Sashe 30
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da safe Musa da kansa ya sanar da su Aisha cewa mamansu zata dawo sannan Antinsu Zainab zata tafi. Sun saba da ita sosai a hannunta suka girma. Tana kuka suna kuka har airport suka rakata. Motarta Musa yace zai bayar a kawo mata har gida. Tayi ta masa godiya da kyakkyawar addu'a ta shige jirgi zuwa garinsu tana mai fatan samun sauyin rayuwa mai dadi.
**********
A firgice Rtd Major Mustapha ya tashi jike da gumi daga mafarkin da yake yawan yi wanda yake daga masa hankali ya shiga laluben kafar katakonsa. Mafarkin ya tsananta a gareshi tun bayan da suka sanya ranar komawa kasar haihuwarsu. Korido din da zai sada shi da kitchen ya nufa don ya sha ruwa ya hango Mami ta barbaza kaya a gabanta na tsaraba da take ta warewa tana saka sunaye.
Kasa tafiya yayi duk motsinta yake bi da kallo. Wannan kyakkyawar matar kanwarsa ce, matarsa kuma uwar 'ya'yansa. Hakika a kullum baya gajiya da sanya Hassana cikin addu'o'insa domin ta cancanci fiye da haka. Tayi hakuri dashi iyakar hakuri musamman a lokutan da yake ganiyar ciwo har yakan nemi rayuwarta ba a cikin hayyacinsa ba. Tunanin kawai kan sa tsigar jikinsa tashi. Tabo uku ne a jikin Mami wanda suka samu a dalilin PTSD dinsa.
Jikinta ya bata yana kallonta haka kawai, ta daga kai suka hada ido. Murmushi suka yiwa juna ya dawo falon ya zauna.
"Me ya hanaki bacci shabiyu har ta wuce?"
"Aikin nan yaki karewa Daddy. List din mutanen ma kamar bamu yi rabi ba" ta dan bata rai.
"Ku kuma mata da baku da nutsuwa indai akan tsaraba ne ko"
Tattara kayan ta soma yi gefe sannan ta dube shi "me ya tasheka ne?"
Shirunsa ya fahimtar da ita komai. Kusa dashi taje ta zauna "nan da kwanaki goma in sha Allah muna gida. Muna kwana biyu an gama gaisawa da 'yan uwa babu inda zamu je sai wurin Ummin Awwab da Hadir. Lokaci yayi da zaka kore komai daga ranka ka rungumi kaddara."
"Yes Ma" yace yana murmushi.
Maida masa martanin murmushin tayi ita ma "Tashi muje mu kwanta kasan gobe is a big day"
Suna kwance tuni Mami tayi bacci amma shi ya kasa sai rarraba dayan biyu yake. Ko yaya iyalin Zayyan? Allah Yasa suna cikin mafi kyaun yanayi. Sai kuma ya koma tunanin auren Zahra da Fauziyya da za'ayi nan da wata biyu. Kowaccensu tuni ta hada degree dinta. Hadi ne na gida zasu auri 'ya'yan 'yan uwa kamar yadda ya kusan zamewa danginsu al'ada. Har nan aka turo mazan suka daidaita kawunansu. Bai san lokacin da bacci yayi awon gaba dashi ba.
Washegari kuwa banda shirin tafiyarsu da yaki karewa karfe bakwai na dare suka tasarma gidan da Mami take aiki. Major sanye yake sa suit sky blue da light grey din shirt a ciki. Yayi gyaran fuska yayi kyau yana rike da sandarsa da take taimakawa wurin rage masa rashin jindadin tafiya da kafar katako duk da ya saba yanzu.
Mami, Zahra, Fauziyya da Zayyana duka abaya ne a jikinsu masu kyau kowacce tayi nadi da mayafin da ya dace.
