Sashe 26
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Farfadowarsa kenan daga allurar anasiziya da aka yi masa kafin a shiga dashi theatre. Tsahon sati biyu da kwanaki da yayi a asibitin Katsina kafin likitan da zaiyi masa aikin kafar yazo daga asibitin koyarwa na Zaria yayi su ne a cikin halin rashin sanin inda yake. Irin kukan da Mami tayi na fili da na zuci bazai fadu ba. Major Mustapha soja yayanta kuma uban 'ya'yanta shine wasu cikin masu zuwa dubiya suke kirawa hauka. Dole ace yana hauka don idan har zaka zauna dashi na minti biyar ido biyu surutan da zaka ji yana yi kwatakwata babu ma'ana ga wanda baya tare dasu a ranar da abin nan ya faru a dajin Liberia. Labari ne na yaki, tashin hankali da zubar jini. Tsananin ciwon da kafarsa take yi shine musabbabin fitarsa daga hayyacinsa har yake wadannan surutai. An tabbatar musu da cewa zafin ciwo ne kawai.
Asibitin suna kokarin dressing din ciwon amma yadda tsutsa ke fita suna cin namansa daga ciki shi kadai yasan azabar da yake ciki. Dakin kansa wani irin wari yake yi don kannensu maza ke kwana dashi ma. An hana Mami kwana sai dai tazo ta wuni ta koma gida.
Kudi sosai suka kashe akan ciwon nasa. To yau dai Allah Yayi likita yazo an yanke kafa dan abinda aka bari iya rabin cinyarsa ne. Sauran naman duk ya zagwanye saboda infection.
Abinda yake fada ya tadawa Mami hankali. Cikin nutsuwa ta matsa kusa dashi tana tambayarsa me ya sami Zayyan din.
"Ni ne dai nayi ajalinsa. Ashe duk mutuncin da yaron nan yake nuna min a dalilina zai rasa ransa. Ya ceci rayuwata ya rasa tasa. Me yasa nima ban mutu ba?"
Mami ta shiga rudani aka sake kiran likita yace su kwantar da hankulansu allura bata gama sakinsa ba. Da kadan da kadan sai da suka kwashe wata uku cur a asibitin nan. Kafarsa ta hade wurin sai dungulmi amma ya gamu da wata sabuwar lalurar da basu ankara da ita da wuri ba wato septicemia. Infection ne na jini da yake samuwa daga infection a wani bangaren jiki sai kwayoyin cutar su gangara cikin jini.
Da zazzafan zazzabi abin ya fara sai kuma yawan jin sanyi. Da fari magunguna da alluran malaria aka bashi. Yayi sati ana wannan babu wani chanji sai ma gaba da abin ya kara. Bugun zuciyarsa sai ya kara gudu har ana gani dagowar kirjinsa, dama ga muguwar rama da ya hada. Da likitocin suka ga babu sauki akace typoid ce. Nan ma duk wasu allurai da magunguna sai da ya karar dasu.
Hankula sun kara tashi ne ranar da zuciyarsa ta nemi bugawa shine fa aka rinka gwaje gwaje baji ba gani. Jininsa har asibitocin koyarwa na Zaria, Kano da Ibadan an tura domin gano abinda yake damunsa. Rashin wadatar kayan aiki a asibitocin kasarmu ya janyo Major Mustapha ya kusa rasa rayuwarsa. Da kyar aka gano a asibitin Ibadan aka turo musu sakamakon. Sai a lokacin aka fara treatment bayan infection din yaci jininsa sosai har ya fara harin kayan cikinsa.
Da aka sallamo shi haka ya dawo gida kamar mutum mutumi. Yau da lafiya gobe babu. Ya rage surutai sai ma rashin son magana da kebewa daga mutane. Idan ya kalli kafarsa sai yaji ya tsani rayuwa gabadaya. Da bai rasata ba Zayyan bazai dawo daukarsa ba. Da sai su gudu tare su tsira tare.
Yayi shekara a kwance. An sayar da motarsa da filinsa na nan Katsina duk a siyan magunguna masu tsada domin samun lafiyarsa.
Wata rana Mami tayi masa zancen su Mairama sai kawai ya saka mata kuka. Taya shi tayi don gabadaya mijin nata yanzu tamkar bashi ba.
