Sashe 48
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani irin abu ne ya fizgi zuciyarta zuwa gareshi a daidai lokacin taji farinciki ya saukar mata irin wanda bata taba ji ba. A nasa bangaren sai da maganar ta fito ya fahimci nauyinta. Maganar zuci ne ta fito fili. Sai dai kuma shi ya sani cewa zuciyarsa bata raya masa karya ba haka nan bakinsa bai fadi karya ba. Haduwar kwana daya jinta yake kamar basu taba rabuwa ba. Zuciyarsa ta ginu da son wannan yarinyar tun tana cikin mahaifiyarta. Tsayin shekaru bai sa ya manta da ita ba. Ya cigaba da rainonta a zuciyarsa har zuwa haduwarsu ta jiya a inda yadda ta koma ya sake kayatar da ruhinsa zuwa gareta. Da kwalkwalin kan, shirme, shiririta da fada duk yaji ya dauka yana son abarsa a haka.
Dena kallonsa tayi don duk abinta bata da rashin kunyar da zata iya jurewa kallon da yake yi mata.
"Ehemmmm ga ruwa ga sabulu a ina zan ajiye?"
Aikin Emzee ne da tun kafin su karaso ya hangosu suna magana. Allah Yasa Ibrahim da Zayyana sunyi wajen wata tinkiya da take haihuwa ya taho wurinsu shi kadai da ledar purewater da sabulu.
Kumatun Radhiya har wani ja yayi don tsabar kunya ta tashi da saurinta zata gudu.
"Da fuskar taki mai warin maza zaki shiga cikin mutane? Dawo ki wanke"
Emzee bai yi wata wata ba ya arce daga wurin. Ya kamata su Ummi su farga da wuri kafin a laluba a nemesu a rasa.
Sabulun ya bata ya farke ledar purewater din ya dauko daya "fara wanke wannan hannun"
Durkusawa yayi a gabanta tana cuda hannuwan yana zuba mata ruwa har ta gama wankewa.
"Saura fuska" yace mata. Sabulun ta sake sakawa ta dage hijab din ta soma cuda fuskarta ya duku gab da ita "wai nan kunya na baki ne kika kasa magana? Kowa yasan Alheran ta Awwab ce baki da wurin zama sai gidansa"
Kirjinta ne ya soma dukan uku uku ta kasa karasa wanke fuskar ya kuma cewa "cire hannunki in wanke miki"
"Me din?" Tace tare da bude idanun ta da sauri tana matsawa kada yaje ya taba ta. Ai kuwa kumfar sabulun ta shige duka idanun biyu ta soma ihu tana tsalle sai da su Fauziyya suka taho garesu da sauri.
"Kinji dadi kin tara min mutane"
"Ka dena min mita ka hure min idona...wayyo yaji"
Su Fauziyya sun kusa karasowa kuma baya son kowa a tare dasu yanzun da yake shirin daukan duka makaman yakinsa ya nemi daidaitawa da kanwarsa.
"To cire hannun mana"
"Naki wani ne zai shiga"
A daidai nan Fauziyya ta fara zuwa gabanta ya mika mata wani ruwan ta zuba mata ta wanke fuskar. Da kyar ta bari ta hure mata idanun sunyi jazur dasu kuwa.
Awwab da yake jin hankalinsa ya tashi yace mata ya idon. Harara ta maka masa kamar ba shine ya janyo mata ba yana wasu maganganu da suke juya mata tunani.
Ana ta yi mata sannu tace su zo su tafi gida an kusa kiran sallah.
"Mal Da'u yace mu tsaya tinkiyar can da ta haihu yanzu ta kasa" Emzee ya sanar da ita.
Idanun da suka gama yin ja da kumburi ta zaro "ta kasa me?"
"Ta haihu ya kasa cire mahaifar sai shure shure take yi. Yankata zaiyi kawai mu tafi da ita gida idan mahaifar bata fito ba"
"Gida? Da wa? So kake Malamijo yasa ayi muku farfesu na kuci da burodi da safe?"
Ibrahim da Fauziyya suna dariya ta fada musu Malamijo yace ko kazarsa ce wani abu ya sameta ita zai kama.
"Hamma kai ya bawa amana kace ka karba" Ibrahim ya tuna masa.
"Ku muje na ajiyeku kawai na nemi wurin kwana a waje da safe zan dawo daukarku. Naga alama kasawar ma zata yi"
Hankalinta dama a tashe yake ta kyabe fuska yadda Zayyana take yi "bakinka ya sari danyen...."
