Sashe 116
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hamdala ya rinka yi babu tsayawa a lokacin da yaji kammaluwar komai Schatzi dinsa ta zama tasa halak malak. Hotuna ake ta yi da gaishe gaishe na 'yan uwa da abokan iyayensu. Malamijo da tawagarsa kadai sun isa gayya. Gidansu Zayyan aka wuce ya sakarwa 'yan uwansa da matansu Badaru ragamar girkin da za'a ciyar da mutane kafin su tafi. Da farko Mairama yaso su zo su kwana a garin domin yin abincin ita kuma tace dama ce ta nuna musu yana kaunarsu kuma ya yarda dasu. Ai kuwa basu bashi kunya ba domin kowa yaci ya sha anyi abu cikin girma. Kuma sai da Baban Arifah ya samu yazo shima duk da mutanen da ya baro a gida. Maikudi ne dai idan akwai namijin mujiya to shi ne a wannan taron. Yana ta rakubewa a gefe Zayyan sai ya dauke kansa kawai. Daga baya ya ga bai da amfani nunawa duniya akwai baraka tsakaninsu shiyasa ya koma sako shi cikin al'amuran. Da yace Maikudi kuwa sai ka ganshi da mugun sauri ya taho.
Ba su suka sami saukin kebewa daga mutane ba sai lokacin da ya idar da sallar la'asar. Yana zaune da 'yar cikinsa ya ajiye babbar rigar da hula can gefe. Bayan doguwar addu'a ya dauko wayarsa ya turawa Radhiya text din da yake ta son yi tun bayan an daura auren.
(Ina hukuncin matar da bata daukar wayar mijinta? Ki fada mata Awwab ya zama na Alheran kuma ta shirya karbar punishment dinta na share shi).
Hira suke yi da Fauziyya da Zahra rabi suna tsokanarta rabi kuma shawarwari ne suke bata tunda yanzu itama girma yazo. Ita dai jiki yayi sanyi kamar ba ita ba. Wani abin tayi dariya wani kuwa sai dai taji kunya idan sun fada amma ta kasa magana. Duk da ba bikin bane ya taso amma gidan ya rude don ma anyi sa'ar kawowa Ummi masu aiki biyu 'yar dattijuwa da kuma mai sauran kuruciya.
Sakon Awwab ta karanta suka ga murmushin nata ya koma na daban.
Fauziyya ta dago wuya zata leka wayar "Ango ya miko gausuwa kenan...mu gani me yace"
Janyota Zahra tayi "ina ruwanki, idan kin matsu kiji me yace nemi naki mijin tunda suna tare kema yayi miki text din. Radhiya tashi ki koma daki kiyi magana da mijinki kinji"
Kasa mikewa tayi Fauziyya ta cigaba da zolayarta sai da Zahra tayi da gaske don ta kula jikin kanwar tasu mai sabon mukamin matar yaya yayi mugun sanyi. Tana tafiya Fauziyya ta tallabe kanta da hannu biyu.
"Jikin ta kanwa yayi la'asar fa Sis. Duk surutunta kinga fa bakin ya mutu. Allah sarki irin matsoratan amaren nan za'ayi"
"Tausayinta kike ji ko tsokana?"
"Tausayin dai...hmmm kazo kayi ciki ka rasa inda za ka tsoma ranka kaji dadi"
Tuntsirewa da dariya Zahra tayi ta gano Fauziyya laulayi ne yasa ta a gaba shine za ta saka mutane itama.
Bayan Radhiya ta koma dakin babu kowa. Gefen da tayi sallah ta kalla ta tuna nasihar da Mama tayi mata a wurin bayan ta umarceta da tayi nafila ta godewa Allah bayan an daura auren. Wata irin soyayyar Awwab take ji tana kara shigarta sosai ta lumshe idanu ta kwanta sannan ta kira shi.
Sautin numfashinsa ne ya sanar da ita ya dauka amma yaki yi mata magana shima nata hawa da saukar numfashin kadai yake sauraro wanda ya kara masa gudun bugawar zuciyarsa.
Ita ta fara kartse shirun nasu ta hanyar gaishe shi da tattausar murya "Hammana ina wuni"
Da kyar ya iya hada kuzarin amsawa yana jin kamar yau ya fara son ta "Matsoraciya yaya kike?"
"Tsoron me nake yi?"
