← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 157

Sashe 40

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Emzee tashi yayi ya sulale daga falon saboda tsabar kunya. Radhiya halinta sai ita. Yace ta basar kamar ba'ayi ba shine zata nuna bata ganshi ba gabadaya. Ji yayi kamar ya saka kuka da ma bai bata wannan shawarar ba.

"Baki ma ganni ba sai yanzu?" Yace yana kallon fuskarta. Dimple dinnan da yake saka yatsansa a ciki idan tana dariya yake kallo yana tuna masa rayuwar da.

Dakewa tayi abinta "ina na ganka na fito ina ta hira da 'yan uwa, yaya hanya? Ka ga Ummi?"

"Baki ganni ba da kika tashi daga bacci dazun nan?"

Radhiya an koyi basarwa da gaske ta wani langabe kai "yaushe? Ka dade da zuwa ne?"

Wai raina masa wayo zata yi ne? Kowa kallonsu yake yi ana dariya kasa-kasa. Hadir kansa murmushinsa ya kusa zama dariya da ya gane so take ta nuna bata ganshi ba. 

Awwab da bai fahimta ba dama shima anyi masa tambarin wauta idan abin dan farin nasa ya tashi yace "dazu fa kin farka har muka hada ido."

Tsuke baki ta soma yi. Ya kamata idan ta basar sau daya kawai a wuce wurin amma sai neman jan zance yake yi.

"Ni din? Bacci fa nayi a kan kujerar nan sai farkawa nayi na ganni a daki su Adda Zahra sun rikeni sun kaini saboda nauyin baccina, ban san lokacin da ka shigo ba"

Zahra ta soma kifta masa ido akan ya bar zancen haka shi kuma ya dage sai ya ga abinda ya turewa buzu nadi.

"Lokacin da abin kanki ya zame haka " ya kwatanta da dan jan dankwalin Fauziyya " har na ga kan...."

Ihu ta saka ta tashi da sauri tana jin kamar taje ta toshe masa baki kada ya karasa fadin ya ga kanta. Kamar zata yi kuka take kallonsa "idan nace ban ganka ba sai kawai ka yarda haka ake yi ko Em..." shiru tayi ta shiga waige da ta ga baya wurin "ina Emzee?" Tayi tambayar tana kallon Ibrahim da dariya tasa ko magana ya kasa.

"Ya fice"

"Ku ga min shegen yaro, shi yace idan na basar kamar ba'ayi ba komai zai  wuce."

Gabadaya falon ya sake kaurewa da dariya. Zainab ta tashi ta kama kujerar Hadir "bari naje na bawa babanku magani, Fauziyya ku kawowa Awwab abinci ko ruwa bai sha ba tunda ya shigo kun saka min 'ya a gaba"

Gani tayi ya dace su baiwa yaran wuri don ba ta biye musu ana tunzura Radhiya ba. So take Awwab ya so kanwar tasa da wuri, gara su fara sabawa da juna. Taimakawa Hadir tayi ya kwanta ta dauko takardun asibitin ta koma kusa dashi tana yi masa bayanin kowanne don neman shawararsa. Da ido da yanayin chanjin fuska take fahimtar abubuwa da dama da yake nufi idan tayi masa tambaya.

Sakale tayi tana kallon Awwab yana murmushi "ban san haka kike so ba, to koma ki sake fitowa. I promise zan tayaki basarwa"

Ita ma sai da abin ya bata dariya ta koma ta zauna tana jiran fitowar Emzee ko ma ina yaje ya buya. Dama idan ba ganganci ba me zaisa ta karbi shawararsa. Wautar kanta take gani na biye masa.

 Yana jiyo me suke yi a inda ya tsaya ya girgiza kai. Bawa Radhiya shawara wataran kamar zuba gari ne a rariya. Kana fada yana zuba. Ibrahim da Zayyana suka tashi suka bi bayan shi zuwa waje. Ibrahim na cewa ta dena binsa ta murguda masa baki tace ita wurin Emzee zata je ba shi take bi ba.