Party ne na bankwana iyalin Herr(Mr) da Frau(Mrs) Schmidt suka shiryawa Mami a matsayinta na shugabar ma'aikatan katon gidan. Sun matukar jindadin zama da ita tun lokacin da suka basu wuri a gidansu kafin daga baya su kama wani mai dan girma a waje. Iyalin babu abinda yasa suka likewa Mami kamar tsantsar tarbiyar da yaransu suke koyi da ita har a makarantunsu. Tarbiya ce irin ta musulunci batare da ta fito zahiri ta tallata musu addinin ba. A fakaice ta rinka kwadaita musu tana fatan wataran idan da rabo su karba. Farkon zuwanta sun so hanata zuwa da lullubi ko karamin hijab. A take tace ta bar aikin. To amma amanar da suke gani daga gareta yasa da kansu suka sake nemota.
Aikin Mami a gidan yana daga cikin abinda Major bazai taba mantawa a rayuwarsa ba. Wai shi Mustapha da ya kai matakin Major a soja shine matarsa take aikatau. Abinda yafi karfi a kasarsu yazo lalura ta cinye komai nasa yafi karfinsa. Bashi da tamkarta a duk duniya. Ya amince samun kamarta sai wata matar sojan. Jarumar mace matar jarumin namiji.
Katuwar harabar gidan tasha gyara da fitilu da flowers ko ina yana kyalli ga kayan abinci a gefe debi wanda kake so.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Max, Anna da Liam sune 'ya'yan da suka tashi a hannun Mami. Suna ganin shigowarsu lawn din suka taho suna murna. Idanun Anna jazur taci kuka tun safe take abu daya.
Rungume Mami tayi "bana so ki tafi Naanaa" tace cikin yaren jamusanci.
Da yaren Mami ta maida mata "kiyi hakuri Anna, watarana zan zo ziyara ko ke kizo mana Nigeria ko"
"Zaki zo aurena next year?"
"In sha Allah"
Hawaye Anna take ta rinka sumbatar kumatun Mami ita kuwa sai dariya. Liam da Max hannuwanta suka rike suka kaita tsakiyar wurin suna nunawa jama'a Naanaa dinsu. Mai aiki ce amma wadda take a inda aka san darajar masu aiki har masu gida suke karrama su.
Ta sami kyaututtuka da yawa daga abokan aikinta da abokan arziki.
Frau Marie Schmidt ta kawo envelop da kudi a ciki ta bata sannan ta bawa Fauziyya da Zahra wasu setin dankunne da sarka 'yan ubansu wai su saka da bikinsu. Zayyana ma an bata katon teddy kusan kansu daya. Tana ta murna Mami a ranta tayi dariya kawai. 'Yan kasarmu ina muka wani san darajar teddy.
Hotunan tarihi suke dauka Major ya daga waya yana fadin inda suke. Ko minti biyu ba'ayi ba sai ga matashin saurayi kyakkyawa wankan tarwada mai cike da kwarjini da haiba ya shigo wurin sanye da uniform dinsa na matukin jirgin KLM mallakar kasar Germany. Jacket da wando ne navy blue sai farar shirt a ciki kansa sanye da hula irin ta Captain din jirgi. Mata hudu ne a gefensa hagu da dama air hostess kowacce da uniform riga da skirt sky blue suna rike da flowers masu kyau.
Shigowar tasu ta kayatar da mutanen wurin bare iyayensa. Yana shigowa kai tsaye wurin Major ya nufa ya rungume shi. Mami ta saki baki sai kuma ta daure fuska cikin wasa.
"Awwab, yau din ma?"
Sai da yayi mata dariya sannan ya rungume Maminsa a kunnenta yana cewa "sorry Mamina"
'Yan matan da suke abokan aikinsa kowacce ta mika mata flower da dan gift suna mata fatan alkhairi.
Awwab ya fiddo tickets biyar daga aljihun sa ya mikawa Major.