Da sauri ya dakatar da ita kafin ta karasa fadin kazantar "ahhhhh don Allah kada ki karasa. Bazai sara ba in sha Allah"
Ya kama kansa kuwa ta sami kofar ramawa tayi shu'umar dariyar da sai ta tashi tsokana take yinta "danyen mangwaro fa zan ce ka hanani. Ka ga bishiyarsa can da nake hawa na tsinko mu rinka dangwala da siga"
Shima harararta yayi na daukar hakkinsa da tayi sannan yace "kwadayi, meye abin dadi a danyen mangwaro da sugar?"
"Kai dai kawai ka tsorata kayi zaton danyen ka...."
Wannan karon shine fuskarsa kamar zaiyi kuka baya son jin kazantar da ta dage sai ta fada "habaaa mana Alheran!"
Sai da ta kalli su Fauziyya tace "yanzu danyen kashu din ma ban isa in fada ba? Shima akwai bishiyarsa daga bayan can"
Hatta Emzee sai da yayi dariya saboda yadda fuskar Awwab tayi.
"Tsokanata kuke yi ko? Nasan me zanyi muku" yace yayi gaba Ghazalatu tayi saurin tarar dashi.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Mota suka nufa cikin sa'a Mal Da'u ya sanar dasu cewa ya fitar da mahaifar tinkiyar ta tashi. Radhiya sai murna kamar wata mutum. Kafin ta bar gidan ta kudiri niyar sai anci nama amma bazata so yau da babu hannunta a ciki ba Malamijo ya kare mata tanadi a bainar jama'a. Kowa wurin zamansa na dazu ya zauna jiki yayi ligib bare ma Ghazalatu da ta hado da tafiya daga Katsina. Suna isa gida sallar magariba suka yi.
Abin farinciki wurin Radhiya ashe bayan fitarsu Nene Marka ta iso. Danne tsohuwar tayi cikin murnar ganinta. Yau tsakar gidan ta san anyi baki kusan kowa anan ya zauna suna shan iskar Allah suna hirarrakinsu. Ana isha Ghazalatu ko abincin da ake yi mata tayi bata iya kallo ba tayi bacci ita kadai a dakin Zahra ma taji sauki ta fito wurin 'yan uwanta.
"Nene muje in nuna miki wani abu" Radhiya tace cikin rada. Dakin da zasu kwana ta ja ta. Ganin Ghazalatu bacci take yi ta cire dankwalin ta nuna mata kan ta "kinga abinda Innawuro tayi min" tace kamar zatayi kuka.
"Me zan gani ni Marka, aski akan budurwa saboda Allah"
Caraf a kunnen Ghazalatu. Da dabara ta juyo idonta ya sauka akan Radhiya dariya ta kusa kwace mata. Ashe ma babu wani dalili da zai sa ta dami kanta akan wannan namijin. Ji take kamar ta jawo gobe ta ganta a Katsina. Yau din taki karewa tunda tazo yarinyar take like da Awwab. Bata so ta nuna masa zahirin yadda take kin mutanen nan saboda yanzu dai a cikinsu take a cikin gidansu ma. Zata jira ko ma meye sai sun koma inda tafi wayo. Da wayo da dabara sai ta kawo karshen wannan alakar tun kafin rayuka su fara baci. Tana ji Radhiya tana yiwa Nene bayanin makeron da tayi da kwarkwata da suka janyo askin.
"Da kansa zai gudu makeron nan kinji 'Yar soja. Gobe da kaina zan shiga kasuwa akwai wani magani mai kyau idan nayi sa'ar haduwa da matar kanki har sai yafi na da in sha Allahu"
"Yauwa Nene" ta rungumeta tana murna.
Tuwo taje suka ci da su Zayyana. A dakin da mazan suke ma Emzee ya kai musu nasu ba kyama ko nuna gayu Awwab yaci nasa. Jakar kayansa ya duba bayan ya gama babu toothpaste ya manto shi a gidan Mama Zainab. Tun a hanya ya tuna bai damu ba tunda da niyar komawa gida suka taho. Bazai iya bacci baiyi brush ba. Ya ma tabbatar ko Emzee ya tambaya za'a bashi amma ransa yafi raya masa ya fita, fitar ma da Alheran bai gaji da ganinta ba.
"Emzee wane irin toothpaste gareku na manto nawa a Kano"
"Close up ne"
Da murna sabanin rashin jindadi da ya kamata ya nuna yace "kash bana iya amfani dashi, akwai inda zan iya siyowa nan kusa?"
"Kawo na siyo maka yanzun nan, da wane iri kake amfani?"