Ya rage su hudu a falon Awwab ya watsawa su Zahra idanunsa "bazaku bani abincin bane?"

Da sauri Radhiya ta tashi don yau dai taji kunya fiye da yadda ta saba "bari na kawo maka"

"No, dawo ki zauna"

Inkiya yake musu su basu wuri sumsum suka tashi suna dariyar dramar Radhiya.

Kai ta sunkuyar karon farko da zata iya tunawa a rayuwarta ta rasa bakin magana saboda kunyar da ta bawa kanta. Dan gayu kamar wannan kyakkyawa daga ita sai shi a falo ai dole harshe yayi nauyi tace a zuciyarta. 

Nazarinta Awwab yake yi ya dago kansa daga jinginar da yayi da kujera yana mamakin wannan yarinyar ta gabansa ita ce Alheran dinnan da yake dauka suyi ta yawo a barrack shekarun baya. 

"Alheran" ya ambaci sunanta a hankali taji wani yarr a jikinta saboda yadda muryar ta ratsata.

"Uhmm"

"Kin dena magana ne kuma?" Ya tsokaneta da ya ga kamar ma a takure take.

Girgiza kai tayi sannan tayi kwafa da guntun tsaki "Wallahi kunya naji, ashe ba haka ake basarwa ba. Bari Emzee ya dawo zai gamu dani"

"Balotelli zaki yi masa?"

Dago kai tayi da sauri ya dage mata gira yana jin komai nata na burge shi. Ba haka yayi zaton ganinta ba. Yana ta kissima wata budurwa mai ji da kai da gayu sai ya hadu da Radhiya wadda kwatancenta sai wanda ya santa. Amma duk da haka yaji tayi masa a yadda ya sameta cikin kankanin lokaci.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: "Gulmata suka rinya yi maka?" Tayi maganar a cikin shagwabar da batayi niyya ba. Hakan yasa Awwab sake yin murmushi. Daga shigowarsa gidan zuwa yanzu idan ma yana da damuwa to tabi ruwa tabi iska Radhiya ta dauke masa ita.

"Kinki zuwa na ganki ba sai na nemi labarinki ba"

"Ba ga su Mama ka gani ba maimakon kayi hira dasu shine zasu kawo maka zancena?" Ta sake marairaice masa.

"Kinsan me yasa na kasa zama na huta duk da tarin gajiyar da nayi?"

"A'a" tace tana girgiza kai.

"Because I missed you Alheran" yace suna hada idanu tayi saurin lumshe nata.

Tayi karatu bare ace bata jin turanci bata fahimce shi ba. I miss you ai sai masoya a iya saninta. Shiyasa taji wata irin kunya ta saukar mata.

Ko a jikinsa don iyakar gaskiyarsa kenan. Murna da sanin cewa ga inda take ya wadatar dashi ya hana shi sukunin duk wani hutu idan ba haduwa suka yi ba "sai da nazo na ga ashe ni kadai na damu dake, kina kallona kina basarwa"

Maganarsa ta bata dariya kamar yadda ya fadeta yana yamutsa fuska shi ba'a kyauta masa ba "wasa ne wannan amma ni fa ban iya tuna ka ba ne sai labarin da Ummi ta bani"

Hannu yasa ya karbi lemon da Fauziyya ta tsiyaya masa. Sai da ya kurba sau biyu ya sake kallonta "ko kadan?"

"Me?"

"Rashin tunawa dani din"

"Ka ga fa nayi kankanta lokacin"

Gefen girarsa ya shafa "kinga wannan tabon?"

Daga inda take tana ganin duhun layin "bille ne ya karkace? Ko ka hadu da wanzamin da bai san aikinsa ba. Me ya hada tsakiyar goshi da gefen gira? Ko irin na gefen nan mai uku-uku aka so yi maka?" Ta rinka jero masa tambayoyi.

