Sashe 59
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya fito daga dakin zasu raka shi bakin mota Emzee ya kawo mata wayar Ummi "Kawu Zakari ne yake son magana dake"
Murmushi ta saki ta mika hannu zata karbi wayar "Allah Sarki Kawu Zakari kwana biyu"
Yadda Awwab ya juyo da sauri Emzee sai da yaja baya ya fasa bata wayar.
"Ba ka gaisa dashi ba?"
"Eh mun gaisa"
"To kace tana gaishe shi, ke kuma muje ki rakani"
Sumsum ta wuce Emzee ya yi murmushi. Hamma yana burge shi kuma ya tabbatar da gaske yake son 'yar uwarsa shiyasa yake kara ganin girmansa. Mutum biyu ne damuwarsa a duniya, daga Ummi sai Adda Radhiya. Farincikinsa shine ya gansu cikin farinciki da kwanciyar hankali. A dole yayi masa karyar bata kusa. Yace to babu matsala gobe suna tafe duba Ummi dasu Innawuro.
Saboda tsokana Emzee sai ya daga murya yadda zasu ji "Adda yace zaku hadu gobe zasu so duba Ummi"
Tsayuwa Awwab yayi ya juya zai yanka masa magana tuni Emzee ya bace yana ta dariya. Hararar sai ta koma kan Radhiya ta dan ja da baya.
"Ni kuma me nayi?"
" 'Yar karamarki dake yarinyar nan kina da crush. Allah Yasa yazo kije kina masa murmushi zan sani ne"
"Shi kuma meye crush din?"
"Ko mutum baiyi niyya ba sai kin sashi dariya" yace yana murmushi.
"Crush din wani ne?"
"Yana nufin wani ya rinka burgeki kiji inama zai zama masoyinki"
Sai da tayi dariya tace ko kishi yake yi ya amsa mata da cewa "sosai ma kuwa, Allah Schatzi kada na tafi ki fara kula likitocin asibitin nan. Gabana ya soma faduwa kada suyi min kwace"
Wata dariyar take yana kallon fuskarta yana jindadi. Komai na Radhiya abin so ne a gareshi. Da kyar ya iya jan motar ya tafi tana ta daga masa hannu har ya fita daga harabar asibitin.
Tunda ya hau hanya bai tsaya ko ina ba sai cikin gidansu. Wata irin gajiya yaji ta dirar masa ya samu yayi bacci bayan yayi wanka.
**********[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Gagarumin taro aka hada na 'ya'yan marigariyi Alh Ghousman da jikokinsa manya. Hankulansu duka a tashe sai maganganu ake yi cikin harshen tamasheq.
Alh Ghoumar da Alh Sidi sune manya a iyaye maza. Hamshakan 'yan kasuwa ne wadanda noma da kiwon da suka gada a wurin mahaifinsu ya zama tushen arzikinsu. Har ila yau a cikin taron akwai Ministan yada labarai Alh Issa Bouba miji ga Gwaggon Zayyan Aghaisha. Tana zaune a kusa da 'yan uwanta tana ta zubar da hawaye.
"Abinda ban gane ba shine a wane dalili wannan yaro Maikudi zai ce mana sun rasu gabadaya?" Alh Sidi yayi maganar cikin kunar rai. Duk tsayin shekarun nan iyalin Zayyan suna raye babu wanda ya sani cikinsu. A tunaninsu tsatson Alheran 'yar uwarsu ya riga ya kare basu da wani ko wata da zasu kalla su dangantata dasu.
"Ba wannan ba ma, ina suka zauna? Me yasa matarsa bata neme mu ba?"
Cikin kuka Gwaggo Aghaisha wadda suke kira Mamme tace da Alh Ghoumar "ka manta yanzu fa mutumin nan da yace tare suke da Zayyan a filin yaki yace har makancewa tayi. Kuma yaushe zaka ga laifinta ma. Mune muka san inda take ita bata taba zuwa Agadez ba."
"Haka ne kuma" yace jiki a sanyaye.
