Sashe 122
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kowa ya sani a Nigeria biyu ga watan junairu ana tsaka da sanyi ne amma banda Salame matar Haji Indararo. Gumi take kashirban tana yiwa Emzee tofin Allah tsine. Lokacin da suka isa wurin yayi sa'ar ganin wata motar na fita yasan zai sami wurin parking. Katinsa ya nuna aka wangale gate ya shiga Salame tana ta numfarfashi. Yana tsayawa ta kama kofa zata fita taji a datse.
Ashe harda hawayen wahala tayi bata sani ba cikin fada tace "shegen yaro mai kama da ifiritu bude min"
Emzee a soja yake baka ganin wani abu wai shi sani ko sabo a tattare dashi sai murmushin mugunta "kinfi kowa sanin cewar ina da uba mijin kanwarki....ko ince mutumin da kike so?" Ya yi mata wani kallon gefe.
Jikin Salame ya bugu saboda tukin da ya yi amma abinda yafi daga mata hankali bai wuce maganar da yayi ba. A ina yaji? Mairama ce ta fada masa ko waye? Karfin hali tayi ta daure fuska.
"Rashin kunyar taka har ta kai haka Karami? Irin tarbiyar da Mairama take baku kenan ashe, kun tashi ba ku ganin girman kowa"
Juyowa Emzee yayi ya mata wani kallo mai firgitarwa kamaninsa sun sauya gabadaya...soja mazan fama.
"Kada ki kuma ambaton sunan Ummina domin tunda take bata taba nakasa dabba ba bare mutum"
"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun" Salame ta fada a tsorace jikinta yana tsuma baki na rawa "me...me kake nufi? Sharri za ka yi min kace ni na makanta ta?"
Sai da kansa ya sara a lokacin domin dama bugun cikinta yayi ya bata tsoro domin jin gaskiyar lamari kuma yaji abinda yake so kafin ma ya tambaya. Duk da yana zargin tabbas ita ce amma yanzu da ya tabbatar sai da abin ya girgiza shi matuka. Ba ya kaunar Salame ko na digon sakan saboda bata cancanci a sota ba. Umminsa tana makance tsayin shekaru Salame tana gidan miji tana ciki da haihuwa taci me kyau tasha me kyau lokacin gwamnatinta na ci a zuciyar Alh Indararo.
"Kuruciya tasa ban fahimci me kika yi ba shiyasa ban tona miki asiri ba tun lokacin da kika saka mata...." yace don ya kara tunzurata yana bude dash board.
Sabon gumi na yake tsattsafo mata jin sirrin boye da ko da kanta bata zancen a zuci yau Emzee ya bankado shi. Harda sanyi ta rinka ji yana ratsata ya cigaba da lalubensa kamar ba ta cikin motar.
Hakoranta sai sarkewa suke yi don tsoro tace "to yanzu kuma uban me kake lalube bayan ka gama yi min sharrin"
"Bindiga"
Idanunta kamar zasu fado karshen tsoro ta kai sannan ga uwa uba wani mahaukacin zawo da ya matsota saboda tsoro.
"An...an. fada. Maka idan...idan ka kasheni. Mairama zata yi murna ne?"
Bude pin din motar yayi "kin zata harbinki zanyi? Allah Ya kiyaye ba'ayi min wannan tarbiyar ba"
Budewa tayi da sauri ya leka da kansa ta inda ta tashi "uhmm nace ba....nagode da kika tabbatar min da zargina akan waye ya makanta min uwa"
Salame sai bude baki tayi tana masa kallon tsananin mamaki shi kuwa ya zura hannu ya janyo kofar ya rufe ta bangaren da take sannan ya kifa kai akan sitiyari yana kokarin mayarda hawayen bakincikin da suke neman zuwar masa. Dago kai yayi ya nemi wayarsa sai ya ga har lokacin tana tsaye. Da kallo daya ya karasa razana ta ta wuce ciki wurin da ake ta karbar baki za'a fara abinda ya tara jama'a.