"Daga kinji nace zaki karbi punishment shine kika dawo daga strike din yi min magana mana"
Kamar yana gabanta ta tura baki "to ba kaine ba"
Katseta yayi don yasan fushin har yanzu na menene "Ko ba ni zan aureki ba kinsan bazan yi missing aurenki ba bare kuma Alheran din ta Awwab ce"
Kunya taji sosai yayi murmushi ganin yau ita ce babu baki "wai ni tun yanzu ina bakin naki ya koma ne? Anya zamu shirya da wannan amaryar kuwa wata bebeya nan da ita"
Ibrahim ne yayi masa alama da hannu motocin da zasu kwashesu sun iso. Ba yadda ya iya sallama yayi mata yace tayi musu addu'a gasu nan fitowa zasu taho. Kafin su iso anyi abinci sosai jiran isowarsu kawai akeyi. Kowa yaci ya koshi kuwa sai son barka aure ya yi albarka sai fatan zaman lafiya ga sababbin ma'auratan.
A gajiye su ka dawo ana sallar isha kowa sai bacci. Angwayen biyu, Raji da Bilal suna gidan Mami. Ibrahim da Emzee kuwa gidan Mama. Daya ga wata ta matso babu lokacin zama babban taron da ake ta jira ne Allah Ya kawo shi. A haka ma da ba su ne suka shirya ba basu da zama balle kuma na washegarin da yake nasu.
Dadin abin ma kuma domin tallata shirin Radhiya Baban Arifah ya samu yace a saka wani bangare nashi a wurin taron tunda shugaban kasa zai je. Ita kuma sai ta gaggauta sanar da Supervisor dinta domin ta nema mata izini. Kwana biyu a tsakani matar ta fada mata cewa su uku an wakiltasu zuwa su gani sannan su tayata murnar dawowar mahaifinta. Ranar kwanan murna tayi sai gashi ana gobe taron sun iso. Duk wannan lokacin angon nata yayi wuyar gani suyi nan suyi can saboda ganin sun kammala komai bisa tsari yadda suke so.
Malamijo da kansa ya hada mutum biyar cikin masu zuwa taron daga gidansa a yara sai kuma Yadikko da Hajjo. Shatar mota yayi musu ana shirin tafiya sai ga Salame niki niki da kaya ita da yaranta wai itama zata je. Ba wani abu bane ya tunzurota kuwa sai labarin da ta samu na cewa Rahima ashe ta bi Mairama. Zuwa zata yi har gidan taci mutumcin yarinyar tunda tana son nunawa makiyanta cewa bata isa ba. Abu na biyu kuma so take taje ta ganewa idanunta wace irin rayuwa Mairama da Zayyan suke yi da akaje daurin auren 'yarsu a Sakkwato aka dawo ana zuzuta taron da angon da Radhiya ta dace da shi. Malamijo bai hanata zuwa ba amma da karamar 'yarta kadai ya yarda taje sauran ya turasu cikin gidansa.
Tunda aka shigo garin Abuja bakin Salame yaki rufuwa tana ta kalle kalle. A tasha dreban ya tsaya aka tura wani dreban daga gidan yaje ya taho dasu. Nan fa cikin Salame ya duri ruwa ganin sojoji da bindiga tun daga bakin gate din wani irin katon gida mai kyau. Jikinta yayi sanyi kalau ba ta fatan ace wannan ne gidan Mairama. Bata gama tunanin ba kuwa aka wangale gate din gidan. Wani bacin rai taji ya tuko ta da fa yanzu gidan nan nata ne ba don bakincikin da Mairama tayi mata ba. Suna shiga Ummi da kanta ta fito tarbarsu da murnarta tare da Rahima wadda tun safe da tace mata Malamijo yace da Salame za'a taho jikinta yayi sanyi. Ummi tana kula da duk motsin yarinyar kuzarinta ya ragu sai kayi mata magana bata ji ba saboda zulumi.
Ashe kuwa ba a banza ba don suna saukowa daga mota da ta tafi da murnarta saboda tana son Umman nata taje ta durkusa har kasa tana gaisheta. Kusan hambareta Salame tayi kafin ta dangwara mata yarinyar da ta kai shekara uku tana wani irin wari.