"Daddy ga nawa gift din...Captain M.A Mustapha shine zai ja jirginku zuwa birnin Abuja. Sai da na duba schedule dina na sayi ticket. Tafiya ta dawo nan da sati biyu. I hope it is okay"
Zayyana tayi tsalle ta dane shi tana ihun murna. Mami sai murmushi kawai na jindadi. Major kuwa tsokanarsa yake yi wai bazai shiga ba kada ya zubar dasu a teku.
An gama party lafiya suka koma gida tare dashi. Shirye shirye ya kankama inda suka hada ya nasu ya nasu sai gida Nigeria.
***********
Iyayen Zainab sun sakata a gaba kowa da abinda yake cewa tun da ta sanar musu cewa a yiwa iyayen Hadir magana akan aurensu.
"Wai shin idan kin koma soyayya zaki rinka zuba muku a kwano kuna ci? Ke ba aiki shi a zaune. Ni har yau ban gamsu da ba ke kika kashewa kanki aure ba" mamanta tace a hasale.
Babanta ne ma mai dan sauki a gareta "Zainab nasan kila ko a wurin Ibrahim kina ji cewa jikin Hadir babu wani sauki sai na musulunci. Kinje kin shafe shekaru tare da Musa kin saba da jindadi. Ta ina zaki koma gidansu?"
"Baba na fada muku ya bani gida a Kano sannan ya kara min jari akan wanda ya bani tun da nake zuwa Dubai saro kaya dashi. Alhamdulillah Allah Ya wadatani Abbansu Aisha ne sila. Ni zan cigaba da tafiya kasuwancina ne Ibrahim ya rinka kula dashi idan bana nan"
Mamanta ta kara kulewa "sannu uwar tsari, waro har kin gama tsara yadda komai zai kasance"
Allah Ya sani tana son iyayenta kuma tana girmama su. Amma wannan karon tana jin tayi girman da ya kamata a karbi uzurinta idan tazo dashi.
"Idan ba kwa so na komawa Hadir bazan koma ba. Amma wallahi bazan kara aure ba har na mutu"
Tsam ta tashi daga dakin Baban nata. Sun san Zainab da taurin kai. Anyi sa'a ma zamanta da Musa Allah Yayi da tsayin kwana. Tufka suke da warwara suna guje mata matsala a gaba. Karshe mahaifinta yace su barta Allah kadai Yasan dalilin wannan soyayya da take yi masa.
Bayan kwanaki ana muhawara da 'yan uwa babanta da kansa yaje Kano da dan uwansa ya gabatarwa Baban Hadir bukatarsu. Sunyi matukar mamaki ace har yanzu Zainab tana son dansu. Matar da sun sani yanzu ita dashi kamar wutsiyar rakumi ne da kasa. Daga irin suturun da take yiwa Ibrahim da abubuwan zamani da take wadata shi dasu zaka san Haj Zainab take don tayi Hajji da Umara albarkacin Musa.
"Idan na fadawa Hadir bazai yarda ya aureta ba saboda lalurarsa" Babansa ya amsa musu a sanyaye. Hadir ya riga ya karbi kaddarar rayuwarsa.
"Sai kayi shiru mu kulla abinmu a tsakaninmu ba shikenan ba" Kawun Zainab ya bashi amsa.
Da izinin Allah a ranar basu tashi ba sai da aka mayar da auren Zainab jaruma mai sadaukarwa da Hadir jarumin kasata da kasar ta dade da mantawa dashi.
Da aka kirata da wannan kyakkyawan labari tayi kukan farinciki sosai. Sati daya aka diba tariya inda Baba ya sa Ibrahim ya kwashe kayan sawarsu ya rinka maidawa gidanta da yake Janbulo. Hadir yana kallo bai iya tambaya sai ya sawa ransa ko gyara za'ayi a dakin.
**********
"Wayyo Innawuro, kiyi min rai....Ummiiiii ki ceceni"
Ihun Radhiya kenan da ya karade gidan tana zaune Emzee ya danneta Innawuro zata yi mata aski.
