Sashe 77
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haushi ya kama Radhiya da ta fahimci da mace yake magana. Gara ta bashi wuri idan ma akwai wata I love you da zamanta a wurin ya hana a fada sai yaji dadin sakewa. Tashi tayi da karfinta ai kuwa goyon nata taji gabadaya yayi sako-sako yana neman kwancewa baby ya fado. Yadda gabanta ya fadi sauri tayi ta duka jikinta na rawa ta tallafo Daadaa da hannuwanta ta baya. A hankali ta saki tana kokarin gyara gaban da ya kwance duka yaron yayi motsi a gigice tace "Hamma"
Yana da kallonta amma a zatonsa goyon zata gyara. Kuma tsabar tsoro ta kasa daga murya kada yaron ya tsorata ya fado.
"Hamma ka ajiye wayar mana" tace tana daga murya.
Sai lokacin ya cire wayar daga kunnensa "me kika ce?"
Kafafu biyu Daadaa yake dan shureta dasu alamun baya jindadin yanayin da yake.
Kuka ne ya taho mata kada ta saki dan mutane "Hamma please help" tace tana rike gaban zanin sosai kuma taki dagowa.
Wayarsa ya ajiye da sauri akan kujerar da ta tashi ya zagayo yana dukawa ya ga me ya sameta "meye?"
A rikice take bata san ya zasu kwashe da Ummi ba idan ya fado "goyon ya kwance"
"To ki gyara mana" yace yana mikewa ya gyara tsayuwarsa.
"Ban iya ba fa Hamma"
"Seriuosly?" Shima ya soma rikicewar ganin tana ta saka hannu daya a gaba daya a baya.
"Zai fadi" ta sake cewa da yayi wani irin zillo yana canyara ihu ya gaji.
"Kwace zanin da sauri" yace yana saka hannu a bayan yaron ita kuma ta kwance gaban "tashi a hankali"
Tana tashi yaron ya fada a hannunsa ya kankame shi a kirjinsa "are you okay?" ya tambayeta yana kallon yadda tayi wuri wuri.
"Allah Ya soni da ya fado..."
"Da sai mu haifi wani" yace yana kallon dimple dinta.
Idanunta ta dauke daga kansa maganar tana dada shiga kwanyarta. Duk wasu matakan nuna masa yanzu ba da bane ta nemesu ta rasa sai uwar kunyar da ya hadata da ita. Ya san me yayi mata amma sai ya wayance irin yadda ta taba yi masa.
"Silly girl, me kike tunanin ina nufi?"
"Ba nufinka idan ka haifi naka nima na haifi nawa sai mu kawo mu hada mata ba?"
Kanta tsaye tayi maganar kafin ya gama gano lagonta ta tafi ta barshi da baby a hannu.
**********
"Wurin wa kazo?"
"Waye shugabanku a nan barrack din?"
Dariya ya basu suna masa kallon wanda bai san me yake yi ba. Barrack ai ba wurin da zaka zo kai tsaye bane idan baka san wanda kake nema ba.
Chibuzor ya rasa wa zaice musu. Sai da yayi sati a garinsu ana ta jajantawa iyayensa abinda ya same shi sannan da kyar ya kwaci kansa ya taho Sakkwato saboda cika alkawarin da ya daukarwa kansa da Zayyan. Bai san komai game da tsarin sojoji ba kamar chanjin mukami shiyasa kawai yace "Lieutenant Hadir nake nema" yana fata daidai ya fadi sunan.
Duk wani hargagi da zasu yi masa sunyi a ganinsu bai san me yake yi ba. Gashi dai a haka yayo fes dashi. Kin tafiya yayi tun safe har yamma ana ta abu daya yana tsaye a bakin gate. Wani ne cikinsu ya shiga ciki bangaren ofisoshinsu suna hira da wani da yake zaune a bayan wata kanta yake bashi labarin wani msi naci a waje.
"Baku saka shi tsallen kwado ba?"
"Tausayi ya bani. Ya dage wai sako ya kawowa Lt Hadir. Ban taba jin sunan ba ma. Amma an chaje shi babu komai a jikinsa"
Wani yazo wucewa suka tambaye shi ko ya taba jin mai wannan sunan. Wanda yake bayansa ne ya amsa "an taba yi mana amma shi fa yayi retire saboda rashin lafiya tun bayan dawowarsu daga Liberia an dade don tun ina non-commisioned officer"
Wanda ya kawo zancen ya mike "yayi zancen Liberia fa. Bari dai na koma naji"
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Mamaki sosai yayi da aka sanar dashi bakon nasa yace da sakatariyarsa tayi sauri ta shigo dashi duk da cewa ya gama shiri zai tafi gida ne lokacin tashi yayi. A bakin kofa ya tsaya ya tarbe shi yana murmushi suka kama hannuwan juna suna gaisawa. Kowannensu sanye yake da manyan kaya da babbar riga. Kana ganin bakon kasan naira ta zauna da kyau. Daga hularsa har zuwa takalmi babu wani abu da kudinsa yake kasa da dubu ashirin.
