata kan Mama ya nemi komawa tana ta kumburi tace "kada kije din...kuma sai na fadawa Mami" fuuuu tayi gaba tana sababin da babu wanda ya santa dashi.
Nene Marka tace "maza Zainabu dauko mayafinki wannan 'yar uwar taki bata iya fushi ba ko kadan"
Duk da babu nisa motar Mairama suka shiga sabo mutane dreba ya ja su.
**********
Bayan marin da Alh Indararo ya rinka saukewa Salame zuciyarsa a sama har yana haki ya nuna ta yatsa "naji komai kuma nasan komai. Sai yau na fahimci yaya akayi na aureki Salame"
Radhiya gefe ta koma abinta bayanta na zugi tana jiran isowar su Ummi saboda Daada yace ta jira gasu nan zuwa.
Kuka yaki zuwar wa Salame sai kumatunta duka biyun da ta rike zugi da radadi na shigarta.
Cigaba yayi da fadansa sa'arsu daya babu yara a gidan kamar anyi shara. Dama na Salame ne masu zama su ma yau Radhiya tayi musu jan ido babu ko daya.
"Lallai biri yayi kama da mutum. Salame ko ina shan giya me zai kaini aurenki bayan tun kina gidan Idris na sanki. Sau nawa nake bawa matana labarin yadda yake zuwa wurina neman bashi saboda ya auri hatsabibiyar mata mai bani-bani wadda ta raina shi. Kinsan talaka ne amma kike amfani da son da yake miki kika tatike shi. Ranar da zaki haifi Rahima ma idan baki sani ba ni na bashi aron mota aka kaiki asibiti. Sannan ragon suna da kika matsanta masa shima bashi ya nema a wurina sai da ya shekara uku ya iya hada min kudin ragon."
"Alhaji me ya kawo wannan tone-tonen? Kada kace ka yarda da zancen yarinyar..."
Mugun kallon da ya jefa mata yasa ta koma tayi lakwas "Salame kyan dan maciji asirinki ya tonu" ya nuna Maman Danmama "ga uwargidana nan ki tambayeta ko da Mairama ta makance nan nazo na fada musu matar da zan aura ta sami matsalar ido kuma tana da marayu. Idan ta tare duk wadda ta cutar da ita a bakin aurenta. Amma duk wannan abu lokaci guda naji zan iya rabuwa da kowa a kanki Salame. To albishirinki aikin boka yayi ci da kyau domin ke da gidan nan sai dai kiyi min takaba ko a fitar da gawarki. Kinzo kenan 'yar kundun uba"
Wayar da ta gama dukan su Rahima da ita ya dauko daga kan kujera ya daga kawai ya shiga lafta mata. Saukar farko Salame ta zabura za tayi rawar 'yan bori. Ashe ba dadi ta sa matar da ya saki karshe sai da yayi mata dukan kawo wuka kawai saboda ta dakar mata 'ya. Dukan da yake mata ya soma firgita Radhiya da uwargidansa duk haushinta da suke ji Radhiya sai ta sami kanta da janyo Salame bayanta yayin da Maman Danmama ta rike hannun Alhajin yana ta kumfar baka yana masifa kamar ya ari baki.
Numfarfashi Salame take saukewa su ka ji sallama daga waje wadda mai yinta ko ba'a fada ba yana cikin bacin rai ne da fushi. Ba'a dena sallamar ba cikin daga murya tare da dukan kofar gidan a fusace.
Alh Indararo shima cikin bacin rai ya fita yaci karo da Idris rungume da 'yarsa Rahima idonta daya ya kumbura ga shatin waya yayi bororo a rabin fuskarta har wurin idon da samansa.
Mutum mai hakuri ba sawa ba fitarwa irin Baffan Rahima yau shima an kure shi karshe ko gaisawa basuyi ba ya soma fada "Billahillazi huwar Rahmanu Alhaji ka gargadi matarka idan ba haka ba zan tube rigar mutumci in shiga har cikin gidan nan inci mutumcinta. Dubi wannan diban albarka da ta yiwa Rahima. Yau yarinyar nan ko zaman kishi suka yi da uwarta a yanzu da babu aure a tsakaninmu bata cancanci wannan abu ba bare kuma 'yar cikinta."