"Ki wuce da ita ki gyara mata jiki tayi kashi sannan ki bata abinci "
Jiki na rawa Rahima ta karbi yarinyar da kafarta da komai amma dole ta dauketa ta wuce Ummi ta shiga ciki. Itama Ummin ba ta niyar koyawa Rahima rashin kunya dole ta bi umarnin mahaifiyarta. Sakin fuska tayi tana musu maraba. Salame tana ta wani basarwa ita bata ga abin burgewa ba har suka shiga ciki. Tun daga katon falon zaka san gida ne na wanda ya isa duniya take damawa dashi. Dakunan da zasu zauna ta nuna musu da kanta su Radhiya suka zo gaishesu ita da Zayyana da Hibbah wadda tayiwa gidansu kaura duk da cewa Maman tasu tana gari. Duj inda 'yan mata suka hadu sunfi jindadin kasancewa tare musamman idan tasu tazo daya.
Rahima wanka ta shiga yiwa kanwarta Khadi yarinyar tana ta yi mata rashin kunya
"Ki dena tabani"
"Kin kona ni"
"Sai na fadawa Umma"
"Ni ki bani sabulun da kaina dan wanke"
Radhiya tuni ta hasala ta fada bandakin tace Rahima ta fita ta karbo mata kaya. Wani irin kallo ta yiwa Khadi yarinya ta bare baki za tayi kuka ta daure fuska "kina yi min kuka zan cillaki ta taga kowa ya huta mara kunyar kawai"
Yadda bata ga alamun wasa a fuskar Radhiya ba sai ta hadiya kukan dama na samun wuri ne tayi mata wanka kamar tayi amai ace yarinya kamar wannan tana kashi a wando ga wani kai a daddage babu gyara anyi kitson roba da yawa sun warware. Zuge sauran tayi ta zuba mata shampoo akan ta soma kukan sai ta fadawa Umma saboda bata yarda a taba mata kai ko Salamen sai tayi ta lallabata tunda tana ji da ita. Radhiya bata sake bi ta kan rarrashi ba sai da ta wanke kan nan tayi mata wankan.
A kasa kuma Rahima dakin da suke taje a gaban Salame ta durkusa tace a bata kayan Khadi.
"Kin wanke wadancan ko kuwa ni zaki kawowa na wanke?"
"Yanzu zan wanke Umma"
Hajjo tuni ta fara zuwa wuya a kufule tace "Salame idan kinsan zuwa kikayi ki tsangwami yarinyar nan ina mai tabbatar miki yanzu zan kira Malamijo a mayar dake gida. Shashancin banza da hofi kai. Rahima ga jakarta can bude ki dauka"
Ummi tana wurin ita abin na Salame yanzu tausayi ne take bata saboda ta hana kanta sakewa ta hana wasu. Rahima da ta duba kayan ashe na babbar Salame ta dauko garin haushin an hanata zuwa da dukkansu. Rigunan sunyi girma haka dai ta dauki wata riga zata saka mata ga pants din duk na babbar. A kanta Salame ta huce haushin rashin dauko kayan daidai tana ta yi mata fada saboda bata san yadda zata yi ba.
Ummi ta kada kai "Rahima anjima bayan magariba kizo na aikeki dasu Zayyana"
Ba su suka sami saukin kebewa daga mutane ba sai lokacin da ya idar da sallar la'asar. Yana zaune da 'yar cikinsa ya ajiye babbar rigar da hula can gefe. Bayan doguwar addu'a ya dauko wayarsa ya turawa Radhiya text din da yake ta son yi tun bayan an daura auren.
(Ina hukuncin matar da bata daukar wayar mijinta? Ki fada mata Awwab ya zama na Alheran kuma ta shirya karbar punishment dinta na share shi).
Hira suke yi da Fauziyya da Zahra rabi suna tsokanarta rabi kuma shawarwari ne suke bata tunda yanzu itama girma yazo. Ita dai jiki yayi sanyi kamar ba ita ba. Wani abin tayi dariya wani kuwa sai dai taji kunya idan sun fada amma ta kasa magana. Duk da ba bikin bane ya taso amma gidan ya rude don ma anyi sa'ar kawowa Ummi masu aiki biyu 'yar dattijuwa da kuma mai sauran kuruciya.
Sakon Awwab ta karanta suka ga murmushin nata ya koma na daban.
Fauziyya ta dago wuya zata leka wayar "Ango ya miko gausuwa kenan...mu gani me yace"
Janyota Zahra tayi "ina ruwanki, idan kin matsu kiji me yace nemi naki mijin tunda suna tare kema yayi miki text din. Radhiya tashi ki koma daki kiyi magana da mijinki kinji"
Kasa mikewa tayi Fauziyya ta cigaba da zolayarta sai da Zahra tayi da gaske don ta kula jikin kanwar tasu mai sabon mukamin matar yaya yayi mugun sanyi. Tana tafiya Fauziyya ta tallabe kanta da hannu biyu.