"Alh Salisu wai kaine nake gani ko dai mafarki nake yi?"
"Tuba nake Alh Musa ni din mai laifine a wurin mutane da yawa. Nine da kaina ba sako ba na yakice ayyukan gabana nace sai nazo"
Alh Musa ya nuna masa wuri ya zauna sannan ya tashi ya kira sakatariyarsa ya soma fada mata me zata hadow bakon ya dakatar dashi.
"Kada ka damu kanka a koshe nake."
Zama ya sake yi suka kuma gaisawa da tambayar juna bayan rabuwa.
"Yara suna dakunansu ko?"
"Wallahi kuwa"
"Naso zuwa daurin auren nan amma wallahi Musa zama a wuri daya na sati gagarata yake yi"
"Ya fa kamata ka sassautawa kanka Alh Salisu. Mutum yana fafutukar neman kudin nan fa kawai sai mutuwa ta riskeshi. Sai ya laluba ya ga babu wani abin arziki da ya tara sai wahala. Shiyasa ka ga na makale wuri daya yanzu"
"Mtsww ni zan fada maka yawon nan baiyi ba ko kadan. Amaryata fa mai aiki ta kama da dreban da na daukar mata a cikin gidana don bala'i"
"Subhanallahi garin yaya haka ta faru?"
"Kaima ka sani ai, cewa tayi bana zama bani da lokacinta. Inda na gode Allah bamu haihu ba da ta saka ni wasiwasi"
"Ka chanja tsari Alh Salisu. Girma sai dada kamamu yake yi da kunya irin wannan na fitowa daga gidajen aurenmu. Ai kamata yayi ace macen kwarai ko bata sonka ta san kiyaye addini da darajar kanta"
Daya daga cikin wayoyin Alh Salisu ce tayi kara ya kasheta sannan yace "ka tuna Halifa ai babban dana. To mahaifiyarsa wallahi ita ta cire min son mata gabadaya shiyasa bana damuwa da zama dasu tunda nasan kudin ne ya kawosu sai na basu kawai. Da bamu rabu ba ina mai tabbatar maka ko zanyi yawo ba kamar yadda nake yanzu ba. Sannan mafi yawa tare zamuyi gani gata"
"Kace kun zuba soyayya" Alh Musa ya fada da dariya.
"Wace soyayya? Matar da ta aureni alhali tana son mijin kanwarta. Kaji fa kanwa da suka hada uba kuma bata iya boye min. Kishi take da kanwar abin babu kyaun gani. Shiyasa da na saketa bayan abin ya fito da mijin kanwar ya rasu ko shi Halifan bana bari yaje wurinta sosai"
"Amma kuwa kayi kuskure Alh Salisu wa yake raba da da uwa banda abinka? Nima nayi irin auren nan amma wallahi Zainab 'yar halak ce. Ka tuna kazo daurin aurenmu. Ita dole aka raba auren mijin ya sami paralysis ga rashin magana amma ta kafe sai ta zauna dashi. Kasan Allah ko zanyi rantsuwa bani da kaffara tunda na aureta Zainab bata sake zuwa Kano ba sannan ko a bayan idona idan tayi waya da danta bata taba cewa ina mahaifinsa. In karkare maka zance na saketa kuma mijin ya sami lafiya. Aisha ma ta kirani wai ta haihu...kai kaji kudura ta Ubangiji"
Sosai Alh Salisu yaji dadin shawarwarin Alh Musa don gaskiya yasan bai kyauta ba. Kasuwancinsa ya bunkasa sosai amma zumunci dai bashi da lokacinsa. Yana China babansa ya rasu haka yana India babarsa ta rasu da kyar ya roki yayyensa aka jinkirta jana'izarta. Kudi dai danginsa sun warke amma ganinsa yayi wuya.