Saukowa Alh Indararo yayi saboda yadda yarinyar ta bashi tausayi "dakata muyi magana Baban Rahima"
"Wace irin dakatawa zanyi? Kullum da fargaba da komai ni ko Iya muke matsanta mata tazo gidannan saboda uwa uwace komai lalacewarta. Babu ranar da Rahima bazata dawo min gida da hawaye ba amma yau ka duba ka gani don Allah. Dubi yadda fuskarta ta koma daga zuwanta"
Motar su Mairama ce ta tsaya suka firfito gabadayansu. Kafin su karaso Rahima ta kwasa a guje ta rungumeta tana kuka mai ban tausayi. Hajjo ce ta fara ganin fuskar ta dago kanta da sauri. Mairama ma ta gani a tsorace tace "meye wannan Rahima?"
"Umma ce ta dakeni"
Mairama cije lebenta kawai tayi ta damki hannun Rahima ko Alh Indararo da Baffan Rahiman bata tsaya yiwa kwakkwaran kallo ba ta shige cikin gidan tana cewa "SALAME kina ina?".
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Washegari kafin a kira assalatu Emzee ya gama shirinsa. Ana kiran sallah yayi tare da Daada a nan wurin masu gadi sannan yace zai tafi.
"Ba ka ci komai ba Zayyan, Umminka bazata ji dadi ba"
Agogonsa ya kalla "Daada so nake kafin 9 ina cikin NDA in sha Allah"
Addu'a da fatan alkhairi Zayyan ya yiwa dansa suna jiran karasowar Ibrahim ya kaishi tasha saboda ba a gidan ya kwana ba. Kan wasu kujeru masu kyau daga gefen kofa suka zauna suna hira irin ta uba da da gwanin ban sha'awa. Ummi ce ta fito sanye da hijabi akan doguwar rigar baccinta da ta daura zani ta ciki da tray yana ta turiri ta taho inda suke.
"Inata saurin kada ka tafi ba ka ci komai ba. Ungo kuma ban yarda ka rage ba"
Indomie ce guda biyu da daffafen kwai biyu sai kofin orange juice mai sanyi. Tasan halinsa baya shan abu mai zafi da safe sai dare.
"Ummi tana gidan Malamijo"
"Ke kuma kina ina?"
"Gidan Gwaggo Salame" ta fada tare da kara sautin kukan kamar lokacin ma dukanta ake yi.
Cikin fada yace "Can nace kije ko nan mijinki ya tura ki?"
"Kiji tsoron Allah Radhiya me nayi miki kike kara kuka haka" Salame tayi maganar tana komawa kalar tausayi sosai.
Shi kuwa Zayyan kukan 'yarsa har kokon ransa yake jinsa. Lallabata ya koma yi don yaji me ya faru "Alheran dena kukan ko waye ya taba min ke ba kyalewa zanyi ba"
Ba kunya ta sakarwa Salame murmushi sannan tasa speaker ta kure volume din wayar "Daada dukana tayi da wayar rediyo fatar bayana ta cire..."
"Laaaaahhhh kuji min yarinya...ba Rahima nazo duka ba kika tare? Ni ina ruwana da 'ya'yan gidanku me zai kaini dukanku...." idanunta har sun fara tara kwalla saboda wani sauyin numfashi da take iya jiyowa na Zayyan ransa ya soma baci.
"Wai don na gane ashe tana sonka kuma ita ta makanta Ummi don ta auri Alha...."
Salame kasa hakuri tayi tasa hannu ta toshe bakin Radhiya saboda yadda Zayyan yace "ME???" da karfi.
Alh Indararo yana jin haka shi kuma ya wawurota ji kake tas-tas ya tsittsinka mata mari. Zayyan da ya zata tasa 'yar ake duka a kidime ya kashe wayar ya kira Mairama.
Baiwar Allah bata san me ake yi ba tana tare dasu Innawuro ana hira ta dauka. Abinda bata taba ji ba wato Zayyan ya daga mata murya taji a yau. Zai iya hakuri da komai banda taba masa 'ya'ya ba kuma wai don bashi da kara ba sai don yasan wacece Salame a da lokacin da bata ji kunyar kai masa kokon barar soyayya ba alhali yana neman kanwarta. Abu na biyu kuwa bai wuce shekarun da ya kwasa cike da tsananin kewar iyalinsa. Yanzu da ya sami dama ta biyu ba zaiyi wasa da ita yana ji yana gani 'ya'yansa suna zubar da hawaye ba. Bashi da uwa ba uba sai mata sai su. Baya fata amma ya sani ana chanja mata amma jininsa bazai iya taba chanja shi ba.
