← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 83 OF 157

Sashe 83

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Garin yayi lufluf sanyin bai fara hana sukuni ba. Takalminta heel ne shiyasa tana tafiya taku daidai irin na matan da suka san kansu ta fito da karamar sling bag wadda babu komai sai tarkacen su hoda da wayarta a hannu.

Tun daga kofar gidan Mami da suke jiranta saboda motocin a can aka ajiyesu Awwab yake kallonta ya kasa dauke ido. Wani mahaukacin kishi ne ya taso ya rufe shi da ya ga kamar duka hankula suna kanta ne. Itama shi take kallo tana murmushin da yake kara susuta tunaninsa. Gaskiya motar da zai ja yake so ta shiga ta zauna a kusa dashi. Da ka yayi mata alamar ta taho ai kuwa ta nufi motar. Sai da ta tsaya a gaba kamar zata bude ta juya wurinsu Fauziyya.

"Adda wannan zaki tuka?"

"Wannan Hamma ne zai ja"

"Ohhh" ta juya ta koma jikin daya motar ta shiga baya ita da Zahra da Femi. Gaba kuma Zayyana ce da Jawad sai Fauziyya da zata ja su.

"Rufe bakin mana loverboy" Raji yace da turanci suka tafa da Yousuf suna yiwa Awwab dariya. Wai shi zata yiwa haka ta sa masa rai ta basar. Ba don gudun fadan Ummi ba da babu inda zai je saboda bashi da kuzarin tukin ma. Wani kallo ya watsa musu suka sake kwashewa da dariya sannan suka shiga motar yana gaba Fauziyya na binsa a baya.

"Radhiya ba sauki yau kin motsa mana Hamma. Jikina yana bani kamar da wuya ki koma France babu aure fa kila ma da dan guzuri"

Zahra ce ta zunguro Fauziyya rainon Mama zata yi barin zance a gaban Zayyana. Jinsu kawai take tana murmushi da kewar 'yan uwanta Ibrahim abokin fada da Emzee mai lallabata. Da suna nan ko kallon wannan motar bazata yi ba. Radhiya tayi murmushi kawai zuciyarta fes. Masu sayar da irin lemukan nan da ake saka kankara a leda ta hango maltina yawunta ta tsinke. Da can bata iya sha har cewa suke giya ce. Zuwanta na karshe ta dandana shikenan ya zama abin shanta har da guzuri da zata koma.

"Adda don Allah saya min maltina"

"Wacce a ciki? Nima fakiriya ce irinki babu chanji a hannuna" Zahra ta amsa mata.

Dan turo kanta tayi gaba "Adda Fauzinmu taimaka"

"Ni da kika ki shirya min yaro harda harara"

"Yanzu kullata ta kika yi a ranki kamar ba babba ba? An dai yi abin kunya"

Yadda tayi maganar yasa su duka dariya. Zahra tace "Wani idan ya kalleki a haka dai zai ce irin high class babes dinnan ne. Sai an zauna dake a gane ashe 'yar soja ce mai balotelli"

Rokon maltina ta cigaba duk junction amma Fauziyya taki saya. 

"Ki roki Hamma idan mun tsaya"

"Roko zaki koya min?" Ta zaro idanu.

"Kayan masoyi ai naki ne...ke da kuke sharing spoon meye don ya saya miki maltina?"

Bata sake iya magana ba taji kunya ta koma ta zauna shiru har suka isa. Ita bata taba zuwa gidan ba. Su kuma rabon su da zuwa tun bikin Ghazalatu farkon tafiyar Awwab Ukraine. Su ne a gaba ita a karshe suka bi bayan mazan zuwa cikin gidan.

Zahra ke ta sallama shiru ba'a amsa ba. Mai aiki ce ta leko daga baya lokacin Awwab ya fara jin haushin zuwan nasu tace su shigo Mummy tana sama za ta yi mata magana.

"Kice mata su Zayyana ne" Zahra tace su duka suka sami wuri suka zauna a falon da mai aikin ta kaisu. 

