← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 157

Sashe 36

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shiri Awwab yake da sauri sauri yau kadai yake da damar fita yayi sayayyar da zaiyi gobe ya taho Nigeria. Tun dare yake tunanin me zai saya ya kai musu ya rasa. Ba sabawa yayi da irin wannan abubuwan na mata yayi ba. Dan tunani yayi ya dauki waya ya kira wadda yasan za ta bashi shawara mai kyau. Ringing biyu ta dauka kamar jira take dama. A shagwabe ta soma magana tana korafin rashin kiranta da yayi har na kwana biyu.

"Sorry my G aiki ne"

"Lokacin aiki daban nawa ma daban" Ghazalatu ta sake narke masa.

"Naji nayi laifi shiyasa ma ticket din Abuja na saya don na fara ganinki kafin na wuce gida"

Ihun da tayi sai da ya cire wayar daga kunnensa yana dariya. Yana matukar son Ghazalatu. Ita ta nemi su boye soyayyarsu ma sai ta gama degree dinta idan ba haka ba aure za'ayi mata a gida ta sani. Yanzu wata biyu da yin final exam bautar kasa take jira. Sun gama tsarinsu idan Awwab ya dawo zasu gabatarwa da iyayensu da abinda ke tsakaninsu.

Sun taba hira don ta dena fushin tunda taji zai taho washegari.

"G albishirinki"

"Goro kyakkyawa kamar Yayana"

"Su Mami sun je gidan Ummin nan nawa da nake baki labari"

Yadda taji yana murna dole ta taya shi ba don ta damu ba. Yayi ta fada mata ashe harda kani an yiwa Alheran.

"Na tayaka murna, zan so ganinta gaskiya"

"Ki bini Katsina mana idan na zo"

Dadi taji tayi saurin amincewa. Awwab bai kyaleta ba yace "kune sarakan tsaraba, me kike ganin zai dace da yarinya about 18 to 19 years"

"Friend kayi mace har kake fada min za kayi mata siyayya?" Tace cikin fushi da kishi.

"Nope, Alheran nake son sayawa wani abu"

Duk da haka ranta baiyi mata dadi ba amma bata son bata masa rai yanzu sai yace ya fasa tsayawa a Abujan.

"Ka saya mata takalmi, jaka, turare, kayan kwalliya da jewelleries"

Yaji kayan da yawa to amma so yake ya yi musu abin bajinta "thanks dear" yace da Ghazalatu kafin ya ajiye wayar.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Ruwa yaje ya watsawa fuskarsa yayi brush sannan ya dauko wani karamin hankici kamar tawul iya tafin hannunsa ya goge fuskar. Komawa yayi ya zauna yana jin kansa yayi wani fresh balle da ya tuna mutanen da zai gani. Kayataccen murmushi yayi shi kadai wata matashiya da suke zaune tare ta maida masa saboda ya dan fuskanceta ne yana laluben seat belt dinsa.

"Hi handsome" tace dashi da ingantaccen turancinta.

Sai da ya waiga bayansa ya tabbatar babu kowa sannan ya nuna kansa sai ta gyada kai.

"Hello" ya maida mata da kyar don baya son mace mara kamun kai. Da ace magana tayi masa kawai bazai damu ba. Amma idan kaji ana handsome ko beautiful ai kasan kwanan zancen.

"Kaima bahaushe ne ko?"

Baiyi mamakin da ta gane ba tunda suna zama ya soma waya bai dena ba sai da yaga jirgin ya fara tafiya.

"Kema haka ko?"

Murmushi tayi, a rayuwarta tana son namiji mai kaurin murya. Ba da karfi ya amsa mata ba amma amon muryar ya isa ya sanya mata da yawa muradin son kasancewa da mai ita musamman idan suka hado dashi. Wankan tarwada, dogo, hanci madaidaici da ya dace da kyakkyawar fuskarsa.

"Na kula baka ci komai ba tun tasowarmu."