"Kije gidan yayarki Salame ki dauko min Alheran sannan gobe zanzo na dauketa mu koma gida"
Tashi tayi ta matsa daga cikin mutane hankali a tashe "Sojana ban fahimceka ba"
"Nima ban fahimta ba Fillo.."yace cike da damuwa "Alheran ta kirani yanzu wai Salame tana dukanta da wayar rediyo...."
Ko karshen zancen bata tsaya ji ba ta koma ciki da sauri danunta sun kada sunyi ja. Nanatawa take yi yau ko ita ko Salame...ta gaji da wannan halayya da take nuna mata. Rahima ma a yanzu ba bari zata yi ta tabata ba bare kuma Radhiyanta. Wani dauke kai da take yi akanta ba shine yake nufin bata son abarta ba. Bata hada son 'ya'yanta da komai sai dai sanin rayuwa da kyaun hali yasa bata sangartasu da soyayya ba.
"Mairama ina zaki haka lokaci guda kin fita hayyacinki" cewar Yadikko tana tasowa ta riketa.
"Gidan Salame zani Yadikko. Kuzo muje kuyi shaida ayi min tsakani da ita domin na rantse zan nuna mata duk abinda nake yi ba wai rashin sanin ciwon kai bane. Idan zumunci dani ne bata so a yau ni da kaina zansa wuka na datse shi uban kowa ma ya huta"
Mama cire DK tayi da take shayarwa ta mikawa Laila ta dafa Mairama "kiyi hakuri ki fadi me tayi miki"
Kowa ya ga Mairama yasan tana cikin bacin rai dama ga ta da zuciya. Hakurinta da yawan kau da kai shine yake sawa a ga kamar bata da fushi.
"Babansu Karami ya kirani yanzu wai Salame tana dukan wannan yarinya da wayar rediyo"
"Me kika ce?" Malamijo yace da sauri yana nufosu. Hayaniya yake ji har soro shine ya fito.
Cikin kankanin lokaci Malamijo, Nene Marka, Yadikko da Hajjo su ka hadu da Mairama zasu tafi gidan Salame kowa ya kasa gane me yake faruwa. Mairama ta kira Radhiya amma tana dauka kuka kawai ta rinka yi bata ce komai ba. Zasu fita ta ga Mama Zainab a tsaye bata da niyar binsu.
"Yanzun nan in fada miki ana dukan 'yarki amma ki tsaya a nan Zainab" cewar Mairama.
Gani tayi abin ya shafi danginsu bai dace ta tura kai ba "Kuje ku dawo Ummin Awwab"
Fushin nata kan Mama ya nemi komawa tana ta kumburi tace "kada kije din...kuma sai na fadawa Mami" fuuuu tayi gaba tana sababin da babu wanda ya santa dashi.
Nene Marka tace "maza Zainabu dauko mayafinki wannan 'yar uwar taki bata iya fushi ba ko kadan"
Duk da babu nisa motar Mairama suka shiga sabo mutane dreba ya ja su.
**********
Bayan marin da Alh Indararo ya rinka saukewa Salame zuciyarsa a sama har yana haki ya nuna ta yatsa "naji komai kuma nasan komai. Sai yau na fahimci yaya akayi na aureki Salame"
Radhiya gefe ta koma abinta bayanta na zugi tana jiran isowar su Ummi saboda Daada yace ta jira gasu nan zuwa.
Kuka yaki zuwar wa Salame sai kumatunta duka biyun da ta rike zugi da radadi na shigarta.
Cigaba yayi da fadansa sa'arsu daya babu yara a gidan kamar anyi shara. Dama na Salame ne masu zama su ma yau Radhiya tayi musu jan ido babu ko daya.
"Lallai biri yayi kama da mutum. Salame ko ina shan giya me zai kaini aurenki bayan tun kina gidan Idris na sanki. Sau nawa nake bawa matana labarin yadda yake zuwa wurina neman bashi saboda ya auri hatsabibiyar mata mai bani-bani wadda ta raina shi. Kinsan talaka ne amma kike amfani da son da yake miki kika tatike shi. Ranar da zaki haifi Rahima ma idan baki sani ba ni na bashi aron mota aka kaiki asibiti. Sannan ragon suna da kika matsanta masa shima bashi ya nema a wurina sai da ya shekara uku ya iya hada min kudin ragon."
"Alhaji me ya kawo wannan tone-tonen? Kada kace ka yarda da zancen yarinyar..."