Yau ranar farinciki ce dole ya saita kansa. Ibrahim ya kira bugu daya ya dauka.
"Bro turo min Rahima" yace da wata iron murya can kasa.
"Bangane ba. Ba tare kuke ba?" Zai sake magana ya hangota tare da Zayyana zasu zauna "kana ina ne na ganta"
Kwatanta masa inda yayi parking Emzee yayi Ibrahim yaje inda suke ya fadawa Zayyana ita kuma ta fada mata. Tana tashi bayan ta ajiye Khadi akan kujerarta ta hango Salame amma da ta ga hankalinta baya gareta sai ta wuce ta tafi.
Ya gama saka rigarsa kenan yana gyara zaman hular a kansa ta bullo. Shagala Emzee yayi da yadda Rahima take tafiya cikin nutsuwa. Yanayin da ya shiga mai wuyar fassara soyayyarta ta mamaye masa kowane lungu da sako na zuciyarsa. Duk kunya ta isheta saboda yadda ya kafeta da ido har ta karaso.
"Mu zauna a nan ko mu shiga ciki?" Yace yana fatan ta amince su zauna.
"Za'a nemeka ai"
"Okay muje" sun fara tafiya ya ga dacewar ya bata hakuri akan abinda yayar mahaifiyarsa tayi musu "Rahima kiyi hakuri akan abinda ya faru dazu. Na saka ki zaman jirana kuma bani na kawoki ba"
Ita da tasan mahaifiyarta ce tayi sai tayi saurin cewa "ni ya kamata na baka hakuri"
"Akan me? For being a good girl me jin maganarrr.....maganar wa dinki kika ji?" Ya zuba mata idanu.
Murmushi tayi kanta a kasa "Ya Emzee?"
"Nope" tsayuwa yayi ya hanata tafiya "Rahima wane matsayi kika bani?"
Kasa magana tayi tambayar tayi mata nauyi duk da amsarta tana jin tamkar ta amayo masa ita ne ko za ta sami saukin wannan soyayya da tayi mata mugun kamu.
Kamar yayi mata kuka saboda taki magana "gobe zan koma Kaduna da sassafe. Please Rahima ki fada min ni waye a gareki kafin na tafi....idan ba haka ba retire zanyi tun kafin na fara aikin na dawo ga filin yaki nan in your beautiful eyes muyi ta fafatawa."
Zuwa yanzu ko fuskarta baya iya gani ta shige cikin mayafin ta rufe kanta gabadaya sai murmushi kawai take yi. Da kyar ta iya cewa "ni wa dinka ce to?"
"My heart..." yace da sauri "ke fa?"
Babu wanda zai wuce ya gansu baiyi musu kallo na biyu ba. Kana ganinsu ka ga masoyan da suka mutu akan juna kuma suka dace sosai da juna. Emzee fari ne kamar yayarsa ga kyau ga jikin matashin soja. Rahima kuwa baka ce fatarta tafi kama da wankan tawarda don da kadan Zayyana ta fita haske. Kyakkyawa ce sosai tafi Halifa da sauran 'ya'yan Salame nesa ba kusa ba sai dai su nuna mata haske. Round shaped eyes dinta sunfi komai daukar hankali akan fuskarta. Kamaninta sosai da kakarta Iya shiyasa take ji da ita.
"Kinyi shiru Rahiman Muhammad"
Sautin loudspeaker suka ji za'a bude taron da addu'a Rahima ta daure tace "to me kake so nace Muhammadun Rahima?"
Murmushinsa dariyar farinciki ya koma yana kallonta da adoration "kince komai....realy? Kin yarda Muhammadun Rahima ne ni? Daga ni fa babu kari"
Dariya tayi ta cikin mayafin tana gyada kai. Zuciyar Emzee ta cika da soyayyar kanwarsa da bai san suna da alaka ba ko kadan. Da sauri sauri suka karasa hall din za ta wuce bangaren mata ya bi bayanta da sauri yana maida numfashi tamkar wanda yayi tsere taji yace "Ina sonki Rahiman Muhammad"
Juyowa tayi suka hada ido kowa da kayataccen murmushi a saman fuskarsa sannan suka nemi wurin zama.
