Sashe 93
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba wata tafiyar kirki suka yi ba suka iso kofar gidan Salame tana ta hura hanci ita mai da. Sauran kuwa a gida ta barsu har wadda ta yaye idan ta sami abinci ta tafi musu dashi.
Emzee da Ibrahim suna bakin mota suna sauko da kaya suka iso.
"Drama ta barka Halifa" Emzee yace yana dariya.
"Ko me akayi a dawo dashi farko gaskiya"
Salame ta kallesu ta watsar Emzee sau biyu yana cewa Gwaggo Salame ina wuni tayi kamar bata ji ba. Sai yake ya yiwa Ibrahim shima bata amsa shi ba yace wai kila don tana sauri ne bata ji su ba. Ta kai bakin kofa su kuma suna fitowa. Ummi da Daada zasu yiwa rakiya da zasu tafi yanzu. Sai kuma dreban gidan su Halifa shima zai tafi idan sun tashi tafiya Halifa zai kira shi yazo ya tafi dasu.
Gaban Salame wani irin bugu yayi da ta ga Mairama tayi wani irin kyau ta kara haske. Kayan jikinta a hasashen Salame sai kace wata matar gwamna. Wannan 'yar ta ta mai kama da aljanu itama ka kalleta sai ka kara ga wasu 'yan matan Zayyana da Hibba su ma kowacce ta hadu karahe. Bayan wani ta gani kusa da Malamijo suna magana ta wuce su Mairama a fusace za ta shiga cikin gidan.
"Salame babu gaisuwa? Ko ba ita bace?" Zayyan yace albarkacin Halifa da ya tabo shi yana cewa ga Ummansa.
Ba ta iya juyowa ba sai tsuma da take yi tun daga tsakar kanta har tafin kafa. Tasan muryar nan da irin tasirin da ta jima tana yi mata a duk lokacin da taji ta. Sannu a hankali ta juyo idanunta suka sauka akan Zayyan Muhammad Tureta mutumin da har yau babu wani namiji da ya kaishi daraja da kima a idanunta.
Takowa take yi jiki a mace zuwa gabansa ta ma manta da kowa da komai sai tashin tsumin kaunar da take masa. Idanunta suna kwararar da hawaye ta kusa isa gareshi "Zayyan dama kana raye?"
Malamijo gani yayi tana neman wuce gona da iri yasha gabanta "sai ki ka ga mijin kanwarki ko? Ashe tsahon shekarun nan yana daure a gidan yari"
"Gidan yari? Allah sai Ya saka mana. Ni dama jikina yana bani baka barmu ba Zayyan" tace tana kuka sosai.
"Zai saka mana kam ni da iyalina. Mairama matso ku gaisa mu tafi" Zayyan yace fuskarsa babu digon fara'a ko kadan. Ji wannan zubar da mutumci da take neman yi a gaba danta, mahaifi da kanwarta kuma matarsa.
Ita Mairama dama tsayawa tayi ta ga iya gudun ruwanta saboda yadda ta kula kamar bata cikin hayyacinta. Da ace bata san tana son mijin nata ba sai tayi tsammanin tsabar kaduwa ce kawai.
"Adda Salame yaya gida da yara? Da Halifa bai taso ki ba ma zamu tsaya a gidan naki ai su gaisa da maigidan naki"
Firgigit ta tuna wai tana da aure. Amma Allah Ya isa Alh Indararo. Wallahi tayar masa da hankali kawai zata yi ya sauwake mata ta huta. Sakin fuska tayi don dole suka gaisa da Mairama ta rakata har bakin mota. Ta bangaren da Zayyan yake zaune a baya ta tsaya yayi saurin danna abin rufe window ya dage glass din. Bata bata rai ba ta dawo bangaren Mairama ta leko da kanta.
"Hmm nace bari nayi miki karambani. Kun dai tambayi malamai game da matsayin auren naku ko. Kada aje ana haramtaccen zama. Idan babu auren gara a san me ake ciki tun wuri"
Da Mairama tana zagi da sai ta hado mai kyau ta zubawa Salame. Wannan jaraba har ina. Daga sake haduwa dashi take kokarin dawo da maitarta a fili.
"Kinsan ba sakina yayi ba kuma ban sake aure ba. Saboda haka auren mu yana nan har yanzu"
"Mu tafi mana" Zayyan yace da dreban rai a dan bace tun bayan dawowarsa. Ba don ta gaji da kallonsa ba ta koma gefe aka ja motar tana tsaye tana daga hannu "bye bye, bye bye" take ta fadi tana murmushi.
Hannun Mairama ya rike yana kallon fuskarta "meye na tsayawa yi mata dogon bayani bayan kinsan akan hanya muke?"