Bai wani kare mata kallo ba yace "bana jin yunwa ne"

So take hirar ta tsawaita don tunda ta dora idanu a kansa zuciyarta bata kara samun sauki ba. Ta kula mutumin kamar yana da ji da kai sai dai kuma bazata bari shan kamshinsa ya hanata samun abinda take so ba. Dawowarta kenan daga Germany inda taje hutu wurin yayarta. Mahaifinta tsohon soja ne da ya tsunduma siyasa tun lokacin mulkin farar hula. Yanzu haka sanata ne da yake wakiltar mazabarsu a jihar Plateau.

"Suna na Arifah"

"Awwab"

Daga haka ya kafa waya a kunne don tuni sun sauka an bada damar kowa ya tashi. Cikin cabin crew din wata 'yar Nigeria da tasan Awwab tazo suna gaisawa da ya tashi zai dauki jakarsa.

"Captain yau fa ka yi mana wayo. Kasha bacci ka barmu da aiki"

Sai yanzu Arifah ta ga ya sake sakin fuska harda dariya "ki dauki hutu kema sai mu koma tare. Yanzu ina da wata guda na mantawa da kowa sai family dina"

'Yar hira suka taba sannan suka yi sallama. Awwab na fita Arifah ta bi bayan matar da suka gaisa mai suna Chisom ta roketa numbar wayarsa.

"Ki bishi ya baki da kansa, Captain Awwab baya son irin haka don an taba yi masa na gani"

Marairaicewa tayi tana fada mata yadda take son shi tare da rokon ta taimaka mata. Kudi ta dauko daga jakarta za ta mika mata Chisom ta bata rai "ba sai kin sayeni ba, Awwab is a nice man ga number dinsa ki gwada sa'arki"

Arifah kamar ta zuba ruwa a kasa tasha ta rubuce number din da ta karanto mata daga wayarta ta fita da sauri ko zata sake samunsa sai dai yayi mata nisa bata ma san ina yayi ba. Bata da damuwa tunda akwai numbar da zata same shi.

Yana fitowa waje hasken rana ya kwale a sama kamar ba shida ke neman yi ba. Jacket dinsa ya cire ya sakale a hannunsa ya jana jan akwatinsa.

Kamar ance ya kalli hagunsa suka hada ido da Ghazalatu. Taci kwalliya sosai don ta burge shi ta kuwa yi nasarar sanya shi murmushi. Daga ita sai dreba suka zo daukarsa kannenta suna makaranta.

"Yayana" tace da ya zagayo wurin motar tana murmushi.

"My G kinyi kyau fa"

"Ba wani nan, kai dai kawai ka dade baka ganni bane"

Gaisawa yayi da dreban ya shiga gaba ita kadai a baya suna ta hira. Ji take kamar ya dawo bayan motar su zauna tare. Ta rasa gane masa ne ana soyayya amma shi tamkar wanda ya taso a kauye. Baya irin yadda wayayyu suke yi. Ko gidansu taje hutu haka zata karaci zamanta hannu wannan bai san ya rike mata ba ko da su kadai suka fita. Yanzu wata hudu rabon da ya ganta amma simple hug ma su ji dumin juna ya gagara.

Waya ya rinka yi a rabin tafiyar saboda tazarar airport din da cikin gari. Mami ta fada masa su Alheran suna Kano amma Ummi tana tare dasu.

"In sha Allahu gobe asubanci zanyi zuwa Katsina. Sai na ga Ummi zanje wurinsu. Uhmm Mami tare zamu taho da Ghazalatu fa"

"Jiya Gambo ta fada min, sai kun iso. Jirgi zaku biyo?"

"Gamu nan dai sai abinda Mummy tace"

Sunyi sallama Ghazalatu ta rankwafa daidai kansa yana jin numfashinta a kunnuwansa da wuya.

"Daga kanki G" yace yana yin gaba da kansa saboda yadda yake ji.