"Duk shekarun nan kila ta yisu ne cikin jin haushinmu. Tana ganin kamar mun rabu da ita saboda babu idon mijinta a duniya" Mamme ta sake fashewa da kuka.
Ko cikakken rabin awa basuyi ba da yin waya da Major Mustapha wanda yayi musu bayanin da zai yiwu ta waya. Bayan ya tura a binciko masa inda suke da takaitaccen bayanin cewa Mairama da 'ya'yanta suna da rai shine suka hadu cikin tashin hankali da mamakin wannan labari suka kira nambar da ya bayar. Sun dade suna waya inda ya fada musu abubuwan da suka sami wannan iyali. Basu da dalilin karyata shi tunda harda hoto ya tura musu domin shaida a lokacin da yace a nemo su.
Sai da hankula suka dan natsa sannan Alh Sidi yace "ina ganin ya kamata mu shirya muje mu gansu. Yaran mu kawosu su ga 'yan uwa don kada irin haka ta sake faruwa"
Kowa yayi na'am da wannan shawara. To sai kuma batun su waye zasu je. Babu wanda yake so a barshi a baya. Jirgi suka fara tunanin bi daga baya aka soke saboda zasu bukaci motocin hawa idan sun je.
"Babu wani abin damuwa tunda zamu daukosu. A sanar da sauran dangi idan yayi muku nan da kwanaki kadan sai mu shirya duk abinda ya kamata mu tafi"
Sati dayan ma suna ganin tsayinsa to amma tafiyar basu dauketa ta garaje ba. Danginsu, jininsu da kaddara ta rabasu. Ya zama wajibi a garesu su yiwa wannan tafiya shiri na musamman.
**********
Bayan sallar magariba Awwab sunyi da Ghazalatu zai je wurinta. Yana shiryawa suna waya da Radhiya tana masa shagwaba yana biye mata. Kwankwasa masa kofa akayi tare da sallama yana makale da wayar a kafada ya budewa Fauziyya kofar.
"Daddy yana kiranka"
Da ka ya amsa ya koma ya gama fesa turare sannan ya yiwa Radhiya sallama da sakon gaisuwa ga Umminsa.
A dakin Daddy din ya samesu tare da Mami. Yana shiga Daddy yace mata tayi hakuri ta basu wuri.
"Ba sai kun koreni ba na dade da sanin kuna wareni. To dadin abin ina da 'yan mata na"
"Zahra da Fauziyya ko? Kinsan dai ko da kudi bazaki saye min Zayyanatu ba" Daddy yace da murmushin dole saboda kwata kwata baya cikin nutsuwarsa tun jiya. Mami ta kula kuma ta tambayeshi sau daya yace babu komai sai taja bakinta tayi shiru. Ita ma din tana da danuwar da take dannewa bata so ta fada masa game da Zahra.
Murmushin ta mayar masa "ka manta jiya baka bata kudin kanwar amarya day ba mun ganku a rana? Yanzu zanje na sayeta"
Bayan fitarta Daddy ya maida kallonsa ga Awwab da yake zaune a kasa daga gefen wata duguwar kujera.
"MUHAMMAD"
Dago kai yayi da sauri saboda yadda kiran ya ratsa ko ina a jikinsa. Baya tunanin idan ba a makaranta ba ko za'a fadawa wani sunansa Daddy yana kiransa da Muhammad balle da irin wannan yanayi da yake nuni da babu wasa cikin maganar da zasu yi.
"Na'am Daddy"
"Meye tsakaninka da kanwarka Ghazalatu?"
Dama yayi tunanin wannan maganar ce tunda Ghazalatu tace tana tunanin Daddy Haroun ya sani ko ma yayi zancen da Alh Baba.
"Daddy maganar aure ce"
"Awwab meyasa baka sanar dani ko mahaifiyarka ba?"
Sunkuyar da kansa yayi yana mai takaicin biye mata da yayi tun a lokacin suka boye. Da an sani a gida zasu iya rokar alfarmar ta gama karatun kafin ayi aure tunda shine babbar damuwarta. Haka nan dai ya sanar da Daddy dalilin boyewar tasu.