Murmushi tayi ya karawa fuskarta kyau "gani nayi gara nayi mata bayani tun wuri kada tayi tunanin akwai wata kofa da za ta iya samu ta shiga gidanka"
Bude baki yayi ya kalleta "kada kice min ta fada miki"
"Bata ji komai ba ta sanar dani kuma shine dalilin mutuwar aurenta kamar yadda Alh Salisu ya fada min jiya da kana waya da Baban Arifah lokacin da yazo. Cewa yayi nayi hankali da ita mai hali baya fasa halinsa kuma gashi na gani"
"Mairama ina so ki sani wallahi ban taba cin amanarki ba akan Salame"
Kanta ta dora akan kafadarsa ta rufe ido "kada zancenta ya bata mana farincikinmu"
Alamun saka zip yayi a baki yana dariya suka cigaba da hirarsu cikin shauki har suka isa Kano. Gidan da ya gina da guminsa da kuma gadon mahaifiyarsa ya shiga yana tuna baya. Saboda hazo ya fara kura amma da gani an kashe masa kudi wurin gyara da kayan alatu. Mairama ya janyo ya dora kansa a kafadarta yana tsaye a bayanta yace "kin tuna zuwanmu gidan nan na farko?"
Sai da taji kunya Allah Yasa baya ganin fuskarta "ban tuna komai ba"
"Da gaske? Ni kuwa kamar a kaina aka ajiye ranakun da Mairama ta rinka nunawa Zayyan soyayya irin wadda nake sa ran a maimaita. Jikina yana bani a nan kika samo Zayyan fa"
"Ni dai ka kyaleni gyaran gida zanyi" tace a kunyace
"Muje na tayaki ai muna da lokaci. Sai jibi zamu tafi Sakkwato in je mu hadu da Maikudi"
Ajiyar zuciya tayi tana hango wannan haduwa bazata yiwa Maikudi kyau ba ko kadan.
**********
Ranar da daddare bayan Yadikko ta dawo ne Radhiya taji komai game da amaryar Malamijo a wurinta. Taji zafin sakin Hajjo ita ma tayi ta bawa Yadikko baki akan kada ta tafi wa zasu gani su ji dadi.
Shima Malamijon kuma sai ya fada mata abubuwan da Hajiyayyen tayi masa.
"Malamijo ai kowa maye ne sai dai idan baiso nunawa ba. Ka rubuta mata takardarta tun dare gobe zaka bata kuma wallahi Hajjo kadai na yarda ka dawo da ita"
"Ba ma sai kin fada ba 'Yar soja ikon Allah. Na ma gama aure yanzu sai dai ku"
"Wai ni su waye ma suke yi maka waliyai ne a aure auren Malamijo?"
"Kaniyarki mai ido a tsakar ka" yace yana laluben takalmi zai biyota dashi ta gudu.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: 'Ya'yan nasu sun hadu a falon Ummi kowa na bawa Daada labarin kansa musamman game da karatu shi kuma yana rike da Daada Karami. Radhiya ta kalli yaron ya kurawa babanta ido tayi murmushi tana tambayar Mami da suke shigowa tare da Mama suna neman wucewa dakin Ummi wai yaushe zasu yi taron sunansa ne.
Mama ce ta bata amsa "babu wani taro fa Radhiya tunda babansa ya dawo me kuma zai bukata? Masu tahowa dai zasu zo amma barka kawai"
"Yaya zaki yi mana haka babu shawara Zainab?" Cewar Mami tana nuna mata rashin jindadi.
"Ni da dana zata yi min karfa karfa to wallahi ban yarda ba" inji Ummi tana goyon bayan Mami.
Zayyan ya daga hannu kamar dan makaranta "idan kun bani dama in raba gardama?"
"Mun baka" Mama tace da sauri tana neman tsira. Da Baba Hadir suka yi shawarar soke taron kawai kwanaki sun kara ja kuma ma dai dawowar Zayyan ita ce abu mafin dadi garesu.