Mairama hakuri take bata akan ta bari ayi "idan ba'a magance kwarkwatar nan ba wallahi duka sai kin shafa mana. Har na gama makarantar kwana ni banyi ba. Ku baku iya kula da kanku sai kazanta da gayun banza"
**********
A firgice Rtd Major Mustapha ya tashi jike da gumi daga mafarkin da yake yawan yi wanda yake daga masa hankali ya shiga laluben kafar katakonsa. Mafarkin ya tsananta a gareshi tun bayan da suka sanya ranar komawa kasar haihuwarsu. Korido din da zai sada shi da kitchen ya nufa don ya sha ruwa ya hango Mami ta barbaza kaya a gabanta na tsaraba da take ta warewa tana saka sunaye.
Kasa tafiya yayi duk motsinta yake bi da kallo. Wannan kyakkyawar matar kanwarsa ce, matarsa kuma uwar 'ya'yansa. Hakika a kullum baya gajiya da sanya Hassana cikin addu'o'insa domin ta cancanci fiye da haka. Tayi hakuri dashi iyakar hakuri musamman a lokutan da yake ganiyar ciwo har yakan nemi rayuwarta ba a cikin hayyacinsa ba. Tunanin kawai kan sa tsigar jikinsa tashi. Tabo uku ne a jikin Mami wanda suka samu a dalilin PTSD dinsa.
Jikinta ya bata yana kallonta haka kawai, ta daga kai suka hada ido. Murmushi suka yiwa juna ya dawo falon ya zauna.
"Me ya hanaki bacci shabiyu har ta wuce?"
"Aikin nan yaki karewa Daddy. List din mutanen ma kamar bamu yi rabi ba" ta dan bata rai.
"Ku kuma mata da baku da nutsuwa indai akan tsaraba ne ko"
Tattara kayan ta soma yi gefe sannan ta dube shi "me ya tasheka ne?"
Shirunsa ya fahimtar da ita komai. Kusa dashi taje ta zauna "nan da kwanaki goma in sha Allah muna gida. Muna kwana biyu an gama gaisawa da 'yan uwa babu inda zamu je sai wurin Ummin Awwab da Hadir. Lokaci yayi da zaka kore komai daga ranka ka rungumi kaddara."
"Yes Ma" yace yana murmushi.
Maida masa martanin murmushin tayi ita ma "Tashi muje mu kwanta kasan gobe is a big day"
Suna kwance tuni Mami tayi bacci amma shi ya kasa sai rarraba dayan biyu yake. Ko yaya iyalin Zayyan? Allah Yasa suna cikin mafi kyaun yanayi. Sai kuma ya koma tunanin auren Zahra da Fauziyya da za'ayi nan da wata biyu. Kowaccensu tuni ta hada degree dinta. Hadi ne na gida zasu auri 'ya'yan 'yan uwa kamar yadda ya kusan zamewa danginsu al'ada. Har nan aka turo mazan suka daidaita kawunansu. Bai san lokacin da bacci yayi awon gaba dashi ba.
Washegari kuwa banda shirin tafiyarsu da yaki karewa karfe bakwai na dare suka tasarma gidan da Mami take aiki. Major sanye yake sa suit sky blue da light grey din shirt a ciki. Yayi gyaran fuska yayi kyau yana rike da sandarsa da take taimakawa wurin rage masa rashin jindadin tafiya da kafar katako duk da ya saba yanzu.
Mami, Zahra, Fauziyya da Zayyana duka abaya ne a jikinsu masu kyau kowacce tayi nadi da mayafin da ya dace.