"Nagode Alh Musa, zan gyara don ina komawa zansa a kai Halifa Sumaila wurin babarsa da kakaninsa. Bai saba da kowa ba sai ni. Cikin gidan ma kannensa ba shirginsu yake shiga ba ni kuma ban damu ba ganin duka mata ne"
"Matan idan babu kai ba shine gatansu ba?"
"Hakane, sai ka tuna min da abokaina na kuruciya da duka na watsar da kace mijin matarka na da yana da paralysis. Akwai aminina soja ne a yaki ya kamu da wannan lalura. Sau biyu naje duba shi shikenan kamar wani sallamamme na dena waiwayarsa. Daga baya kunya da nauyin jinkirin yasa na kasa zuwa kuma"
"Tunda kana da rai ai babu wani jinkiri. Itama Zainab din mijinta fa a yaki ne tasa lalurar sunansa Hadir"
Alh Salisu sai ya gyara zama da kyau "Hadir Murtala mutumin Kano?"
Da mamaki sosai a fuskarsa yace kwarai kuwa "shine aminin naka?"
"Shine Alh Musa wallahi shine. Ina zuwa Kano gidansa zani...ni kam kudi naga sharrinsa tunda ya nesanta ni da makusanta na"
Alh Musa yayi matukar mamaki. Da Alh Salisu ya rike zumunci da Hadir bai kwashi wadannan shekarun a kwance ba. Kudi ne dashi fa na ban mamaki don shi a haka bai kama kafarsa ba. Duniya komai sai Allah Ya nufa amma sakacinmu ke janyo mana. Adireshin gidansu na Abuja ya nema wurin 'yarsa ya bashi.
"Daga nan ni sai birnin tarayya inji mutanenmu."
Godiya mai tarin yawa ya yiwa Alh Musa sannan ya koma katon gidansa dake garin Port Harcourt din. Halifa ya kira yace masa ya shirya gobe ya taho Abuja. Bautar kasa zai fara dayake a turai yayi karatu ya gama da wuri. Sake tunani yayi na tuna cewa yaron da kannensa ma babu shakuwa yace masa dashi da kannen nasa mata ne su hudu su taho tare. Sai kuma ya kira matarsa uwar uku cikin yaran Farida, Husna da Meena. Dayar mai bin Halifa a jerin haihuwa Hibbah tata maman ta dade da fita itama ya fada mata tace yaran su shirya. Baiwar Allah har ranta taji dadi yau da kansa yana wani garin yace a tura masa 'ya'yansa kuma wai kuma su da Halifa. Bata taba kin yaron ba duk miskilancinsa da shiru shiru. Irin 'ya'yan baba dinnan ne sangartattu amma ba wai ya lalace da dabi'un banza bane sai son jiki.
Yana da kallonta amma a zatonsa goyon zata gyara. Kuma tsabar tsoro ta kasa daga murya kada yaron ya tsorata ya fado.
"Hamma ka ajiye wayar mana" tace tana daga murya.
Sai lokacin ya cire wayar daga kunnensa "me kika ce?"
Kafafu biyu Daadaa yake dan shureta dasu alamun baya jindadin yanayin da yake.
Kuka ne ya taho mata kada ta saki dan mutane "Hamma please help" tace tana rike gaban zanin sosai kuma taki dagowa.
Wayarsa ya ajiye da sauri akan kujerar da ta tashi ya zagayo yana dukawa ya ga me ya sameta "meye?"
A rikice take bata san ya zasu kwashe da Ummi ba idan ya fado "goyon ya kwance"
"To ki gyara mana" yace yana mikewa ya gyara tsayuwarsa.
"Ban iya ba fa Hamma"
"Seriuosly?" Shima ya soma rikicewar ganin tana ta saka hannu daya a gaba daya a baya.
"Zai fadi" ta sake cewa da yayi wani irin zillo yana canyara ihu ya gaji.
"Kwace zanin da sauri" yace yana saka hannu a bayan yaron ita kuma ta kwance gaban "tashi a hankali"
Tana tashi yaron ya fada a hannunsa ya kankame shi a kirjinsa "are you okay?" ya tambayeta yana kallon yadda tayi wuri wuri.
"Allah Ya soni da ya fado..."
"Da sai mu haifi wani" yace yana kallon dimple dinta.
Idanunta ta dauke daga kansa maganar tana dada shiga kwanyarta. Duk wasu matakan nuna masa yanzu ba da bane ta nemesu ta rasa sai uwar kunyar da ya hadata da ita. Ya san me yayi mata amma sai ya wayance irin yadda ta taba yi masa.
"Silly girl, me kike tunanin ina nufi?"