**********
Taro ya soma kankama bayan addu'o'i da mika godiya ga Allah mai gabatarwa Ibrahim Hadir ya gabatar da manyan baki na musamman. Ba kowa bane illa manyan aminai 'yan uwa ga Zayyan kowa da matarsa. Excellency baban Arifah, Major Daddy, Baba Hadir sai kuma Tante da mijinta mahaifin Yousuf. Wadannan mutane kowannensu ya taka muhimmiyar rawa a rayuwar iyalin Zayyan shiyasa idan suna ganin ya kyautata musu wurin ceton rayuwarsu ya kan ce babu kyautatawa mafi tsada da daraja sai wadda za kayi a bayan idon mutum idan ya mutu. Wannan kyautatawar kayi ta ne ba don ganin ido ba bare kasa ran a saka maka. A gefe guda ga duka 'yan uwan Zayyan mata uku da maza biyu domin Maikudi bazai taba iya zuwa ba duk da Zayyan ya bukaci hakan. To da wane ido zai kalli su Mairama, Daddy da har yau bai manta kalar bacin ran da ya gani a idanunsa ba, da uban gayya Zayyan wanda ya mare shi. Ya kure Zayyan iyakar kurewa kuma ya tabbatar abinda yayi musu bazai taba gogewa a zukatansu ba. Son zuciya da kwadayi ya mayar dashi mujiya a cikin ahalinsa. Yana ji yana gani sai dai yayi ta dari dari dasu domin tsanarsa da yake gani a idanunsu.
Captain Onomza shima yazo ga jama'ar Rugar Barkindo, na gidan Malamijo da abokan arziki. Sannan mutumin da Zayyan ya dauka da matukar mahimmanci a rayuwarsa wato Chibuzor da matarsa da 'yarsu su ma kayan jikinsu irin na wadanda su ka yi ankon fari da green din. Sai kuma Maman Dolapo da Christie ma sun zo kafin shigowar Emzee suka share hawayensu dasu Mama. Ga Alh Salisu da nasa iyalin abin sai son barka.
Ibrahim ne yake magana da turanci da hausa domin kowa ya fahimta ya sanar da cewa akwai gajeren wasa da abokan Emzee zasu gabatar mai taken A Soldier's Dream (Burin Soja).
Drama ce mai kayatarwa wadda ta janyo wurin yayi shiru aka zuba musu idanu daga kan stage. Sojoji ne rataye da bindiga da 'yan jakunkunansu sunyi shirin tafiya filin daga. Gefe guda matansu da iyayensu suna ta kuka da yara. Idan ka ga yadda suke gabatar da dramar da matukar ban tausayi. Sun rabu da iyali suna ta kuka sannan sunje yakin an kashe da yawansu. Nan ma wurin dawowarsu mata da yawa suka rinka suma duk wadda ta ga babu mijinta. Mutane kuwa sai share hawaye domin an shigar dasu cikin rayuwar da basu santa ba kuma a da babu wanda yake damuwa da sanin nata.
Da dramar ta kare Radhiya ma duk yadda ta ga abubuwa a Military Voice lokacin da suke dauka sai da tayi wani kukan. Bayan an gama tafa musu Ibrahim ya bukaci wadanda ake taro dominsu su hadu wuri daya.
Zayyana dauke da DK wanda kayansa harda hula babu bambanci da na Daada da Emzee anyi masa komai dan karami daidai da jikinsa suka je wurin Daada. Wani envelop da Ummi tayi wrapping mai dan tudu Zayyan ya daga hannun DK da yake jikin Zayyan ya dora masa a kirjinsa.