"Rashin sanin kana nemanta ya sanya nayi maka karambani. Zuwanmu Rugar Barkindo na yiwa kakannin Radhiya alkawarin za ka aureta saboda sharadin da suka gindaya min kenan na bani ita na dawo da ita cikinku tayi karatu."
Murmushi sosai ya ga Awwab yayi ya sake dukar da kai. Wannan ya tabbatar masa da zancen Mami da tace tana ganin kamar yana sonta.
"Daddy nagode kuma na karba"
"Yaya zaka yi da kanwarka kuma?"
Babu kwauron baki ya fadawa mahaifinsa cewa dama ya dawo ne domin neman shawararsa akan yadda ya kamata ya bullowa lamarin.
"Bazan wulakanta Ghazalatu saboda Alheran ba, itama kuma ko ba ni na nemeta da kaina ba Daddy bazan bari kaji kunyar iyayenta ba"
Hakika tunani da hangen nesa irin na Awwab suna daga cikin dalilin da suka sa Major yake matukar son yaron. Sai aka samu kyakkyawar shakuwa a tsakaninsu wadda tasa suke shawartar juna akan abubuwa daban daban. Yaji dadin amsar dan nasa sosai amma kuma ba abinda nasa iyayen suke so ba ne.
"Ina zaka kai mata biyu a lokaci guda?"
Cikin yanayi na damuwa yace "Daddy nima ban sani ba amma don Allah kada kace na hakura da kowacce bazan iya ba. Dukkansu ni na kai kaina garesu kuma suka amince min"
"Muhammad kayi hakuri da Radhiya, su Alh Baba sun ce na bawa iyayenta hakuri Ghazalatu kadai zaka aura"
A firgici ya dago kai yana mikewa tsaye baki daya "Daddy?"
"Bana son jan zancen nan har Maminku taji. Alhaji yace a bari su gama biki to zan jira a gama din naji hukuncin da zasu yanke. Na sanar da kai ne saboda idan da gaske ka fara neman Radhiya ka janye. Bana son ka cigaba da sa mata rai har sai na gama iya kokarina akan neman amincewarsu ka hada biyun"
Gumi ne sosai ya soma wankewa Awwab fuska. Idan zai iya hakura da Alheran dinsa tabbas zai iya hakura da aure baki daya. Gurfana yayi a gaban Major kamar mai rokon gafara.
"Don Allah Daddy kasa baki wallahi zan iya aurensu su duka."
"Tashi kaje dama yace yana nemanka idan ka dawo. Ka yawaita addu'ar zabin Allah"
Jikinsa sam babu kwari haka ya fita kamar mara lafiya. Mami tana kallon fitarsa Zahra na yi masa magana bai ma san tana yi ba. Jikinta itama sai yayi sanyi. Tabbas akwai abinda yake faruwa wanda Daddy baya son ta sani. To ko ya gane abinda take boyewa na Zahra ne? Kai da wahala tace a ranta tana girgiza kai. Zahra bazata taba fada ba ta sani. Kallon yarinyar tayi a zaune bayan fitar Awwab bai kulata ba tayi shiru. Zuciyarta ce tayi mata nauyi ta rasa da wa zata yi maganar nan ta saukewa kanta nauyi. Fitarta kuma ba karamar illa zai iya janyowa zumunci ba. Shirun dai da ta yi kuma ta roki Zahra da tayi itama shine take ganin kamar zai zame musu maslaha.
Kafin ya isa gidan Alh Baba missed calls din Ghazalatu sun kai goma. Kiransa take tun yana wurin Daddy tana masa tuni akan shiru da ta ji. Ransa gabadaya a cunkushe ya shiga ya gaishe da Mummy kafin ya fito da niyar gaisawa da kakaninsu mata.