Kallon iyalan nasu yayi yana jin tamkar Allah Ya bashi fiye da abinda yake nema a duniya. Major da Hadir harda Baban Arifah da ya sadaukar da rayuwarsa dominsu batare da tunanin ko kadan zasu saka masa ba gashi sun rike masa iyali da gaskiya. Idan ya biyewa zuciyarsa kuka zai yi musu daga su har matan kwarai da suke aure wadanda suka karfafa musu gwiwa wajen dabbaka zumunci a bayan idonsa. Shi ba butulu bane da zai manta Mami Hassana wadda mijinta Major da Ummi suka bashi labarin cewa aikatau tayi a Germany domin ciyar da iyalinta amma a cikin abinda take samu Major ya rinka cire wani abu kafin ya fara aiki yana aikowa matarsa Mairama. Babu wanda baiyi masa ba amma Allah Ya sani yana jin girman Mami sosai a zuciyarsa. Daga ita har Mama Zainab sun wuce matan abokai a gareshi sai dai ya kira su 'yan uwa. Sun burge shi matuka yadda suka tsayawa juna a matsayinsu na matan sojoji suke kokarin rufawa juna asiri. Ba don a gidan iyayensa an bar kari tun ran tubani ba ai da kamata yayi ace ya dawo ya sami matarsa a tsakiyar matan su Badaru. Abin takaici shine sun tashi babu wannan shakuwar tsakaninsa da 'yan uwansa maza da mata. Jume tun kuruciya ta koya musu tsanarsa a matsayin dan kishiya. Sai dai yaji dadi da Mairama ta fada masa yanzu kam idan ka cire Maikudi tsakaninsu da sauran musamman 'ya'ya da jikokin Mal Aminu abokin babansa sai dai hamdala. Ita ma a nata bangaren rashin shakuwa da 'yan uwanta da kuma rashin tsayuwar uba akan 'ya'yansa ya sake bata lamura. Da ace zumuncin nasu mai karfi ne ya tabbatar ko a daji iyalinsa suke bazasu wahala ba. Duka rayuwar Mairama bayan tafiyarsa ai a cikin gidan mahaifinta tayi kafin ta koma Rugar Barkindo amma rashin wannan zumuncin ya sa ita da wadda bata tare da ahalinta kusan daya.
"Daada" Radhiya ta dan taba shi saboda nisa da ya soma yi a tunani.
Murmushi yayi a lokacin Awwab, Daddy da Baba Hadir suka shigo su ma yace "indai na isa to na soke taron sunan"
"Kai da danka Daada waye zai hanaka abinda kake so" Mama tace tana murmushi.
Sauran kuwa da gaske sunyi mamaki harda Ummi kuwa. Sai dai abinda yace ya sanya su wani irin farinciki a take.
"A iya sanina Zayyan kaima ba'ayi taron sunanka ba ko" ya kalli Emzee da suke zaune kusa da juna shi da Ibrahim tamkar tagwaye. Dariya yayi yana zaro idanu "Daada ba dai cewa zaka yi a nade ni a shawl a koma baya ba"
Emzee da Ibrahim suna bakin mota suna sauko da kaya suka iso.
"Drama ta barka Halifa" Emzee yace yana dariya.
"Ko me akayi a dawo dashi farko gaskiya"
Salame ta kallesu ta watsar Emzee sau biyu yana cewa Gwaggo Salame ina wuni tayi kamar bata ji ba. Sai yake ya yiwa Ibrahim shima bata amsa shi ba yace wai kila don tana sauri ne bata ji su ba. Ta kai bakin kofa su kuma suna fitowa. Ummi da Daada zasu yiwa rakiya da zasu tafi yanzu. Sai kuma dreban gidan su Halifa shima zai tafi idan sun tashi tafiya Halifa zai kira shi yazo ya tafi dasu.
Gaban Salame wani irin bugu yayi da ta ga Mairama tayi wani irin kyau ta kara haske. Kayan jikinta a hasashen Salame sai kace wata matar gwamna. Wannan 'yar ta ta mai kama da aljanu itama ka kalleta sai ka kara ga wasu 'yan matan Zayyana da Hibba su ma kowacce ta hadu karahe. Bayan wani ta gani kusa da Malamijo suna magana ta wuce su Mairama a fusace za ta shiga cikin gidan.
"Salame babu gaisuwa? Ko ba ita bace?" Zayyan yace albarkacin Halifa da ya tabo shi yana cewa ga Ummansa.
Ba ta iya juyowa ba sai tsuma da take yi tun daga tsakar kanta har tafin kafa. Tasan muryar nan da irin tasirin da ta jima tana yi mata a duk lokacin da taji ta. Sannu a hankali ta juyo idanunta suka sauka akan Zayyan Muhammad Tureta mutumin da har yau babu wani namiji da ya kaishi daraja da kima a idanunta.
Takowa take yi jiki a mace zuwa gabansa ta ma manta da kowa da komai sai tashin tsumin kaunar da take masa. Idanunta suna kwararar da hawaye ta kusa isa gareshi "Zayyan dama kana raye?"