"Da wane ido zan kalleta Hassana? Ko kinsan cewa da don ta ni ne wallahi na gwammace na kare rayuwa a Liberia da na dawo gida na fuskanci matar Zayyan. Na zama silar da bomb ya tarwatsa mata miji shine abinda kike so kiji na fada mata idan ta tambayeni ta yaya mijinta ya rasa ransa?"
"Kayi hakuri Daddy ba manufata ba kenan. Kasan ya barta da ciki ga Radhiya"
Kai ya girgiza "baki san nauyin da zuciyata take ciki bane da kin kyaleni. I feel guilty and I hate myself and.... my life. Idan zaki je nayi miki izini"
Tasowa tayi ta rungume shi tana hawaye "nima me zance mata?"
"Ban sani ba..." yace da raunin zuciya yana kara kankameta.
Kwanaki kadan da yin wannan magana wata rana da daddare suna kwance ta tuna Fauziyya ta kwanta bata yi fitsari ba. A gidansu Major din aka basu wani bangare dakuna biyu masu fuskantar juna. Awwab a wurin samari yake kwana har an mayar dasu makaranta.
Ta je ta kai Fauziyya tayi fitsari ta dawo da sanda saboda kada ta tashe shi. Amma duk da haka sai da ya farka. Inuwarta ya gani ta tuna masa da lokacin da 'yan tawayen nan suka rinka fitowa ta baya da saman bishiyoyi suna harbinsu. Baiyi wata wata ba ya mirgina jikinsa ya damkota. A daidai wannan lokacin jinsa yake kamar a wancan lokacin. Kunnuwansa suna jiyo masa sautin harbi da hayaniya tartar. Wata muguwar shaka ya kaiwa Mami ya sakar mata karfi.
"Captain na kama daya kuzo ku daure shi mu tafi dashi base dinmu" yace da dan karfi.
Mami sai kokawa take tana son yi masa magana ta kasa saboda wuyanta da ya shake tana numfashi sama sama. A daidai kunnenta yace
"Who sent you?"
Wahala ta fara yawa Mami duhu duhu take gani. Da kyar ta samu ta juya ta saka duka karfinta ta galla masa cizo a kirji. Gashin kanta ya damko da karfi ta saki kara. Daga hannu yayi ya kwada mata mari ta sake yin wata karar. Zai kuma marinta haske ya mamaye dakin. Mahaifiyarsa ce ta shigo tare da kaninsa da suka ji ihun Mami. Tana zuwa itama hannu ta cire ta mare shi.
"Kasheta kake son yi ne Mustapha? Sakar mata gashi"
Tamkar wanda ya tashi daga bacci sai lokacin ya kula da hannunsa da inda hannunsa yake yayi saurin sakinta. A guje ta tashi ta fada jikin Innarsa tana kuka. Wuyanta Innar ta lura dashi saboda farar fata yayi jawur.
"Na shiga uku ni Fatima me zan gani? Ba dai shaketa kayi ba?"
Kansa yaji ya daure wai me yake yi a dakin nan shi da suke tare da su Zayyan a daji. Firgici da tsoro ya kama shi ya soma yunkurin sauka daga kan gadon. Innarsa ta dakatar dashi.
"Kada ka soma matsowa inda muke wallahi." Ta kalli kaninsa "rufe min shi da safe sai a fadawa Alh Baba kafin babanku ya dawo"
Washegari zama na musamman akayi akan abinda ya faru a daren. Mahaifiyar Mami ta shafawa idonta toka tace 'yarta ko dai ta koma gida ko kuma a raba musu daki bazata yarda a kasheta ba. Ko wace ma hakan zata yi shiyasa aka tattara Mami da yaranta ta kuma gidan iyayenta.
Major Mustapha kuma ya shiga wani sabon mawuyacin mataki a rayuwarsa. Iyaye duka sun hadu akan cewa gamo yayi a dajin nan aka shiga banka masa magungunan gargajiya, hayaki da rubutu. Kowa yaji labarin maganin aljanu cikinsu zai bada kudi domin a kawo su gwada. Idan ka ganshi dole ka koka in kasan waye Major Mustapha. Ya rame ya kare sai kashi da tashin hankali. Kuma abu kadan yake tayar masa da wannan abu ya fada cikin dogon tunani yana ganin kamar yanzu abin yake faruwa.
Awwab shine mai zama dashi sosai kafin watarana shima ya shigo daki ya nemi Daddyn nasu ya rasa. Ya zauna jiran ko yana bandaki amma shiru. Haka akayi ta neman Major hankalin kowa a tashe. Mami taci kuka ta more. Sai can kamar ance Awwab ya duka ya ganshi a karkashin gado yana ta rarraba idanu.