Muryar mace tana kuka suka ji wata  tana daga murya "Mummy ba fa zan koma ya kasheni ba"

Kafin Mummy Gambo tace wani abu mai aikin ta fada mata suna da baki.

"Su waye?"

"Wai su Zayyana"

A dan tsorace tace "ba dai falon kasan nan kika kawo min su ba ko"

"Mummy ke kika ce nan zan rinka kawo bakinki"

Ranta a bace kamar ta kai mata duka ta fasa tana huci. Karshenta sun ji hargagin Ghazalatu. Tsaki tayi tace ta kai musu abin sha tana saukowa. Bayan fitarta ta koma kallon Ghazalatu da ta rame tayi baki kamar ta dade tana cuta. Ga fuska a kumbure. Ido daya yayi ja jini ya kwanta.

"Sami wuri ki kwanta zan kira Hussaina idan sun tafi ba aura masa ke akayi don ya kasheki ba"

Cikin takun kasaita ta sauko ta ga falon nata a cike. Duk yadda taso daure fuska kasawa tayi tana ganin Jawad da Femi suna ta kai kawo babu mai shekara biyu cikinsu amma duka akwai girman jiki da lafiya. Iyayensu sun gaisheta harda Radhiya da bata gane ba ta dan saki fuska tana yiwa su Jawad wasa.

"Yaya Mamin taku kowa lafiya ko?"

Zayyana ce ta amsa da "lafiya kalau"

"Madallah, ku masu gida ina cefane ko haka kuka zo min hannu na dukan aljihu?"

Dariya ce su Fauziyya ke yi ta yake kowa ta ciki na ciki yadda ta yiwa Maminsu rashin mutumci musamman da bikin Ghazalatu.

"Awwab yaushe a gari? Yaya aiki?"

"Shekaranjiya muka zo da Zahra. Ga mijinta Raji"

A ladabce Raji ya sake gaisheta don Yarbawa akwai ladabi sosai. Kyakyawan mutum a haka harda dan gemunsa na ustazai amma ita ce mai yadawa a dangi cewa Zahra ta rasa miji an buge da auren bayerabe. Sai gashi a gidanta ido ba mudu ba yasan kima tasan cewa babu tsiya a tare dashi. Kyakkyawar yarinyar da take ta wasa da Femi ta kalla "wannan fa, bakuwa kuka yi?"

"Radhiyan Hamma Awwab ce" Fauziyya tace kai tsaye lokacin da Ghazalatu take saukowa. Ita da Mummyn suka zuba mata idanu sai ta basar duk da ta sake takura ta koma gaishe da Mummyn.

Ghazalatu kamar ta juya ta koma don bakinciki. Radhiya dai da ta sani 'yar kauye mai askakken kai ce a haka kamar wata balarabiya. Murmushin da Radhiyan tayi tana kallon Awwab shi ya gaskakata mata ita saboda wannan dimple din nata. Mayar mata da martani yayi har yaso ya manta a ina suke.   

Kishi fal a cikin Ghazalatu ta kalli Awwab yadda ya sake zama babba ga cika ido. Sai zaman ya koma na kurame tunda akace Daddy Haroun baya nan. Mummy tana hango wautarsu Ghazalatu tana jin takaicin rabasu da Mummyn tayi. Nura dukanta yake kamar jaka idan Mummy tayi magana sai Hussaina tace Ghazalatun ce bata da tarbiya. Kudi ne suka so tatsa Mummy taki saki shiyasa suka dorawa 'yarta karan tsana. Drinks aka kawo harda maltina amma Radhiya ta kasa sha musamma da Ghazalatu ta rinka jan Awwab da hirar aiki da course da taji yaje Ukraine.