Malamijo gani yayi tana neman wuce gona da iri yasha gabanta "sai ki ka ga mijin kanwarki ko? Ashe tsahon shekarun nan yana daure a gidan yari"
"Gidan yari? Allah sai Ya saka mana. Ni dama jikina yana bani baka barmu ba Zayyan" tace tana kuka sosai.
"Zai saka mana kam ni da iyalina. Mairama matso ku gaisa mu tafi" Zayyan yace fuskarsa babu digon fara'a ko kadan. Ji wannan zubar da mutumci da take neman yi a gaba danta, mahaifi da kanwarta kuma matarsa.
Ita Mairama dama tsayawa tayi ta ga iya gudun ruwanta saboda yadda ta kula kamar bata cikin hayyacinta. Da ace bata san tana son mijin nata ba sai tayi tsammanin tsabar kaduwa ce kawai.
"Adda Salame yaya gida da yara? Da Halifa bai taso ki ba ma zamu tsaya a gidan naki ai su gaisa da maigidan naki"
Firgigit ta tuna wai tana da aure. Amma Allah Ya isa Alh Indararo. Wallahi tayar masa da hankali kawai zata yi ya sauwake mata ta huta. Sakin fuska tayi don dole suka gaisa da Mairama ta rakata har bakin mota. Ta bangaren da Zayyan yake zaune a baya ta tsaya yayi saurin danna abin rufe window ya dage glass din. Bata bata rai ba ta dawo bangaren Mairama ta leko da kanta.
"Hmm nace bari nayi miki karambani. Kun dai tambayi malamai game da matsayin auren naku ko. Kada aje ana haramtaccen zama. Idan babu auren gara a san me ake ciki tun wuri"
Da Mairama tana zagi da sai ta hado mai kyau ta zubawa Salame. Wannan jaraba har ina. Daga sake haduwa dashi take kokarin dawo da maitarta a fili.
"Kinsan ba sakina yayi ba kuma ban sake aure ba. Saboda haka auren mu yana nan har yanzu"
"Mu tafi mana" Zayyan yace da dreban rai a dan bace tun bayan dawowarsa. Ba don ta gaji da kallonsa ba ta koma gefe aka ja motar tana tsaye tana daga hannu "bye bye, bye bye" take ta fadi tana murmushi.
Hannun Mairama ya rike yana kallon fuskarta "meye na tsayawa yi mata dogon bayani bayan kinsan akan hanya muke?"
Murmushi tayi ya karawa fuskarta kyau "gani nayi gara nayi mata bayani tun wuri kada tayi tunanin akwai wata kofa da za ta iya samu ta shiga gidanka"
Bude baki yayi ya kalleta "kada kice min ta fada miki"
"Bata ji komai ba ta sanar dani kuma shine dalilin mutuwar aurenta kamar yadda Alh Salisu ya fada min jiya da kana waya da Baban Arifah lokacin da yazo. Cewa yayi nayi hankali da ita mai hali baya fasa halinsa kuma gashi na gani"
"Mairama ina so ki sani wallahi ban taba cin amanarki ba akan Salame"
Kanta ta dora akan kafadarsa ta rufe ido "kada zancenta ya bata mana farincikinmu"
Alamun saka zip yayi a baki yana dariya suka cigaba da hirarsu cikin shauki har suka isa Kano. Gidan da ya gina da guminsa da kuma gadon mahaifiyarsa ya shiga yana tuna baya. Saboda hazo ya fara kura amma da gani an kashe masa kudi wurin gyara da kayan alatu. Mairama ya janyo ya dora kansa a kafadarta yana tsaye a bayanta yace "kin tuna zuwanmu gidan nan na farko?"
Sai da taji kunya Allah Yasa baya ganin fuskarta "ban tuna komai ba"
"Da gaske? Ni kuwa kamar a kaina aka ajiye ranakun da Mairama ta rinka nunawa Zayyan soyayya irin wadda nake sa ran a maimaita. Jikina yana bani a nan kika samo Zayyan fa"
"Ni dai ka kyaleni gyaran gida zanyi" tace a kunyace
"Muje na tayaki ai muna da lokaci. Sai jibi zamu tafi Sakkwato in je mu hadu da Maikudi"
Ajiyar zuciya tayi tana hango wannan haduwa bazata yiwa Maikudi kyau ba ko kadan.
**********
Ranar da daddare bayan Yadikko ta dawo ne Radhiya taji komai game da amaryar Malamijo a wurinta. Taji zafin sakin Hajjo ita ma tayi ta bawa Yadikko baki akan kada ta tafi wa zasu gani su ji dadi.
Shima Malamijon kuma sai ya fada mata abubuwan da Hajiyayyen tayi masa.