"This is for you my son"
Su Daddy suna kallo babu wanda yasan menene a ciki. Wani ya sake daukowa ya fi wancan girma da dan nauyi ya mikawa Zayyana.
"Kallabi tsakanin rawuna Zayyanatun Zayyan ga naki"
Ashe harda hawayen wahala tayi bata sani ba cikin fada tace "shegen yaro mai kama da ifiritu bude min"
Emzee a soja yake baka ganin wani abu wai shi sani ko sabo a tattare dashi sai murmushin mugunta "kinfi kowa sanin cewar ina da uba mijin kanwarki....ko ince mutumin da kike so?" Ya yi mata wani kallon gefe.
Jikin Salame ya bugu saboda tukin da ya yi amma abinda yafi daga mata hankali bai wuce maganar da yayi ba. A ina yaji? Mairama ce ta fada masa ko waye? Karfin hali tayi ta daure fuska.
"Rashin kunyar taka har ta kai haka Karami? Irin tarbiyar da Mairama take baku kenan ashe, kun tashi ba ku ganin girman kowa"
Juyowa Emzee yayi ya mata wani kallo mai firgitarwa kamaninsa sun sauya gabadaya...soja mazan fama.
"Kada ki kuma ambaton sunan Ummina domin tunda take bata taba nakasa dabba ba bare mutum"
"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun" Salame ta fada a tsorace jikinta yana tsuma baki na rawa "me...me kake nufi? Sharri za ka yi min kace ni na makanta ta?"
Sai da kansa ya sara a lokacin domin dama bugun cikinta yayi ya bata tsoro domin jin gaskiyar lamari kuma yaji abinda yake so kafin ma ya tambaya. Duk da yana zargin tabbas ita ce amma yanzu da ya tabbatar sai da abin ya girgiza shi matuka. Ba ya kaunar Salame ko na digon sakan saboda bata cancanci a sota ba. Umminsa tana makance tsayin shekaru Salame tana gidan miji tana ciki da haihuwa taci me kyau tasha me kyau lokacin gwamnatinta na ci a zuciyar Alh Indararo.
"Kuruciya tasa ban fahimci me kika yi ba shiyasa ban tona miki asiri ba tun lokacin da kika saka mata...." yace don ya kara tunzurata yana bude dash board.
Sabon gumi na yake tsattsafo mata jin sirrin boye da ko da kanta bata zancen a zuci yau Emzee ya bankado shi. Harda sanyi ta rinka ji yana ratsata ya cigaba da lalubensa kamar ba ta cikin motar.
Hakoranta sai sarkewa suke yi don tsoro tace "to yanzu kuma uban me kake lalube bayan ka gama yi min sharrin"
"Bindiga"
Idanunta kamar zasu fado karshen tsoro ta kai sannan ga uwa uba wani mahaukacin zawo da ya matsota saboda tsoro.
"An...an. fada. Maka idan...idan ka kasheni. Mairama zata yi murna ne?"
Bude pin din motar yayi "kin zata harbinki zanyi? Allah Ya kiyaye ba'ayi min wannan tarbiyar ba"
Budewa tayi da sauri ya leka da kansa ta inda ta tashi "uhmm nace ba....nagode da kika tabbatar min da zargina akan waye ya makanta min uwa"
Salame sai bude baki tayi tana masa kallon tsananin mamaki shi kuwa ya zura hannu ya janyo kofar ya rufe ta bangaren da take sannan ya kifa kai akan sitiyari yana kokarin mayarda hawayen bakincikin da suke neman zuwar masa. Dago kai yayi ya nemi wayarsa sai ya ga har lokacin tana tsaye. Da kallo daya ya karasa razana ta ta wuce ciki wurin da ake ta karbar baki za'a fara abinda ya tara jama'a.
Yau ranar farinciki ce dole ya saita kansa. Ibrahim ya kira bugu daya ya dauka.
"Bro turo min Rahima" yace da wata iron murya can kasa.