"Muna jiran tsarabarmu"

Tausayi take bashi yana son tambayar me ya sami idonta yana tunanin kada ya bata kunya sai yace "zan kawo miki kafin ki koma KT. Bari mu wuce muna sauri ne"

"Da wuri haka Awwab ina zaku je, zaku dawo ku gaisa da Daddy ko"

Fauziyya ce ta sake cafewa "gidan abokin baban Radhiya"

Ghazalatu tace "a nan din? Nufina a Abujan nan? Cikin Nyanya hala"

Cin fuska Awwab ya hade rai Zayyana ma da abin ya bata haushi tace "gidan gwamnan Plateau a Asokoro"

Mummy sai ta hangame baki tsabar mamaki. Kai gidan gwamna ai da mutane kila dai maigadi ko irin gardiner dinnan.

"Hamma kafin ya fara kira yace ya jimu shiru. Kasan halinsa da yaji Radhiya tazo Nigeria ya rinka damuwa kenan"

Sakato Ghazalatu tayi tana kallon su "ba a Nigeria take ba?" Tace da mamaki Radhiya kunya ta kamata yadda su Zahra suke jindadin abinda suke yi musu.

"Kakanta ya kaita France ai can take karatunta"

Awwab kasa jurewa dramar matan yayi yace su fito haka. Harabar gidan Mummy ta rakosu tana takaicin me ya rabata da yayarta mai sonta da zuciya daya da yaranta. Ta dawo daga rakiyar Hussaina amma kunya harda ta Ummansu ta kasa fadawa kowa halin da ake ciki.

Suna mota Fauziyya tace "dalla muna ta wasa ki maimakon ki turance su ko kiyi french ke da Yousuf tunda ba kowa ke jinsa ba ki tada hankalin 'yan bakinciki"

"Naga alama kin fini rigima yanzu Adda"

"Hmmm ai dole bakina ya bude in fada miki 'yan mata sun saka min miji a gaba da waya. Shi kuma ya fiye shiru shirun wai wulakanci babu kyau. Tuni na mike kafin ya dauko min qaya"

"Su Fauziyya an iya kishi"

"Allah Yasa my in law ya kyallo wata idan kunje garinsu"

"Ba amin ba"

Radhiya da Zayyana suka rinka dariya yadda yayyen nasu ke fadan sakuwa da sakuwa.

An san da zuwansu gidan Excellency suna isa aka bude musu gate. Cikin girmamawa aka kaisu falon matar gidan. Bata da ji da kai kamar mijinta ta rinka jansu da hira tana fada musu me yiwuwa fa sai sun dawo cikin sati saboda jibi Excellency zai taho.

"Munyi waya nake ce masa zaku zo yace gobe yana son ganinka da wuri Awwab wai akwai important issue da zakuyi discussing" 

"Ko maganar Arifah ce" da yake ta nuna sha'awar zuwa Ukraine masters yace sai ya tambayi Awwab yanayin kasar.

Radhiya sai ta zaci ko maganar hadin aure ce kishinta ya motsa. Suna haka Radhiyan ta shigo tabi matan nan kowacce ta rungume tana murnar ganinsu.

"Ashe duka kunzo babu gayyata. Mom kinga ni nake son zumunci dasu basa nemana. Captain ne nawa shi kam bama kwana uku bamu gaisa ba"

Ta sake kunna Radhiya bata sani ba. Wancan karon Ghazalatu yanzu kuma Arifa. Itama haka zai zo yace ta hakura ya fara aurenta? Zaman sai taji ya isheta so take su tafi kawai. Tana kallo suka tashi suka bi wata kofa Mom dinta na cewa dama an dade ba a hadu ba yau tasan zasu sha hira ne.

Haushin kowa ta rinka ji harda su Fauziyya. Basu dade ba suka dawo ta fada masa ne Excellency ya karbi nambar wayarsa a wurinta yace zai kira shi kada yaji waya bazata ya dauka wani abu ne. Suna dawowa yace zasu tafi Mom ta hada kowa da gift tana ta godiya. 

A jikin motar da matan suke Arifah tace musu gobe idan suna da lokaci me zai hana su je park. So take su saba da juna sosai. Zahra ta amince ko don mijinta mai zuwa camping a filling station.

**********[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: *SAKAMAKON ALKHAIRI...ALKHAIRI NE*
Chapter 83 · 0% Book details