"Mami gashi nan"
"Shhhh zasu ganmu."
Mami ta dake ta duka itama "su waye zasu ganmu Daddy?"
" 'Yan tawayen mana"
Kasa magana tayi ta tashi ta koma dakin Innarsa tana kuka. Har yaushe zasu kare rayuwarsu a wannan yanayi? Dama haka ake auren sojan ko kuwa kaddararsu ce haka?
Sauki babu sai daga Allah. A wannan yanayin Gambonsu Mami da mijinta Harun da a wurin Alh Baba suka zo daga Germany inda yake aiki a gidan rediyo a matsayin mai labarai.
Sunyi bakincikin yadda rayuwa ta mayar da 'yan uwansu shine Harun ya shiga newarwa Major da Mami visar tafiya. A cewarsa zai kai dan uwansa asibiti ne tunda babu wani cigaba a gida. Iyayensu dai sun kyaleshi ne amma a iya tunaninsu asarar kudi zaiyi.
Abu na Allah sun tafi Germany a shekara ta uku bayan rasuwar Zayyan. A can ne bincike ya nuna Major yana fama da Post Traumatic Stress Disorder (PTSD). Lalura ce ta kwakwalwa da a lokacin ba'a waye da ita sosai a bangarenmu na Africa ba. PTSD tana samuwa ne ga mutanen da suka yi gamo da mummunan yanayi ko al'amari kuma tana tashi ne idan suka samu kansu a yanayin da zai iya tuna musu da wannan abu. Yawan mafarkin da yake yi da kuma ji ko ganin kamar yanzu abin yake faruwa duka alamominta ne.
Mami tambaya take ba haukacewa yayi ba aka ce mata ba hauka bane sai dai masu ita suna bukatar tsantsar kulawa daga makusantansu don idan abu yayi yawa wasu har kashe kansu suke yi.
A gidan Gambo suka zauna har zuwa lokacin da ya fara jin sauki. Mami ta jajirce sosai wurin kula dashi. Daga baya ta fara tunanin kada su zame musu nauyi tace Harun ya nema mata aiki. To aiki a wata kasar ba'a samunsa kai tsaye. Ta bukaci ko yaya tana son neman kudi kafin su koma saboda kusan karkaf sunyi. Komai nashi ya kare an fara shiga aljihun dangi.
Aikin nanny ya samar mata har yana tsoron fada mata sai ta basu mamaki wurin karbar aikin hannu bibbiyu. Gidan wasu 'yan kasa take zuwa daga bakwai na safe zuwa bakwai na yamma. Tayi su shara, wankin toilet da sauran ayyukan gida hade da raino.
Asibitin suna kokarin dressing din ciwon amma yadda tsutsa ke fita suna cin namansa daga ciki shi kadai yasan azabar da yake ciki. Dakin kansa wani irin wari yake yi don kannensu maza ke kwana dashi ma. An hana Mami kwana sai dai tazo ta wuni ta koma gida.
Kudi sosai suka kashe akan ciwon nasa. To yau dai Allah Yayi likita yazo an yanke kafa dan abinda aka bari iya rabin cinyarsa ne. Sauran naman duk ya zagwanye saboda infection.
Abinda yake fada ya tadawa Mami hankali. Cikin nutsuwa ta matsa kusa dashi tana tambayarsa me ya sami Zayyan din.
"Ni ne dai nayi ajalinsa. Ashe duk mutuncin da yaron nan yake nuna min a dalilina zai rasa ransa. Ya ceci rayuwata ya rasa tasa. Me yasa nima ban mutu ba?"
Mami ta shiga rudani aka sake kiran likita yace su kwantar da hankulansu allura bata gama sakinsa ba. Da kadan da kadan sai da suka kwashe wata uku cur a asibitin nan. Kafarsa ta hade wurin sai dungulmi amma ya gamu da wata sabuwar lalurar da basu ankara da ita da wuri ba wato septicemia. Infection ne na jini da yake samuwa daga infection a wani bangaren jiki sai kwayoyin cutar su gangara cikin jini.
Da zazzafan zazzabi abin ya fara sai kuma yawan jin sanyi. Da fari magunguna da alluran malaria aka bashi. Yayi sati ana wannan babu wani chanji sai ma gaba da abin ya kara. Bugun zuciyarsa sai ya kara gudu har ana gani dagowar kirjinsa, dama ga muguwar rama da ya hada. Da likitocin suka ga babu sauki akace typoid ce. Nan ma duk wasu allurai da magunguna sai da ya karar dasu.