"Yayana ka bari sai zaka tafi kaje. Yanzu cinye mana lokacin hira zasuyi"
"Kinfi so dare yayi sosai lokacin na shiga sunyi bacci? Ba dadewa zanyi ba"
Murmushi ta saki ta mika hannu zata karbi wayar "Allah Sarki Kawu Zakari kwana biyu"
Yadda Awwab ya juyo da sauri Emzee sai da yaja baya ya fasa bata wayar.
"Ba ka gaisa dashi ba?"
"Eh mun gaisa"
"To kace tana gaishe shi, ke kuma muje ki rakani"
Sumsum ta wuce Emzee ya yi murmushi. Hamma yana burge shi kuma ya tabbatar da gaske yake son 'yar uwarsa shiyasa yake kara ganin girmansa. Mutum biyu ne damuwarsa a duniya, daga Ummi sai Adda Radhiya. Farincikinsa shine ya gansu cikin farinciki da kwanciyar hankali. A dole yayi masa karyar bata kusa. Yace to babu matsala gobe suna tafe duba Ummi dasu Innawuro.
Saboda tsokana Emzee sai ya daga murya yadda zasu ji "Adda yace zaku hadu gobe zasu so duba Ummi"
Tsayuwa Awwab yayi ya juya zai yanka masa magana tuni Emzee ya bace yana ta dariya. Hararar sai ta koma kan Radhiya ta dan ja da baya.
"Ni kuma me nayi?"
" 'Yar karamarki dake yarinyar nan kina da crush. Allah Yasa yazo kije kina masa murmushi zan sani ne"
"Shi kuma meye crush din?"
"Ko mutum baiyi niyya ba sai kin sashi dariya" yace yana murmushi.
"Crush din wani ne?"
"Yana nufin wani ya rinka burgeki kiji inama zai zama masoyinki"
Sai da tayi dariya tace ko kishi yake yi ya amsa mata da cewa "sosai ma kuwa, Allah Schatzi kada na tafi ki fara kula likitocin asibitin nan. Gabana ya soma faduwa kada suyi min kwace"
Wata dariyar take yana kallon fuskarta yana jindadi. Komai na Radhiya abin so ne a gareshi. Da kyar ya iya jan motar ya tafi tana ta daga masa hannu har ya fita daga harabar asibitin.
Tunda ya hau hanya bai tsaya ko ina ba sai cikin gidansu. Wata irin gajiya yaji ta dirar masa ya samu yayi bacci bayan yayi wanka.
**********[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Gagarumin taro aka hada na 'ya'yan marigariyi Alh Ghousman da jikokinsa manya. Hankulansu duka a tashe sai maganganu ake yi cikin harshen tamasheq.
Alh Ghoumar da Alh Sidi sune manya a iyaye maza. Hamshakan 'yan kasuwa ne wadanda noma da kiwon da suka gada a wurin mahaifinsu ya zama tushen arzikinsu. Har ila yau a cikin taron akwai Ministan yada labarai Alh Issa Bouba miji ga Gwaggon Zayyan Aghaisha. Tana zaune a kusa da 'yan uwanta tana ta zubar da hawaye.
"Abinda ban gane ba shine a wane dalili wannan yaro Maikudi zai ce mana sun rasu gabadaya?" Alh Sidi yayi maganar cikin kunar rai. Duk tsayin shekarun nan iyalin Zayyan suna raye babu wanda ya sani cikinsu. A tunaninsu tsatson Alheran 'yar uwarsu ya riga ya kare basu da wani ko wata da zasu kalla su dangantata dasu.
"Ba wannan ba ma, ina suka zauna? Me yasa matarsa bata neme mu ba?"
Cikin kuka Gwaggo Aghaisha wadda suke kira Mamme tace da Alh Ghoumar "ka manta yanzu fa mutumin nan da yace tare suke da Zayyan a filin yaki yace har makancewa tayi. Kuma yaushe zaka ga laifinta ma. Mune muka san inda take ita bata taba zuwa Agadez ba."
"Haka ne kuma" yace jiki a sanyaye.