Party ne na bankwana iyalin Herr(Mr) da Frau(Mrs) Schmidt suka shiryawa Mami a matsayinta na shugabar ma'aikatan katon gidan. Sun matukar jindadin zama da ita tun lokacin da suka basu wuri a gidansu kafin daga baya su kama wani mai dan girma a waje. Iyalin babu abinda yasa suka likewa Mami kamar tsantsar tarbiyar da yaransu suke koyi da ita har a makarantunsu. Tarbiya ce irin ta musulunci batare da ta fito zahiri ta tallata musu addinin ba. A fakaice ta rinka kwadaita musu tana fatan wataran idan da rabo su karba. Farkon zuwanta sun so hanata zuwa da lullubi ko karamin hijab. A take tace ta bar aikin. To amma amanar da suke gani daga gareta yasa da kansu suka sake nemota.
Aikin Mami a gidan yana daga cikin abinda Major bazai taba mantawa a rayuwarsa ba. Wai shi Mustapha da ya kai matakin Major a soja shine matarsa take aikatau. Abinda yafi karfi a kasarsu yazo lalura ta cinye komai nasa yafi karfinsa. Bashi da tamkarta a duk duniya. Ya amince samun kamarta sai wata matar sojan. Jarumar mace matar jarumin namiji.
Katuwar harabar gidan tasha gyara da fitilu da flowers ko ina yana kyalli ga kayan abinci a gefe debi wanda kake so.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Max, Anna da Liam sune 'ya'yan da suka tashi a hannun Mami. Suna ganin shigowarsu lawn din suka taho suna murna. Idanun Anna jazur taci kuka tun safe take abu daya.
Rungume Mami tayi "bana so ki tafi Naanaa" tace cikin yaren jamusanci.
Da yaren Mami ta maida mata "kiyi hakuri Anna, watarana zan zo ziyara ko ke kizo mana Nigeria ko"
"Zaki zo aurena next year?"
"In sha Allah"
Hawaye Anna take ta rinka sumbatar kumatun Mami ita kuwa sai dariya. Liam da Max hannuwanta suka rike suka kaita tsakiyar wurin suna nunawa jama'a Naanaa dinsu. Mai aiki ce amma wadda take a inda aka san darajar masu aiki har masu gida suke karrama su.
Ta sami kyaututtuka da yawa daga abokan aikinta da abokan arziki.
Frau Marie Schmidt ta kawo envelop da kudi a ciki ta bata sannan ta bawa Fauziyya da Zahra wasu setin dankunne da sarka 'yan ubansu wai su saka da bikinsu. Zayyana ma an bata katon teddy kusan kansu daya. Tana ta murna Mami a ranta tayi dariya kawai. 'Yan kasarmu ina muka wani san darajar teddy.
Hotunan tarihi suke dauka Major ya daga waya yana fadin inda suke. Ko minti biyu ba'ayi ba sai ga matashin saurayi kyakkyawa wankan tarwada mai cike da kwarjini da haiba ya shigo wurin sanye da uniform dinsa na matukin jirgin KLM mallakar kasar Germany. Jacket da wando ne navy blue sai farar shirt a ciki kansa sanye da hula irin ta Captain din jirgi. Mata hudu ne a gefensa hagu da dama air hostess kowacce da uniform riga da skirt sky blue suna rike da flowers masu kyau.
Shigowar tasu ta kayatar da mutanen wurin bare iyayensa. Yana shigowa kai tsaye wurin Major ya nufa ya rungume shi. Mami ta saki baki sai kuma ta daure fuska cikin wasa.
"Awwab, yau din ma?"
Sai da yayi mata dariya sannan ya rungume Maminsa a kunnenta yana cewa "sorry Mamina"
'Yan matan da suke abokan aikinsa kowacce ta mika mata flower da dan gift suna mata fatan alkhairi.
Awwab ya fiddo tickets biyar daga aljihun sa ya mikawa Major.
"Daddy ga nawa gift din...Captain M.A Mustapha shine zai ja jirginku zuwa birnin Abuja. Sai da na duba schedule dina na sayi ticket. Tafiya ta dawo nan da sati biyu. I hope it is okay"
Zayyana tayi tsalle ta dane shi tana ihun murna. Mami sai murmushi kawai na jindadi. Major kuwa tsokanarsa yake yi wai bazai shiga ba kada ya zubar dasu a teku.