Hankula sun kara tashi ne ranar da zuciyarsa ta nemi bugawa shine fa aka rinka gwaje gwaje baji ba gani. Jininsa har asibitocin koyarwa na Zaria, Kano da Ibadan an tura domin gano abinda yake damunsa. Rashin wadatar kayan aiki a asibitocin kasarmu ya janyo Major Mustapha ya kusa rasa rayuwarsa. Da kyar aka gano a asibitin Ibadan aka turo musu sakamakon. Sai a lokacin aka fara treatment bayan infection din yaci jininsa sosai har ya fara harin kayan cikinsa.
Da aka sallamo shi haka ya dawo gida kamar mutum mutumi. Yau da lafiya gobe babu. Ya rage surutai sai ma rashin son magana da kebewa daga mutane. Idan ya kalli kafarsa sai yaji ya tsani rayuwa gabadaya. Da bai rasata ba Zayyan bazai dawo daukarsa ba. Da sai su gudu tare su tsira tare.
Yayi shekara a kwance. An sayar da motarsa da filinsa na nan Katsina duk a siyan magunguna masu tsada domin samun lafiyarsa.
Wata rana Mami tayi masa zancen su Mairama sai kawai ya saka mata kuka. Taya shi tayi don gabadaya mijin nata yanzu tamkar bashi ba.
"Da wane ido zan kalleta Hassana? Ko kinsan cewa da don ta ni ne wallahi na gwammace na kare rayuwa a Liberia da na dawo gida na fuskanci matar Zayyan. Na zama silar da bomb ya tarwatsa mata miji shine abinda kike so kiji na fada mata idan ta tambayeni ta yaya mijinta ya rasa ransa?"
"Kayi hakuri Daddy ba manufata ba kenan. Kasan ya barta da ciki ga Radhiya"
Kai ya girgiza "baki san nauyin da zuciyata take ciki bane da kin kyaleni. I feel guilty and I hate myself and.... my life. Idan zaki je nayi miki izini"
Tasowa tayi ta rungume shi tana hawaye "nima me zance mata?"
"Ban sani ba..." yace da raunin zuciya yana kara kankameta.
Kwanaki kadan da yin wannan magana wata rana da daddare suna kwance ta tuna Fauziyya ta kwanta bata yi fitsari ba. A gidansu Major din aka basu wani bangare dakuna biyu masu fuskantar juna. Awwab a wurin samari yake kwana har an mayar dasu makaranta.
Ta je ta kai Fauziyya tayi fitsari ta dawo da sanda saboda kada ta tashe shi. Amma duk da haka sai da ya farka. Inuwarta ya gani ta tuna masa da lokacin da 'yan tawayen nan suka rinka fitowa ta baya da saman bishiyoyi suna harbinsu. Baiyi wata wata ba ya mirgina jikinsa ya damkota. A daidai wannan lokacin jinsa yake kamar a wancan lokacin. Kunnuwansa suna jiyo masa sautin harbi da hayaniya tartar. Wata muguwar shaka ya kaiwa Mami ya sakar mata karfi.
"Captain na kama daya kuzo ku daure shi mu tafi dashi base dinmu" yace da dan karfi.
Mami sai kokawa take tana son yi masa magana ta kasa saboda wuyanta da ya shake tana numfashi sama sama. A daidai kunnenta yace
"Who sent you?"
Wahala ta fara yawa Mami duhu duhu take gani. Da kyar ta samu ta juya ta saka duka karfinta ta galla masa cizo a kirji. Gashin kanta ya damko da karfi ta saki kara. Daga hannu yayi ya kwada mata mari ta sake yin wata karar. Zai kuma marinta haske ya mamaye dakin. Mahaifiyarsa ce ta shigo tare da kaninsa da suka ji ihun Mami. Tana zuwa itama hannu ta cire ta mare shi.
"Kasheta kake son yi ne Mustapha? Sakar mata gashi"
Tamkar wanda ya tashi daga bacci sai lokacin ya kula da hannunsa da inda hannunsa yake yayi saurin sakinta. A guje ta tashi ta fada jikin Innarsa tana kuka. Wuyanta Innar ta lura dashi saboda farar fata yayi jawur.