"Duk shekarun nan kila ta yisu ne cikin jin haushinmu. Tana ganin kamar mun rabu da ita saboda babu idon mijinta a duniya" Mamme ta sake fashewa da kuka.
Ko cikakken rabin awa basuyi ba da yin waya da Major Mustapha wanda yayi musu bayanin da zai yiwu ta waya. Bayan ya tura a binciko masa inda suke da takaitaccen bayanin cewa Mairama da 'ya'yanta suna da rai shine suka hadu cikin tashin hankali da mamakin wannan labari suka kira nambar da ya bayar. Sun dade suna waya inda ya fada musu abubuwan da suka sami wannan iyali. Basu da dalilin karyata shi tunda harda hoto ya tura musu domin shaida a lokacin da yace a nemo su.
Sai da hankula suka dan natsa sannan Alh Sidi yace "ina ganin ya kamata mu shirya muje mu gansu. Yaran mu kawosu su ga 'yan uwa don kada irin haka ta sake faruwa"
Kowa yayi na'am da wannan shawara. To sai kuma batun su waye zasu je. Babu wanda yake so a barshi a baya. Jirgi suka fara tunanin bi daga baya aka soke saboda zasu bukaci motocin hawa idan sun je.
"Babu wani abin damuwa tunda zamu daukosu. A sanar da sauran dangi idan yayi muku nan da kwanaki kadan sai mu shirya duk abinda ya kamata mu tafi"
Sati dayan ma suna ganin tsayinsa to amma tafiyar basu dauketa ta garaje ba. Danginsu, jininsu da kaddara ta rabasu. Ya zama wajibi a garesu su yiwa wannan tafiya shiri na musamman.
**********
Bayan sallar magariba Awwab sunyi da Ghazalatu zai je wurinta. Yana shiryawa suna waya da Radhiya tana masa shagwaba yana biye mata. Kwankwasa masa kofa akayi tare da sallama yana makale da wayar a kafada ya budewa Fauziyya kofar.
"Daddy yana kiranka"
Da ka ya amsa ya koma ya gama fesa turare sannan ya yiwa Radhiya sallama da sakon gaisuwa ga Umminsa.
A dakin Daddy din ya samesu tare da Mami. Yana shiga Daddy yace mata tayi hakuri ta basu wuri.
"Ba sai kun koreni ba na dade da sanin kuna wareni. To dadin abin ina da 'yan mata na"
"Zahra da Fauziyya ko? Kinsan dai ko da kudi bazaki saye min Zayyanatu ba" Daddy yace da murmushin dole saboda kwata kwata baya cikin nutsuwarsa tun jiya. Mami ta kula kuma ta tambayeshi sau daya yace babu komai sai taja bakinta tayi shiru. Ita ma din tana da danuwar da take dannewa bata so ta fada masa game da Zahra.
Murmushin ta mayar masa "ka manta jiya baka bata kudin kanwar amarya day ba mun ganku a rana? Yanzu zanje na sayeta"
Bayan fitarta Daddy ya maida kallonsa ga Awwab da yake zaune a kasa daga gefen wata duguwar kujera.
"MUHAMMAD"
Dago kai yayi da sauri saboda yadda kiran ya ratsa ko ina a jikinsa. Baya tunanin idan ba a makaranta ba ko za'a fadawa wani sunansa Daddy yana kiransa da Muhammad balle da irin wannan yanayi da yake nuni da babu wasa cikin maganar da zasu yi.
"Na'am Daddy"
"Meye tsakaninka da kanwarka Ghazalatu?"
Dama yayi tunanin wannan maganar ce tunda Ghazalatu tace tana tunanin Daddy Haroun ya sani ko ma yayi zancen da Alh Baba.
"Daddy maganar aure ce"
"Awwab meyasa baka sanar dani ko mahaifiyarka ba?"
Sunkuyar da kansa yayi yana mai takaicin biye mata da yayi tun a lokacin suka boye. Da an sani a gida zasu iya rokar alfarmar ta gama karatun kafin ayi aure tunda shine babbar damuwarta. Haka nan dai ya sanar da Daddy dalilin boyewar tasu.