"Bangane ba. Ba tare kuke ba?" Zai sake magana ya hangota tare da Zayyana zasu zauna "kana ina ne na ganta"
Kwatanta masa inda yayi parking Emzee yayi Ibrahim yaje inda suke ya fadawa Zayyana ita kuma ta fada mata. Tana tashi bayan ta ajiye Khadi akan kujerarta ta hango Salame amma da ta ga hankalinta baya gareta sai ta wuce ta tafi.
Ya gama saka rigarsa kenan yana gyara zaman hular a kansa ta bullo. Shagala Emzee yayi da yadda Rahima take tafiya cikin nutsuwa. Yanayin da ya shiga mai wuyar fassara soyayyarta ta mamaye masa kowane lungu da sako na zuciyarsa. Duk kunya ta isheta saboda yadda ya kafeta da ido har ta karaso.
"Mu zauna a nan ko mu shiga ciki?" Yace yana fatan ta amince su zauna.
"Za'a nemeka ai"
"Okay muje" sun fara tafiya ya ga dacewar ya bata hakuri akan abinda yayar mahaifiyarsa tayi musu "Rahima kiyi hakuri akan abinda ya faru dazu. Na saka ki zaman jirana kuma bani na kawoki ba"
Ita da tasan mahaifiyarta ce tayi sai tayi saurin cewa "ni ya kamata na baka hakuri"
"Akan me? For being a good girl me jin maganarrr.....maganar wa dinki kika ji?" Ya zuba mata idanu.
Murmushi tayi kanta a kasa "Ya Emzee?"
"Nope" tsayuwa yayi ya hanata tafiya "Rahima wane matsayi kika bani?"
Kasa magana tayi tambayar tayi mata nauyi duk da amsarta tana jin tamkar ta amayo masa ita ne ko za ta sami saukin wannan soyayya da tayi mata mugun kamu.
Kamar yayi mata kuka saboda taki magana "gobe zan koma Kaduna da sassafe. Please Rahima ki fada min ni waye a gareki kafin na tafi....idan ba haka ba retire zanyi tun kafin na fara aikin na dawo ga filin yaki nan in your beautiful eyes muyi ta fafatawa."
Zuwa yanzu ko fuskarta baya iya gani ta shige cikin mayafin ta rufe kanta gabadaya sai murmushi kawai take yi. Da kyar ta iya cewa "ni wa dinka ce to?"
"My heart..." yace da sauri "ke fa?"
Babu wanda zai wuce ya gansu baiyi musu kallo na biyu ba. Kana ganinsu ka ga masoyan da suka mutu akan juna kuma suka dace sosai da juna. Emzee fari ne kamar yayarsa ga kyau ga jikin matashin soja. Rahima kuwa baka ce fatarta tafi kama da wankan tawarda don da kadan Zayyana ta fita haske. Kyakkyawa ce sosai tafi Halifa da sauran 'ya'yan Salame nesa ba kusa ba sai dai su nuna mata haske. Round shaped eyes dinta sunfi komai daukar hankali akan fuskarta. Kamaninta sosai da kakarta Iya shiyasa take ji da ita.
"Kinyi shiru Rahiman Muhammad"
Sautin loudspeaker suka ji za'a bude taron da addu'a Rahima ta daure tace "to me kake so nace Muhammadun Rahima?"
Murmushinsa dariyar farinciki ya koma yana kallonta da adoration "kince komai....realy? Kin yarda Muhammadun Rahima ne ni? Daga ni fa babu kari"
Dariya tayi ta cikin mayafin tana gyada kai. Zuciyar Emzee ta cika da soyayyar kanwarsa da bai san suna da alaka ba ko kadan. Da sauri sauri suka karasa hall din za ta wuce bangaren mata ya bi bayanta da sauri yana maida numfashi tamkar wanda yayi tsere taji yace "Ina sonki Rahiman Muhammad"
Juyowa tayi suka hada ido kowa da kayataccen murmushi a saman fuskarsa sannan suka nemi wurin zama.