Komawa tayi ta gyara zamanta "na daga shikenan, dama tambayarka zanyi ko kayi min tsaraba nima kamar kowa"

"Su waye kowa?"

"Yarinyar da ka tambayeni jiya me zaka saya mata"

"Allah Yasa ba kishi kike yi da yarinyar da ni dake duk bamu gani ba" yace yana dariya.

"Akwai dalilin da zanyi kishinta ne?"

"Ko kadan, please kada muyi abinda muka saba daga zuwana. A bar maganar haka ko."

Bata sake cewa komai ba har suka isa gida. Mummy Gambo tasa an hada masa kayan tarbar babban bako. Ranar da daddare da kansa ya sanar da ita abinda ke tsakaninsa da Ghazalatu. Gambo tayi murna sosai tana ta dokin maganar ta kai kunnen Hassana wato Mami. Abu ne da ya shafi dangi gabadaya ta bangarensu da bangaren mazajensu. Ga Awwab din da shiga rai dole taji dadin wannan hadi.

**********

Harun mahaifin Ghazalatu da ne ga Alh Baba. Babansu Mami kaninsa ne na uku yayin da baban Major ya kasance autansu. Harun ne ya biyawa Alhajinsu umara suka tafi tare. Mutumci, shakuwa da kyakkyawar alakar dake tsakaninsa da Major tasa ya kaishi Germany gashi yanzu shi ma ya tsaya da kafarsa.

Major bashi da wani abokin shawara a dangi kamar Harun shiyasa a daren ranar da ya sanar dasu Mami game da hadin Awwab da Alheran ya kira shi ya fada masa.

"Gaskiya kayi tunani mai kyau ko babu komai yanzu zaka fi ji a ranka cewa ka rike iyalin bawan Allahn nan. Allah Ya gafarta masa Ya nuna mana lokacin"

"Amin Harun"

"Zan fara yiwa Alh Baba maganar yadda muna dawowa za'a je neman aure. Bikin su Zahra duka duka baifi wata daya ba kuma gashi kace gara a hada"

"Gara a hada din muma sai mu sami sauki"

"Hakane, ga 'yarka can Ghazalatu ta tsaya ruwan ido da ta fitar itama ba sai muyi komai mu gama lokaci guda ba"

"Barni da ita, gobe suna hanya ita da Awwab zan binciketa ko akwai wani"

Hirarsu suka yi irin na 'yan uwantaka suna kulla shawarwari game da yadda bikin zai kasance.

Washegari Awwab ya sauka a garin nasu cike da tsantsar farinciki ya rinka sallama a kofar dakin Mami. Tana sane wai sai ta ja masa rai taki amsawa.

"Mami manaaaa"

Dariya tayi "shigo dai ba don halinka ba"

Da saurinsa ya bude kofar idanunsa suka sauka akan Umminsa Mairama maman Alheran. Murmushi take ta yi masa daga inda take zaune wai wannan muryar Awwab ce. Shi kuwa wani dumi yaji a idonsa da sauri ya karasa gabanta ya riko duka hannayenta biyu ya dago kai yana kallon fuskarta.

"Ummi"

Da hannunta daya take bin fuskarsa tana shafawa "Awwab kaine ka zama babban mutum haka"

Mami tana gefe tana murmushin jindadi Ghazalatu kuma ta coge a bakin kofa.

"Ummina kina lafiya? Kin rinka tunawa dani kuwa" yace yana matse hannuwanta cikin nasa. Yau gashi da Umminsa abinda ya dade da cire rai saboda yadda shekaru suke ta yawaita.

Hawaye ta soma yi "ban taba mantawa daku ba Awwab. Ina ma zan iya ganinka da kyau in gani ko wannan tsayin kamar bulala ka dan cike shi da tsoka"

A razane ya kalli Mami sai ya ga tana hawaye. Hannunsa yasa yana yawo dashi a gaban idanunta ya ga ko gezau. Awwab kasa mallakar kansa yayi ya kifa kansa a cinyarta yana kuka.
Chapter 36 · 0% Book details