"Malamijo ai kowa maye ne sai dai idan baiso nunawa ba. Ka rubuta mata takardarta tun dare gobe zaka bata kuma wallahi Hajjo kadai na yarda ka dawo da ita"
"Ba ma sai kin fada ba 'Yar soja ikon Allah. Na ma gama aure yanzu sai dai ku"
"Wai ni su waye ma suke yi maka waliyai ne a aure auren Malamijo?"
"Kaniyarki mai ido a tsakar ka" yace yana laluben takalmi zai biyota dashi ta gudu.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: 'Ya'yan nasu sun hadu a falon Ummi kowa na bawa Daada labarin kansa musamman game da karatu shi kuma yana rike da Daada Karami. Radhiya ta kalli yaron ya kurawa babanta ido tayi murmushi tana tambayar Mami da suke shigowa tare da Mama suna neman wucewa dakin Ummi wai yaushe zasu yi taron sunansa ne.
Mama ce ta bata amsa "babu wani taro fa Radhiya tunda babansa ya dawo me kuma zai bukata? Masu tahowa dai zasu zo amma barka kawai"
"Yaya zaki yi mana haka babu shawara Zainab?" Cewar Mami tana nuna mata rashin jindadi.
"Ni da dana zata yi min karfa karfa to wallahi ban yarda ba" inji Ummi tana goyon bayan Mami.
Zayyan ya daga hannu kamar dan makaranta "idan kun bani dama in raba gardama?"
"Mun baka" Mama tace da sauri tana neman tsira. Da Baba Hadir suka yi shawarar soke taron kawai kwanaki sun kara ja kuma ma dai dawowar Zayyan ita ce abu mafin dadi garesu.
Kallon iyalan nasu yayi yana jin tamkar Allah Ya bashi fiye da abinda yake nema a duniya. Major da Hadir harda Baban Arifah da ya sadaukar da rayuwarsa dominsu batare da tunanin ko kadan zasu saka masa ba gashi sun rike masa iyali da gaskiya. Idan ya biyewa zuciyarsa kuka zai yi musu daga su har matan kwarai da suke aure wadanda suka karfafa musu gwiwa wajen dabbaka zumunci a bayan idonsa. Shi ba butulu bane da zai manta Mami Hassana wadda mijinta Major da Ummi suka bashi labarin cewa aikatau tayi a Germany domin ciyar da iyalinta amma a cikin abinda take samu Major ya rinka cire wani abu kafin ya fara aiki yana aikowa matarsa Mairama. Babu wanda baiyi masa ba amma Allah Ya sani yana jin girman Mami sosai a zuciyarsa. Daga ita har Mama Zainab sun wuce matan abokai a gareshi sai dai ya kira su 'yan uwa. Sun burge shi matuka yadda suka tsayawa juna a matsayinsu na matan sojoji suke kokarin rufawa juna asiri. Ba don a gidan iyayensa an bar kari tun ran tubani ba ai da kamata yayi ace ya dawo ya sami matarsa a tsakiyar matan su Badaru. Abin takaici shine sun tashi babu wannan shakuwar tsakaninsa da 'yan uwansa maza da mata. Jume tun kuruciya ta koya musu tsanarsa a matsayin dan kishiya. Sai dai yaji dadi da Mairama ta fada masa yanzu kam idan ka cire Maikudi tsakaninsu da sauran musamman 'ya'ya da jikokin Mal Aminu abokin babansa sai dai hamdala. Ita ma a nata bangaren rashin shakuwa da 'yan uwanta da kuma rashin tsayuwar uba akan 'ya'yansa ya sake bata lamura. Da ace zumuncin nasu mai karfi ne ya tabbatar ko a daji iyalinsa suke bazasu wahala ba. Duka rayuwar Mairama bayan tafiyarsa ai a cikin gidan mahaifinta tayi kafin ta koma Rugar Barkindo amma rashin wannan zumuncin ya sa ita da wadda bata tare da ahalinta kusan daya.
"Daada" Radhiya ta dan taba shi saboda nisa da ya soma yi a tunani.
Murmushi yayi a lokacin Awwab, Daddy da Baba Hadir suka shigo su ma yace "indai na isa to na soke taron sunan"
"Kai da danka Daada waye zai hanaka abinda kake so" Mama tace tana murmushi.
Sauran kuwa da gaske sunyi mamaki harda Ummi kuwa. Sai dai abinda yace ya sanya su wani irin farinciki a take.
"A iya sanina Zayyan kaima ba'ayi taron sunanka ba ko" ya kalli Emzee da suke zaune kusa da juna shi da Ibrahim tamkar tagwaye. Dariya yayi yana zaro idanu "Daada ba dai cewa zaka yi a nade ni a shawl a koma baya ba"