**********
Taro ya soma kankama bayan addu'o'i da mika godiya ga Allah mai gabatarwa Ibrahim Hadir ya gabatar da manyan baki na musamman. Ba kowa bane illa manyan aminai 'yan uwa ga Zayyan kowa da matarsa. Excellency baban Arifah, Major Daddy, Baba Hadir sai kuma Tante da mijinta mahaifin Yousuf. Wadannan mutane kowannensu ya taka muhimmiyar rawa a rayuwar iyalin Zayyan shiyasa idan suna ganin ya kyautata musu wurin ceton rayuwarsu ya kan ce babu kyautatawa mafi tsada da daraja sai wadda za kayi a bayan idon mutum idan ya mutu. Wannan kyautatawar kayi ta ne ba don ganin ido ba bare kasa ran a saka maka. A gefe guda ga duka 'yan uwan Zayyan mata uku da maza biyu domin Maikudi bazai taba iya zuwa ba duk da Zayyan ya bukaci hakan. To da wane ido zai kalli su Mairama, Daddy da har yau bai manta kalar bacin ran da ya gani a idanunsa ba, da uban gayya Zayyan wanda ya mare shi. Ya kure Zayyan iyakar kurewa kuma ya tabbatar abinda yayi musu bazai taba gogewa a zukatansu ba. Son zuciya da kwadayi ya mayar dashi mujiya a cikin ahalinsa. Yana ji yana gani sai dai yayi ta dari dari dasu domin tsanarsa da yake gani a idanunsu.
Captain Onomza shima yazo ga jama'ar Rugar Barkindo, na gidan Malamijo da abokan arziki. Sannan mutumin da Zayyan ya dauka da matukar mahimmanci a rayuwarsa wato Chibuzor da matarsa da 'yarsu su ma kayan jikinsu irin na wadanda su ka yi ankon fari da green din. Sai kuma Maman Dolapo da Christie ma sun zo kafin shigowar Emzee suka share hawayensu dasu Mama. Ga Alh Salisu da nasa iyalin abin sai son barka.
Ibrahim ne yake magana da turanci da hausa domin kowa ya fahimta ya sanar da cewa akwai gajeren wasa da abokan Emzee zasu gabatar mai taken A Soldier's Dream (Burin Soja).
Drama ce mai kayatarwa wadda ta janyo wurin yayi shiru aka zuba musu idanu daga kan stage. Sojoji ne rataye da bindiga da 'yan jakunkunansu sunyi shirin tafiya filin daga. Gefe guda matansu da iyayensu suna ta kuka da yara. Idan ka ga yadda suke gabatar da dramar da matukar ban tausayi. Sun rabu da iyali suna ta kuka sannan sunje yakin an kashe da yawansu. Nan ma wurin dawowarsu mata da yawa suka rinka suma duk wadda ta ga babu mijinta. Mutane kuwa sai share hawaye domin an shigar dasu cikin rayuwar da basu santa ba kuma a da babu wanda yake damuwa da sanin nata.
Da dramar ta kare Radhiya ma duk yadda ta ga abubuwa a Military Voice lokacin da suke dauka sai da tayi wani kukan. Bayan an gama tafa musu Ibrahim ya bukaci wadanda ake taro dominsu su hadu wuri daya.
Zayyana dauke da DK wanda kayansa harda hula babu bambanci da na Daada da Emzee anyi masa komai dan karami daidai da jikinsa suka je wurin Daada. Wani envelop da Ummi tayi wrapping mai dan tudu Zayyan ya daga hannun DK da yake jikin Zayyan ya dora masa a kirjinsa.
"This is for you my son"
Su Daddy suna kallo babu wanda yasan menene a ciki. Wani ya sake daukowa ya fi wancan girma da dan nauyi ya mikawa Zayyana.
"Kallabi tsakanin rawuna Zayyanatun Zayyan ga naki"