An gama party lafiya suka koma gida tare dashi. Shirye shirye ya kankama inda suka hada ya nasu ya nasu sai gida Nigeria.
***********
Iyayen Zainab sun sakata a gaba kowa da abinda yake cewa tun da ta sanar musu cewa a yiwa iyayen Hadir magana akan aurensu.
"Wai shin idan kin koma soyayya zaki rinka zuba muku a kwano kuna ci? Ke ba aiki shi a zaune. Ni har yau ban gamsu da ba ke kika kashewa kanki aure ba" mamanta tace a hasale.
Babanta ne ma mai dan sauki a gareta "Zainab nasan kila ko a wurin Ibrahim kina ji cewa jikin Hadir babu wani sauki sai na musulunci. Kinje kin shafe shekaru tare da Musa kin saba da jindadi. Ta ina zaki koma gidansu?"
"Baba na fada muku ya bani gida a Kano sannan ya kara min jari akan wanda ya bani tun da nake zuwa Dubai saro kaya dashi. Alhamdulillah Allah Ya wadatani Abbansu Aisha ne sila. Ni zan cigaba da tafiya kasuwancina ne Ibrahim ya rinka kula dashi idan bana nan"
Mamanta ta kara kulewa "sannu uwar tsari, waro har kin gama tsara yadda komai zai kasance"
Allah Ya sani tana son iyayenta kuma tana girmama su. Amma wannan karon tana jin tayi girman da ya kamata a karbi uzurinta idan tazo dashi.
"Idan ba kwa so na komawa Hadir bazan koma ba. Amma wallahi bazan kara aure ba har na mutu"
Tsam ta tashi daga dakin Baban nata. Sun san Zainab da taurin kai. Anyi sa'a ma zamanta da Musa Allah Yayi da tsayin kwana. Tufka suke da warwara suna guje mata matsala a gaba. Karshe mahaifinta yace su barta Allah kadai Yasan dalilin wannan soyayya da take yi masa.
Bayan kwanaki ana muhawara da 'yan uwa babanta da kansa yaje Kano da dan uwansa ya gabatarwa Baban Hadir bukatarsu. Sunyi matukar mamaki ace har yanzu Zainab tana son dansu. Matar da sun sani yanzu ita dashi kamar wutsiyar rakumi ne da kasa. Daga irin suturun da take yiwa Ibrahim da abubuwan zamani da take wadata shi dasu zaka san Haj Zainab take don tayi Hajji da Umara albarkacin Musa.
"Idan na fadawa Hadir bazai yarda ya aureta ba saboda lalurarsa" Babansa ya amsa musu a sanyaye. Hadir ya riga ya karbi kaddarar rayuwarsa.
"Sai kayi shiru mu kulla abinmu a tsakaninmu ba shikenan ba" Kawun Zainab ya bashi amsa.
Da izinin Allah a ranar basu tashi ba sai da aka mayar da auren Zainab jaruma mai sadaukarwa da Hadir jarumin kasata da kasar ta dade da mantawa dashi.
Da aka kirata da wannan kyakkyawan labari tayi kukan farinciki sosai. Sati daya aka diba tariya inda Baba ya sa Ibrahim ya kwashe kayan sawarsu ya rinka maidawa gidanta da yake Janbulo. Hadir yana kallo bai iya tambaya sai ya sawa ransa ko gyara za'ayi a dakin.
**********
"Wayyo Innawuro, kiyi min rai....Ummiiiii ki ceceni"
Ihun Radhiya kenan da ya karade gidan tana zaune Emzee ya danneta Innawuro zata yi mata aski.
Mairama hakuri take bata akan ta bari ayi "idan ba'a magance kwarkwatar nan ba wallahi duka sai kin shafa mana. Har na gama makarantar kwana ni banyi ba. Ku baku iya kula da kanku sai kazanta da gayun banza"