"Jikin ta kanwa yayi la'asar fa Sis. Duk surutunta kinga fa bakin ya mutu. Allah sarki irin matsoratan amaren nan za'ayi"
"Tausayinta kike ji ko tsokana?"
"Tausayin dai...hmmm kazo kayi ciki ka rasa inda za ka tsoma ranka kaji dadi"
Tuntsirewa da dariya Zahra tayi ta gano Fauziyya laulayi ne yasa ta a gaba shine za ta saka mutane itama.
Bayan Radhiya ta koma dakin babu kowa. Gefen da tayi sallah ta kalla ta tuna nasihar da Mama tayi mata a wurin bayan ta umarceta da tayi nafila ta godewa Allah bayan an daura auren. Wata irin soyayyar Awwab take ji tana kara shigarta sosai ta lumshe idanu ta kwanta sannan ta kira shi.
Sautin numfashinsa ne ya sanar da ita ya dauka amma yaki yi mata magana shima nata hawa da saukar numfashin kadai yake sauraro wanda ya kara masa gudun bugawar zuciyarsa.
Ita ta fara kartse shirun nasu ta hanyar gaishe shi da tattausar murya "Hammana ina wuni"
Da kyar ya iya hada kuzarin amsawa yana jin kamar yau ya fara son ta "Matsoraciya yaya kike?"
"Tsoron me nake yi?"
"Daga kinji nace zaki karbi punishment shine kika dawo daga strike din yi min magana mana"
Kamar yana gabanta ta tura baki "to ba kaine ba"
Katseta yayi don yasan fushin har yanzu na menene "Ko ba ni zan aureki ba kinsan bazan yi missing aurenki ba bare kuma Alheran din ta Awwab ce"
Kunya taji sosai yayi murmushi ganin yau ita ce babu baki "wai ni tun yanzu ina bakin naki ya koma ne? Anya zamu shirya da wannan amaryar kuwa wata bebeya nan da ita"
Ibrahim ne yayi masa alama da hannu motocin da zasu kwashesu sun iso. Ba yadda ya iya sallama yayi mata yace tayi musu addu'a gasu nan fitowa zasu taho. Kafin su iso anyi abinci sosai jiran isowarsu kawai akeyi. Kowa yaci ya koshi kuwa sai son barka aure ya yi albarka sai fatan zaman lafiya ga sababbin ma'auratan.
A gajiye su ka dawo ana sallar isha kowa sai bacci. Angwayen biyu, Raji da Bilal suna gidan Mami. Ibrahim da Emzee kuwa gidan Mama. Daya ga wata ta matso babu lokacin zama babban taron da ake ta jira ne Allah Ya kawo shi. A haka ma da ba su ne suka shirya ba basu da zama balle kuma na washegarin da yake nasu.
Dadin abin ma kuma domin tallata shirin Radhiya Baban Arifah ya samu yace a saka wani bangare nashi a wurin taron tunda shugaban kasa zai je. Ita kuma sai ta gaggauta sanar da Supervisor dinta domin ta nema mata izini. Kwana biyu a tsakani matar ta fada mata cewa su uku an wakiltasu zuwa su gani sannan su tayata murnar dawowar mahaifinta. Ranar kwanan murna tayi sai gashi ana gobe taron sun iso. Duk wannan lokacin angon nata yayi wuyar gani suyi nan suyi can saboda ganin sun kammala komai bisa tsari yadda suke so.
Malamijo da kansa ya hada mutum biyar cikin masu zuwa taron daga gidansa a yara sai kuma Yadikko da Hajjo. Shatar mota yayi musu ana shirin tafiya sai ga Salame niki niki da kaya ita da yaranta wai itama zata je. Ba wani abu bane ya tunzurota kuwa sai labarin da ta samu na cewa Rahima ashe ta bi Mairama. Zuwa zata yi har gidan taci mutumcin yarinyar tunda tana son nunawa makiyanta cewa bata isa ba. Abu na biyu kuma so take taje ta ganewa idanunta wace irin rayuwa Mairama da Zayyan suke yi da akaje daurin auren 'yarsu a Sakkwato aka dawo ana zuzuta taron da angon da Radhiya ta dace da shi. Malamijo bai hanata zuwa ba amma da karamar 'yarta kadai ya yarda taje sauran ya turasu cikin gidansa.