"Na hadu da wanzamiya dai"

Fauziya za ta fara dariya don gidansu kowa yasan tabon aikin Radhiya ne ya kalleta sai ta sake tashi. Wai meye ne Hamma yake korarsu...kodai, kodai...dan murmushi ta saki amma kuwa da tayi farinciki idan haka ne. Abincin da Zahra ta gama hadawa ta karbo don so take ta sake ganin gulma.

"Ana wanzamai mata dama?"

"Alheran sunanta ma"

"Da gaske?"

"Yakushina fa kika yi" yace yana kallon yadda ta ware idano ta saman kofin hannunsa.

Tasowa tayi ta dawo kujerar gefensa yadda zata gani sosai tana ta karkata kai hagu da dama "Allah Hamma, ko dai don nace ban tunaka bane zaka dora min" ta rinka dage girarta duka biyu a tare tana cewa "eyye, eyye?"

"Cute" ya furta a sanyaye ya rasa me yake damunsa tun da ta fito daga dakin. Wasu abubuwa take yi da suke tado masa da memories din kuruciyarsu. Ta bude ido ta lumshe, ta turo baki ta sha kunu ko murmushi.

"Da kina yarinya kin fiye rigima da fada...uhmm harda kuka. Gashi naga alama babu wanda kika dena cikinsu."

"Tsokanata akayi ne, amma yanzu na dena fada"

Fauziyya da ta duka za ta zuba masa abincin a plate tace "A yaushe kika dena fadan?"

"Babu ruwanki da hirarmu bar abincin ma zata zuba min idan na tashi ci. Tafi kawai ki barmu kinsan ba wurinku nazo ba"

Dadi kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha yace ba wurinsu yazo ba. Kai na rawa tana jujjuya idanu tace mata " yehhh sai a tafi kinji me Hamma Awwab dina yace. Dama na fada muku idan ya zo zai dena kula kowa sai ni, nima kuma in dena kula ku ehe"

"Shikenan ka bata damar cigaba da raina mu ni da Zahra"

Kallon tuhuma yayi mata "wai haka?"

"Fada kawai take yi don ta hadamu, kowa ya shaideni a gidan nan wurin girmama manya ba daga nan ba" yanayin maganar kadai zai gane karya taje yi. Bata da innocent face, kana ganinta kasan akwai jini a jika.

"Allah Ya shiryeki Radhiya" Fauziyya tace tana tafiya za ta je kaiwa Zahra tsirku.

Abincin ya nuna mata ta soma zuba masa "ba kya son na kula kowa?"

Ta dago kai "eh wallahi, ko na yau kawai kada kayi musu magana su gani duk kafi sona. Ni kadai ce kanwarka banda su"

"Gobe zan koma Kt ba kya so nayi hira dasu Ibrahim?"

Dena zuba abincin tayi tana jin babu dadi a ranta "gobe kuma Hamma ko sabawa bamuyi ba zaka koma?"

Wannan karon shi ya fara janye idanunsa daga gareta. Ya rasa gane me yasa suna kallon juna sai yaji abu ya taba zuciyarsa. Ya dai alakanta hakan da dawo masa da tunanin baya da take yi ne.

"Akwai wani sabon da ya rage msna bayan wanda muka yi in less than an hour?"

Wuya ta shiga sosawa irin na marasa gaskiya tana sunkuyar da kai da murmushi. Dimple dinnan ya sake kallo ya miko hannu kamar zai saka yatsansa yadda ya saba yi mata a baya ya tallabo habarta da ragowar yatsunsa sai kuma yayi saurin janyewa. Alheran is not a child anymore ya yiwa kansa fada.

"Na yarda kayi hirar minti goma goma da kowa su Baba kuma awa daya, sauran kuma duka nawa ne."

"Bazaki gaji dani ba?" Bai san me ya kaishi yin tambayar ba. Yayi saurin datse bakinsa bayan ta fito.
Chapter 40 · 0% Book details