Mugun kallon da ya jefa mata yasa ta koma tayi lakwas "Salame kyan dan maciji asirinki ya tonu" ya nuna Maman Danmama "ga uwargidana nan ki tambayeta ko da Mairama ta makance nan nazo na fada musu matar da zan aura ta sami matsalar ido kuma tana da marayu. Idan ta tare duk wadda ta cutar da ita a bakin aurenta. Amma duk wannan abu lokaci guda naji zan iya rabuwa da kowa a kanki Salame. To albishirinki aikin boka yayi ci da kyau domin ke da gidan nan sai dai kiyi min takaba ko a fitar da gawarki. Kinzo kenan 'yar kundun uba"
Wayar da ta gama dukan su Rahima da ita ya dauko daga kan kujera ya daga kawai ya shiga lafta mata. Saukar farko Salame ta zabura za tayi rawar 'yan bori. Ashe ba dadi ta sa matar da ya saki karshe sai da yayi mata dukan kawo wuka kawai saboda ta dakar mata 'ya. Dukan da yake mata ya soma firgita Radhiya da uwargidansa duk haushinta da suke ji Radhiya sai ta sami kanta da janyo Salame bayanta yayin da Maman Danmama ta rike hannun Alhajin yana ta kumfar baka yana masifa kamar ya ari baki.
Numfarfashi Salame take saukewa su ka ji sallama daga waje wadda mai yinta ko ba'a fada ba yana cikin bacin rai ne da fushi. Ba'a dena sallamar ba cikin daga murya tare da dukan kofar gidan a fusace.
Alh Indararo shima cikin bacin rai ya fita yaci karo da Idris rungume da 'yarsa Rahima idonta daya ya kumbura ga shatin waya yayi bororo a rabin fuskarta har wurin idon da samansa.
Mutum mai hakuri ba sawa ba fitarwa irin Baffan Rahima yau shima an kure shi karshe ko gaisawa basuyi ba ya soma fada "Billahillazi huwar Rahmanu Alhaji ka gargadi matarka idan ba haka ba zan tube rigar mutumci in shiga har cikin gidan nan inci mutumcinta. Dubi wannan diban albarka da ta yiwa Rahima. Yau yarinyar nan ko zaman kishi suka yi da uwarta a yanzu da babu aure a tsakaninmu bata cancanci wannan abu ba bare kuma 'yar cikinta."
Saukowa Alh Indararo yayi saboda yadda yarinyar ta bashi tausayi "dakata muyi magana Baban Rahima"
"Wace irin dakatawa zanyi? Kullum da fargaba da komai ni ko Iya muke matsanta mata tazo gidannan saboda uwa uwace komai lalacewarta. Babu ranar da Rahima bazata dawo min gida da hawaye ba amma yau ka duba ka gani don Allah. Dubi yadda fuskarta ta koma daga zuwanta"
Motar su Mairama ce ta tsaya suka firfito gabadayansu. Kafin su karaso Rahima ta kwasa a guje ta rungumeta tana kuka mai ban tausayi. Hajjo ce ta fara ganin fuskar ta dago kanta da sauri. Mairama ma ta gani a tsorace tace "meye wannan Rahima?"
"Umma ce ta dakeni"
Mairama cije lebenta kawai tayi ta damki hannun Rahima ko Alh Indararo da Baffan Rahiman bata tsaya yiwa kwakkwaran kallo ba ta shige cikin gidan tana cewa "SALAME kina ina?".
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Washegari kafin a kira assalatu Emzee ya gama shirinsa. Ana kiran sallah yayi tare da Daada a nan wurin masu gadi sannan yace zai tafi.
"Ba ka ci komai ba Zayyan, Umminka bazata ji dadi ba"
Agogonsa ya kalla "Daada so nake kafin 9 ina cikin NDA in sha Allah"
Addu'a da fatan alkhairi Zayyan ya yiwa dansa suna jiran karasowar Ibrahim ya kaishi tasha saboda ba a gidan ya kwana ba. Kan wasu kujeru masu kyau daga gefen kofa suka zauna suna hira irin ta uba da da gwanin ban sha'awa. Ummi ce ta fito sanye da hijabi akan doguwar rigar baccinta da ta daura zani ta ciki da tray yana ta turiri ta taho inda suke.
"Inata saurin kada ka tafi ba ka ci komai ba. Ungo kuma ban yarda ka rage ba"
Indomie ce guda biyu da daffafen kwai biyu sai kofin orange juice mai sanyi. Tasan halinsa baya shan abu mai zafi da safe sai dare.