Shiru Awwab yayi zancen gaskiya bashi da wani zabi indai yana da kyau yana saya. Da dai sabulun wanka ne to baya tsallake pears masu mabambantan kamshi da sinadaren gyaran fata.
"Colgate nake so, amma zani da kaina kwatanta min"
Emzee da wayo ya gano Hamman nasu. Kallonsu yake daga shi har Radhiya ya ga ina za'a dire wannan abu.
"Ko in kira Adda ta raka ka ta fini sanin wurare. Idan ba'a samu a wani wuri ba baza'a rasa a wani ba"
Ido ya kafe Emzee dashi yana tunanin ko dai yaron ya fahimci yadda ya damu da ita ne. Ba ya son bawa kansa kunya a gaban yara ba. To amma meye a ciki don ya damu da ita ba kanwarsa bace? Yana can yana musu da zuciyarsa Emzee ya fice ya tafi nemanta. Tana dakin da su Mami zasu kwana sun je ita da Zayyana suna damunsa da hira. Fauziyya da Zahra suna nasu dakin kowacce tana waya.
"Adda kizo inji Hamma"
"Tayi masa me a daren nan tara saura?" Cewar Mami .
"Nima ban sani ba"
Mairama addu'a take Allah Ya daidaita kansu kada a sami matsala. Zama da Radhiya idan babu soyayya fa to akwai daru.
"Kai Hajiya yanzu bashi da ikon kiran kanwarsa?" Hajjo tayi maganar tana murmushi irin na ta fara gano manufar yaron.
"Radhiya tashi kije"
Sai dai tun suna magana Radhiya tayi gaba abinta. Nemanta suka yi suka rasa suka kwashe da dariya gabadaya.
Ta riga tayi wanka bayan magariba da suka rinka layi ita dasu Zahra kowa jiki yayi datti. Wata riga ce cotton mara nauyi take bacci da ita sai zani da ta daura da hijabi a kai. Shima Awwab can dakin da suke a bangaren samarin akwai bandaki wanda Emzee ya wanke musu shi tas suka yi wanka.
Lokacin da Awwab ya juya bai ga Emzee ba tunanin ina ya tafi ya fara yi sai gashi ya dawo yace Radhiya tana kofar gida inda ya turata yace ta jira shi. Yana fita shi da Ibrahim suka kwashe da dariya.
"Zeezee malamin soyayya. Nima na fara ganosu fa" Ibrahim yace yana mika masa hannu suka tafa.
"Idan ka sami ta ka kuma ka rasa yadda zakayi ka fada mata ka nemeni ka ga aiki da cikawa"
Daure fuska Ibrahim yayi da wasa "an fada maka na shirya ganganci ne. Idan na samu ma sai ranar kai amarya zan tura ka daukota"
"Dalili"
Dena kallonsa tayi don duk abinta bata da rashin kunyar da zata iya jurewa kallon da yake yi mata.
"Ehemmmm ga ruwa ga sabulu a ina zan ajiye?"
Aikin Emzee ne da tun kafin su karaso ya hangosu suna magana. Allah Yasa Ibrahim da Zayyana sunyi wajen wata tinkiya da take haihuwa ya taho wurinsu shi kadai da ledar purewater da sabulu.
Kumatun Radhiya har wani ja yayi don tsabar kunya ta tashi da saurinta zata gudu.
"Da fuskar taki mai warin maza zaki shiga cikin mutane? Dawo ki wanke"
Emzee bai yi wata wata ba ya arce daga wurin. Ya kamata su Ummi su farga da wuri kafin a laluba a nemesu a rasa.
Sabulun ya bata ya farke ledar purewater din ya dauko daya "fara wanke wannan hannun"
Durkusawa yayi a gabanta tana cuda hannuwan yana zuba mata ruwa har ta gama wankewa.
"Saura fuska" yace mata. Sabulun ta sake sakawa ta dage hijab din ta soma cuda fuskarta ya duku gab da ita "wai nan kunya na baki ne kika kasa magana? Kowa yasan Alheran ta Awwab ce baki da wurin zama sai gidansa"
Kirjinta ne ya soma dukan uku uku ta kasa karasa wanke fuskar ya kuma cewa "cire hannunki in wanke miki"
"Me din?" Tace tare da bude idanun ta da sauri tana matsawa kada yaje ya taba ta. Ai kuwa kumfar sabulun ta shige duka idanun biyu ta soma ihu tana tsalle sai da su Fauziyya suka taho garesu da sauri.