"Na shiga uku ni Fatima me zan gani? Ba dai shaketa kayi ba?"
Kansa yaji ya daure wai me yake yi a dakin nan shi da suke tare da su Zayyan a daji. Firgici da tsoro ya kama shi ya soma yunkurin sauka daga kan gadon. Innarsa ta dakatar dashi.
"Kada ka soma matsowa inda muke wallahi." Ta kalli kaninsa "rufe min shi da safe sai a fadawa Alh Baba kafin babanku ya dawo"
Washegari zama na musamman akayi akan abinda ya faru a daren. Mahaifiyar Mami ta shafawa idonta toka tace 'yarta ko dai ta koma gida ko kuma a raba musu daki bazata yarda a kasheta ba. Ko wace ma hakan zata yi shiyasa aka tattara Mami da yaranta ta kuma gidan iyayenta.
Major Mustapha kuma ya shiga wani sabon mawuyacin mataki a rayuwarsa. Iyaye duka sun hadu akan cewa gamo yayi a dajin nan aka shiga banka masa magungunan gargajiya, hayaki da rubutu. Kowa yaji labarin maganin aljanu cikinsu zai bada kudi domin a kawo su gwada. Idan ka ganshi dole ka koka in kasan waye Major Mustapha. Ya rame ya kare sai kashi da tashin hankali. Kuma abu kadan yake tayar masa da wannan abu ya fada cikin dogon tunani yana ganin kamar yanzu abin yake faruwa.
Awwab shine mai zama dashi sosai kafin watarana shima ya shigo daki ya nemi Daddyn nasu ya rasa. Ya zauna jiran ko yana bandaki amma shiru. Haka akayi ta neman Major hankalin kowa a tashe. Mami taci kuka ta more. Sai can kamar ance Awwab ya duka ya ganshi a karkashin gado yana ta rarraba idanu.
"Mami gashi nan"
"Shhhh zasu ganmu."
Mami ta dake ta duka itama "su waye zasu ganmu Daddy?"
" 'Yan tawayen mana"
Kasa magana tayi ta tashi ta koma dakin Innarsa tana kuka. Har yaushe zasu kare rayuwarsu a wannan yanayi? Dama haka ake auren sojan ko kuwa kaddararsu ce haka?
Sauki babu sai daga Allah. A wannan yanayin Gambonsu Mami da mijinta Harun da a wurin Alh Baba suka zo daga Germany inda yake aiki a gidan rediyo a matsayin mai labarai.
Sunyi bakincikin yadda rayuwa ta mayar da 'yan uwansu shine Harun ya shiga newarwa Major da Mami visar tafiya. A cewarsa zai kai dan uwansa asibiti ne tunda babu wani cigaba a gida. Iyayensu dai sun kyaleshi ne amma a iya tunaninsu asarar kudi zaiyi.
Abu na Allah sun tafi Germany a shekara ta uku bayan rasuwar Zayyan. A can ne bincike ya nuna Major yana fama da Post Traumatic Stress Disorder (PTSD). Lalura ce ta kwakwalwa da a lokacin ba'a waye da ita sosai a bangarenmu na Africa ba. PTSD tana samuwa ne ga mutanen da suka yi gamo da mummunan yanayi ko al'amari kuma tana tashi ne idan suka samu kansu a yanayin da zai iya tuna musu da wannan abu. Yawan mafarkin da yake yi da kuma ji ko ganin kamar yanzu abin yake faruwa duka alamominta ne.
Mami tambaya take ba haukacewa yayi ba aka ce mata ba hauka bane sai dai masu ita suna bukatar tsantsar kulawa daga makusantansu don idan abu yayi yawa wasu har kashe kansu suke yi.
A gidan Gambo suka zauna har zuwa lokacin da ya fara jin sauki. Mami ta jajirce sosai wurin kula dashi. Daga baya ta fara tunanin kada su zame musu nauyi tace Harun ya nema mata aiki. To aiki a wata kasar ba'a samunsa kai tsaye. Ta bukaci ko yaya tana son neman kudi kafin su koma saboda kusan karkaf sunyi. Komai nashi ya kare an fara shiga aljihun dangi.
Aikin nanny ya samar mata har yana tsoron fada mata sai ta basu mamaki wurin karbar aikin hannu bibbiyu. Gidan wasu 'yan kasa take zuwa daga bakwai na safe zuwa bakwai na yamma. Tayi su shara, wankin toilet da sauran ayyukan gida hade da raino.