"Rashin sanin kana nemanta ya sanya nayi maka karambani. Zuwanmu Rugar Barkindo na yiwa kakannin Radhiya alkawarin za ka aureta saboda sharadin da suka gindaya min kenan na bani ita na dawo da ita cikinku tayi karatu."
Murmushi sosai ya ga Awwab yayi ya sake dukar da kai. Wannan ya tabbatar masa da zancen Mami da tace tana ganin kamar yana sonta.
"Daddy nagode kuma na karba"
"Yaya zaka yi da kanwarka kuma?"
Babu kwauron baki ya fadawa mahaifinsa cewa dama ya dawo ne domin neman shawararsa akan yadda ya kamata ya bullowa lamarin.
"Bazan wulakanta Ghazalatu saboda Alheran ba, itama kuma ko ba ni na nemeta da kaina ba Daddy bazan bari kaji kunyar iyayenta ba"
Hakika tunani da hangen nesa irin na Awwab suna daga cikin dalilin da suka sa Major yake matukar son yaron. Sai aka samu kyakkyawar shakuwa a tsakaninsu wadda tasa suke shawartar juna akan abubuwa daban daban. Yaji dadin amsar dan nasa sosai amma kuma ba abinda nasa iyayen suke so ba ne.
"Ina zaka kai mata biyu a lokaci guda?"
Cikin yanayi na damuwa yace "Daddy nima ban sani ba amma don Allah kada kace na hakura da kowacce bazan iya ba. Dukkansu ni na kai kaina garesu kuma suka amince min"
"Muhammad kayi hakuri da Radhiya, su Alh Baba sun ce na bawa iyayenta hakuri Ghazalatu kadai zaka aura"
A firgici ya dago kai yana mikewa tsaye baki daya "Daddy?"
"Bana son jan zancen nan har Maminku taji. Alhaji yace a bari su gama biki to zan jira a gama din naji hukuncin da zasu yanke. Na sanar da kai ne saboda idan da gaske ka fara neman Radhiya ka janye. Bana son ka cigaba da sa mata rai har sai na gama iya kokarina akan neman amincewarsu ka hada biyun"
Gumi ne sosai ya soma wankewa Awwab fuska. Idan zai iya hakura da Alheran dinsa tabbas zai iya hakura da aure baki daya. Gurfana yayi a gaban Major kamar mai rokon gafara.
"Don Allah Daddy kasa baki wallahi zan iya aurensu su duka."
"Tashi kaje dama yace yana nemanka idan ka dawo. Ka yawaita addu'ar zabin Allah"
Jikinsa sam babu kwari haka ya fita kamar mara lafiya. Mami tana kallon fitarsa Zahra na yi masa magana bai ma san tana yi ba. Jikinta itama sai yayi sanyi. Tabbas akwai abinda yake faruwa wanda Daddy baya son ta sani. To ko ya gane abinda take boyewa na Zahra ne? Kai da wahala tace a ranta tana girgiza kai. Zahra bazata taba fada ba ta sani. Kallon yarinyar tayi a zaune bayan fitar Awwab bai kulata ba tayi shiru. Zuciyarta ce tayi mata nauyi ta rasa da wa zata yi maganar nan ta saukewa kanta nauyi. Fitarta kuma ba karamar illa zai iya janyowa zumunci ba. Shirun dai da ta yi kuma ta roki Zahra da tayi itama shine take ganin kamar zai zame musu maslaha.
Kafin ya isa gidan Alh Baba missed calls din Ghazalatu sun kai goma. Kiransa take tun yana wurin Daddy tana masa tuni akan shiru da ta ji. Ransa gabadaya a cunkushe ya shiga ya gaishe da Mummy kafin ya fito da niyar gaisawa da kakaninsu mata.
"Yayana ka bari sai zaka tafi kaje. Yanzu cinye mana lokacin hira zasuyi"
"Kinfi so dare yayi sosai lokacin na shiga sunyi bacci? Ba dadewa zanyi ba"