"Kinji dadi kin tara min mutane"
"Ka dena min mita ka hure min idona...wayyo yaji"
Su Fauziyya sun kusa karasowa kuma baya son kowa a tare dasu yanzun da yake shirin daukan duka makaman yakinsa ya nemi daidaitawa da kanwarsa.
"To cire hannun mana"
"Naki wani ne zai shiga"
A daidai nan Fauziyya ta fara zuwa gabanta ya mika mata wani ruwan ta zuba mata ta wanke fuskar. Da kyar ta bari ta hure mata idanun sunyi jazur dasu kuwa.
Awwab da yake jin hankalinsa ya tashi yace mata ya idon. Harara ta maka masa kamar ba shine ya janyo mata ba yana wasu maganganu da suke juya mata tunani.
Ana ta yi mata sannu tace su zo su tafi gida an kusa kiran sallah.
"Mal Da'u yace mu tsaya tinkiyar can da ta haihu yanzu ta kasa" Emzee ya sanar da ita.
Idanun da suka gama yin ja da kumburi ta zaro "ta kasa me?"
"Ta haihu ya kasa cire mahaifar sai shure shure take yi. Yankata zaiyi kawai mu tafi da ita gida idan mahaifar bata fito ba"
"Gida? Da wa? So kake Malamijo yasa ayi muku farfesu na kuci da burodi da safe?"
Ibrahim da Fauziyya suna dariya ta fada musu Malamijo yace ko kazarsa ce wani abu ya sameta ita zai kama.
"Hamma kai ya bawa amana kace ka karba" Ibrahim ya tuna masa.
"Ku muje na ajiyeku kawai na nemi wurin kwana a waje da safe zan dawo daukarku. Naga alama kasawar ma zata yi"
Hankalinta dama a tashe yake ta kyabe fuska yadda Zayyana take yi "bakinka ya sari danyen...."
Da sauri ya dakatar da ita kafin ta karasa fadin kazantar "ahhhhh don Allah kada ki karasa. Bazai sara ba in sha Allah"
Ya kama kansa kuwa ta sami kofar ramawa tayi shu'umar dariyar da sai ta tashi tsokana take yinta "danyen mangwaro fa zan ce ka hanani. Ka ga bishiyarsa can da nake hawa na tsinko mu rinka dangwala da siga"
Shima harararta yayi na daukar hakkinsa da tayi sannan yace "kwadayi, meye abin dadi a danyen mangwaro da sugar?"
"Kai dai kawai ka tsorata kayi zaton danyen ka...."
Wannan karon shine fuskarsa kamar zaiyi kuka baya son jin kazantar da ta dage sai ta fada "habaaa mana Alheran!"
Sai da ta kalli su Fauziyya tace "yanzu danyen kashu din ma ban isa in fada ba? Shima akwai bishiyarsa daga bayan can"
Hatta Emzee sai da yayi dariya saboda yadda fuskar Awwab tayi.
"Tsokanata kuke yi ko? Nasan me zanyi muku" yace yayi gaba Ghazalatu tayi saurin tarar dashi.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Mota suka nufa cikin sa'a Mal Da'u ya sanar dasu cewa ya fitar da mahaifar tinkiyar ta tashi. Radhiya sai murna kamar wata mutum. Kafin ta bar gidan ta kudiri niyar sai anci nama amma bazata so yau da babu hannunta a ciki ba Malamijo ya kare mata tanadi a bainar jama'a. Kowa wurin zamansa na dazu ya zauna jiki yayi ligib bare ma Ghazalatu da ta hado da tafiya daga Katsina. Suna isa gida sallar magariba suka yi.
Abin farinciki wurin Radhiya ashe bayan fitarsu Nene Marka ta iso. Danne tsohuwar tayi cikin murnar ganinta. Yau tsakar gidan ta san anyi baki kusan kowa anan ya zauna suna shan iskar Allah suna hirarrakinsu. Ana isha Ghazalatu ko abincin da ake yi mata tayi bata iya kallo ba tayi bacci ita kadai a dakin Zahra ma taji sauki ta fito wurin 'yan uwanta.
"Nene muje in nuna miki wani abu" Radhiya tace cikin rada. Dakin da zasu kwana ta ja ta. Ganin Ghazalatu bacci take yi ta cire dankwalin ta nuna mata kan ta "kinga abinda Innawuro tayi min" tace kamar zatayi kuka.