Tunda aka shigo garin Abuja bakin Salame yaki rufuwa tana ta kalle kalle. A tasha dreban ya tsaya aka tura wani dreban daga gidan yaje ya taho dasu. Nan fa cikin Salame ya duri ruwa ganin sojoji da bindiga tun daga bakin gate din wani irin katon gida mai kyau. Jikinta yayi sanyi kalau ba ta fatan ace wannan ne gidan Mairama. Bata gama tunanin ba kuwa aka wangale gate din gidan. Wani bacin rai taji ya tuko ta da fa yanzu gidan nan nata ne ba don bakincikin da Mairama tayi mata ba. Suna shiga Ummi da kanta ta fito tarbarsu da murnarta tare da Rahima wadda tun safe da tace mata Malamijo yace da Salame za'a taho jikinta yayi sanyi. Ummi tana kula da duk motsin yarinyar kuzarinta ya ragu sai kayi mata magana bata ji ba saboda zulumi.
Ashe kuwa ba a banza ba don suna saukowa daga mota da ta tafi da murnarta saboda tana son Umman nata taje ta durkusa har kasa tana gaisheta. Kusan hambareta Salame tayi kafin ta dangwara mata yarinyar da ta kai shekara uku tana wani irin wari.
"Ki wuce da ita ki gyara mata jiki tayi kashi sannan ki bata abinci "
Jiki na rawa Rahima ta karbi yarinyar da kafarta da komai amma dole ta dauketa ta wuce Ummi ta shiga ciki. Itama Ummin ba ta niyar koyawa Rahima rashin kunya dole ta bi umarnin mahaifiyarta. Sakin fuska tayi tana musu maraba. Salame tana ta wani basarwa ita bata ga abin burgewa ba har suka shiga ciki. Tun daga katon falon zaka san gida ne na wanda ya isa duniya take damawa dashi. Dakunan da zasu zauna ta nuna musu da kanta su Radhiya suka zo gaishesu ita da Zayyana da Hibbah wadda tayiwa gidansu kaura duk da cewa Maman tasu tana gari. Duj inda 'yan mata suka hadu sunfi jindadin kasancewa tare musamman idan tasu tazo daya.
Rahima wanka ta shiga yiwa kanwarta Khadi yarinyar tana ta yi mata rashin kunya
"Ki dena tabani"
"Kin kona ni"
"Sai na fadawa Umma"
"Ni ki bani sabulun da kaina dan wanke"
Radhiya tuni ta hasala ta fada bandakin tace Rahima ta fita ta karbo mata kaya. Wani irin kallo ta yiwa Khadi yarinya ta bare baki za tayi kuka ta daure fuska "kina yi min kuka zan cillaki ta taga kowa ya huta mara kunyar kawai"
Yadda bata ga alamun wasa a fuskar Radhiya ba sai ta hadiya kukan dama na samun wuri ne tayi mata wanka kamar tayi amai ace yarinya kamar wannan tana kashi a wando ga wani kai a daddage babu gyara anyi kitson roba da yawa sun warware. Zuge sauran tayi ta zuba mata shampoo akan ta soma kukan sai ta fadawa Umma saboda bata yarda a taba mata kai ko Salamen sai tayi ta lallabata tunda tana ji da ita. Radhiya bata sake bi ta kan rarrashi ba sai da ta wanke kan nan tayi mata wankan.
A kasa kuma Rahima dakin da suke taje a gaban Salame ta durkusa tace a bata kayan Khadi.
"Kin wanke wadancan ko kuwa ni zaki kawowa na wanke?"
"Yanzu zan wanke Umma"
Hajjo tuni ta fara zuwa wuya a kufule tace "Salame idan kinsan zuwa kikayi ki tsangwami yarinyar nan ina mai tabbatar miki yanzu zan kira Malamijo a mayar dake gida. Shashancin banza da hofi kai. Rahima ga jakarta can bude ki dauka"
Ummi tana wurin ita abin na Salame yanzu tausayi ne take bata saboda ta hana kanta sakewa ta hana wasu. Rahima da ta duba kayan ashe na babbar Salame ta dauko garin haushin an hanata zuwa da dukkansu. Rigunan sunyi girma haka dai ta dauki wata riga zata saka mata ga pants din duk na babbar. A kanta Salame ta huce haushin rashin dauko kayan daidai tana ta yi mata fada saboda bata san yadda zata yi ba.
Ummi ta kada kai "Rahima anjima bayan magariba kizo na aikeki dasu Zayyana"