"Ba nufinka idan ka haifi naka nima na haifi nawa sai mu kawo mu hada mata ba?"
Kanta tsaye tayi maganar kafin ya gama gano lagonta ta tafi ta barshi da baby a hannu.
**********
"Wurin wa kazo?"
"Waye shugabanku a nan barrack din?"
Dariya ya basu suna masa kallon wanda bai san me yake yi ba. Barrack ai ba wurin da zaka zo kai tsaye bane idan baka san wanda kake nema ba.
Chibuzor ya rasa wa zaice musu. Sai da yayi sati a garinsu ana ta jajantawa iyayensa abinda ya same shi sannan da kyar ya kwaci kansa ya taho Sakkwato saboda cika alkawarin da ya daukarwa kansa da Zayyan. Bai san komai game da tsarin sojoji ba kamar chanjin mukami shiyasa kawai yace "Lieutenant Hadir nake nema" yana fata daidai ya fadi sunan.
Duk wani hargagi da zasu yi masa sunyi a ganinsu bai san me yake yi ba. Gashi dai a haka yayo fes dashi. Kin tafiya yayi tun safe har yamma ana ta abu daya yana tsaye a bakin gate. Wani ne cikinsu ya shiga ciki bangaren ofisoshinsu suna hira da wani da yake zaune a bayan wata kanta yake bashi labarin wani msi naci a waje.
"Baku saka shi tsallen kwado ba?"
"Tausayi ya bani. Ya dage wai sako ya kawowa Lt Hadir. Ban taba jin sunan ba ma. Amma an chaje shi babu komai a jikinsa"
Wani yazo wucewa suka tambaye shi ko ya taba jin mai wannan sunan. Wanda yake bayansa ne ya amsa "an taba yi mana amma shi fa yayi retire saboda rashin lafiya tun bayan dawowarsu daga Liberia an dade don tun ina non-commisioned officer"
Wanda ya kawo zancen ya mike "yayi zancen Liberia fa. Bari dai na koma naji"
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Mamaki sosai yayi da aka sanar dashi bakon nasa yace da sakatariyarsa tayi sauri ta shigo dashi duk da cewa ya gama shiri zai tafi gida ne lokacin tashi yayi. A bakin kofa ya tsaya ya tarbe shi yana murmushi suka kama hannuwan juna suna gaisawa. Kowannensu sanye yake da manyan kaya da babbar riga. Kana ganin bakon kasan naira ta zauna da kyau. Daga hularsa har zuwa takalmi babu wani abu da kudinsa yake kasa da dubu ashirin.
"Alh Salisu wai kaine nake gani ko dai mafarki nake yi?"
"Tuba nake Alh Musa ni din mai laifine a wurin mutane da yawa. Nine da kaina ba sako ba na yakice ayyukan gabana nace sai nazo"
Alh Musa ya nuna masa wuri ya zauna sannan ya tashi ya kira sakatariyarsa ya soma fada mata me zata hadow bakon ya dakatar dashi.
"Kada ka damu kanka a koshe nake."
Zama ya sake yi suka kuma gaisawa da tambayar juna bayan rabuwa.
"Yara suna dakunansu ko?"
"Wallahi kuwa"
"Naso zuwa daurin auren nan amma wallahi Musa zama a wuri daya na sati gagarata yake yi"
"Ya fa kamata ka sassautawa kanka Alh Salisu. Mutum yana fafutukar neman kudin nan fa kawai sai mutuwa ta riskeshi. Sai ya laluba ya ga babu wani abin arziki da ya tara sai wahala. Shiyasa ka ga na makale wuri daya yanzu"
"Mtsww ni zan fada maka yawon nan baiyi ba ko kadan. Amaryata fa mai aiki ta kama da dreban da na daukar mata a cikin gidana don bala'i"
"Subhanallahi garin yaya haka ta faru?"
"Kaima ka sani ai, cewa tayi bana zama bani da lokacinta. Inda na gode Allah bamu haihu ba da ta saka ni wasiwasi"
"Ka chanja tsari Alh Salisu. Girma sai dada kamamu yake yi da kunya irin wannan na fitowa daga gidajen aurenmu. Ai kamata yayi ace macen kwarai ko bata sonka ta san kiyaye addini da darajar kanta"
Daya daga cikin wayoyin Alh Salisu ce tayi kara ya kasheta sannan yace "ka tuna Halifa ai babban dana. To mahaifiyarsa wallahi ita ta cire min son mata gabadaya shiyasa bana damuwa da zama dasu tunda nasan kudin ne ya kawosu sai na basu kawai. Da bamu rabu ba ina mai tabbatar maka ko zanyi yawo ba kamar yadda nake yanzu ba. Sannan mafi yawa tare zamuyi gani gata"
"Kace kun zuba soyayya" Alh Musa ya fada da dariya.