"Me zan gani ni Marka, aski akan budurwa saboda Allah"
Caraf a kunnen Ghazalatu. Da dabara ta juyo idonta ya sauka akan Radhiya dariya ta kusa kwace mata. Ashe ma babu wani dalili da zai sa ta dami kanta akan wannan namijin. Ji take kamar ta jawo gobe ta ganta a Katsina. Yau din taki karewa tunda tazo yarinyar take like da Awwab. Bata so ta nuna masa zahirin yadda take kin mutanen nan saboda yanzu dai a cikinsu take a cikin gidansu ma. Zata jira ko ma meye sai sun koma inda tafi wayo. Da wayo da dabara sai ta kawo karshen wannan alakar tun kafin rayuka su fara baci. Tana ji Radhiya tana yiwa Nene bayanin makeron da tayi da kwarkwata da suka janyo askin.
"Da kansa zai gudu makeron nan kinji 'Yar soja. Gobe da kaina zan shiga kasuwa akwai wani magani mai kyau idan nayi sa'ar haduwa da matar kanki har sai yafi na da in sha Allahu"
"Yauwa Nene" ta rungumeta tana murna.
Tuwo taje suka ci da su Zayyana. A dakin da mazan suke ma Emzee ya kai musu nasu ba kyama ko nuna gayu Awwab yaci nasa. Jakar kayansa ya duba bayan ya gama babu toothpaste ya manto shi a gidan Mama Zainab. Tun a hanya ya tuna bai damu ba tunda da niyar komawa gida suka taho. Bazai iya bacci baiyi brush ba. Ya ma tabbatar ko Emzee ya tambaya za'a bashi amma ransa yafi raya masa ya fita, fitar ma da Alheran bai gaji da ganinta ba.
"Emzee wane irin toothpaste gareku na manto nawa a Kano"
"Close up ne"
Da murna sabanin rashin jindadi da ya kamata ya nuna yace "kash bana iya amfani dashi, akwai inda zan iya siyowa nan kusa?"
"Kawo na siyo maka yanzun nan, da wane iri kake amfani?"
Shiru Awwab yayi zancen gaskiya bashi da wani zabi indai yana da kyau yana saya. Da dai sabulun wanka ne to baya tsallake pears masu mabambantan kamshi da sinadaren gyaran fata.
"Colgate nake so, amma zani da kaina kwatanta min"
Emzee da wayo ya gano Hamman nasu. Kallonsu yake daga shi har Radhiya ya ga ina za'a dire wannan abu.
"Ko in kira Adda ta raka ka ta fini sanin wurare. Idan ba'a samu a wani wuri ba baza'a rasa a wani ba"
Ido ya kafe Emzee dashi yana tunanin ko dai yaron ya fahimci yadda ya damu da ita ne. Ba ya son bawa kansa kunya a gaban yara ba. To amma meye a ciki don ya damu da ita ba kanwarsa bace? Yana can yana musu da zuciyarsa Emzee ya fice ya tafi nemanta. Tana dakin da su Mami zasu kwana sun je ita da Zayyana suna damunsa da hira. Fauziyya da Zahra suna nasu dakin kowacce tana waya.
"Adda kizo inji Hamma"
"Tayi masa me a daren nan tara saura?" Cewar Mami .
"Nima ban sani ba"
Mairama addu'a take Allah Ya daidaita kansu kada a sami matsala. Zama da Radhiya idan babu soyayya fa to akwai daru.
"Kai Hajiya yanzu bashi da ikon kiran kanwarsa?" Hajjo tayi maganar tana murmushi irin na ta fara gano manufar yaron.
"Radhiya tashi kije"
Sai dai tun suna magana Radhiya tayi gaba abinta. Nemanta suka yi suka rasa suka kwashe da dariya gabadaya.
Ta riga tayi wanka bayan magariba da suka rinka layi ita dasu Zahra kowa jiki yayi datti. Wata riga ce cotton mara nauyi take bacci da ita sai zani da ta daura da hijabi a kai. Shima Awwab can dakin da suke a bangaren samarin akwai bandaki wanda Emzee ya wanke musu shi tas suka yi wanka.
Lokacin da Awwab ya juya bai ga Emzee ba tunanin ina ya tafi ya fara yi sai gashi ya dawo yace Radhiya tana kofar gida inda ya turata yace ta jira shi. Yana fita shi da Ibrahim suka kwashe da dariya.
"Zeezee malamin soyayya. Nima na fara ganosu fa" Ibrahim yace yana mika masa hannu suka tafa.
"Idan ka sami ta ka kuma ka rasa yadda zakayi ka fada mata ka nemeni ka ga aiki da cikawa"
Daure fuska Ibrahim yayi da wasa "an fada maka na shirya ganganci ne. Idan na samu ma sai ranar kai amarya zan tura ka daukota"
"Dalili"