"Wace soyayya? Matar da ta aureni alhali tana son mijin kanwarta. Kaji fa kanwa da suka hada uba kuma bata iya boye min. Kishi take da kanwar abin babu kyaun gani. Shiyasa da na saketa bayan abin ya fito da mijin kanwar ya rasu ko shi Halifan bana bari yaje wurinta sosai"
"Amma kuwa kayi kuskure Alh Salisu wa yake raba da da uwa banda abinka? Nima nayi irin auren nan amma wallahi Zainab 'yar halak ce. Ka tuna kazo daurin aurenmu. Ita dole aka raba auren mijin ya sami paralysis ga rashin magana amma ta kafe sai ta zauna dashi. Kasan Allah ko zanyi rantsuwa bani da kaffara tunda na aureta Zainab bata sake zuwa Kano ba sannan ko a bayan idona idan tayi waya da danta bata taba cewa ina mahaifinsa. In karkare maka zance na saketa kuma mijin ya sami lafiya. Aisha ma ta kirani wai ta haihu...kai kaji kudura ta Ubangiji"
Sosai Alh Salisu yaji dadin shawarwarin Alh Musa don gaskiya yasan bai kyauta ba. Kasuwancinsa ya bunkasa sosai amma zumunci dai bashi da lokacinsa. Yana China babansa ya rasu haka yana India babarsa ta rasu da kyar ya roki yayyensa aka jinkirta jana'izarta. Kudi dai danginsa sun warke amma ganinsa yayi wuya.
"Nagode Alh Musa, zan gyara don ina komawa zansa a kai Halifa Sumaila wurin babarsa da kakaninsa. Bai saba da kowa ba sai ni. Cikin gidan ma kannensa ba shirginsu yake shiga ba ni kuma ban damu ba ganin duka mata ne"
"Matan idan babu kai ba shine gatansu ba?"
"Hakane, sai ka tuna min da abokaina na kuruciya da duka na watsar da kace mijin matarka na da yana da paralysis. Akwai aminina soja ne a yaki ya kamu da wannan lalura. Sau biyu naje duba shi shikenan kamar wani sallamamme na dena waiwayarsa. Daga baya kunya da nauyin jinkirin yasa na kasa zuwa kuma"
"Tunda kana da rai ai babu wani jinkiri. Itama Zainab din mijinta fa a yaki ne tasa lalurar sunansa Hadir"
Alh Salisu sai ya gyara zama da kyau "Hadir Murtala mutumin Kano?"
Da mamaki sosai a fuskarsa yace kwarai kuwa "shine aminin naka?"
"Shine Alh Musa wallahi shine. Ina zuwa Kano gidansa zani...ni kam kudi naga sharrinsa tunda ya nesanta ni da makusanta na"
Alh Musa yayi matukar mamaki. Da Alh Salisu ya rike zumunci da Hadir bai kwashi wadannan shekarun a kwance ba. Kudi ne dashi fa na ban mamaki don shi a haka bai kama kafarsa ba. Duniya komai sai Allah Ya nufa amma sakacinmu ke janyo mana. Adireshin gidansu na Abuja ya nema wurin 'yarsa ya bashi.
"Daga nan ni sai birnin tarayya inji mutanenmu."
Godiya mai tarin yawa ya yiwa Alh Musa sannan ya koma katon gidansa dake garin Port Harcourt din. Halifa ya kira yace masa ya shirya gobe ya taho Abuja. Bautar kasa zai fara dayake a turai yayi karatu ya gama da wuri. Sake tunani yayi na tuna cewa yaron da kannensa ma babu shakuwa yace masa dashi da kannen nasa mata ne su hudu su taho tare. Sai kuma ya kira matarsa uwar uku cikin yaran Farida, Husna da Meena. Dayar mai bin Halifa a jerin haihuwa Hibbah tata maman ta dade da fita itama ya fada mata tace yaran su shirya. Baiwar Allah har ranta taji dadi yau da kansa yana wani garin yace a tura masa 'ya'yansa kuma wai kuma su da Halifa. Bata taba kin yaron ba duk miskilancinsa da shiru shiru. Irin 'ya'yan baba dinnan ne sangartattu amma ba wai ya lalace da dabi'un banza bane sai son jiki.